Friday, 8 December 2017

HUDUBAR JUMA'AH MAI TAKEN HARAMCIN MURNAR SABUWAR SHEKARA.

HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallacin Jumu'a Na
Ukku Dake Area II, Tsafe Sheik Sani
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan
#KAUCEWA_KOYI_DA_YAHUDAWA_TARE
_KAUCEWA_MURNAR_SABUWAR_SHEKARA
Bayan Yin Salati ga Manzon Tsira Sallallahu
Alaihi Wassalam, Da Kuma Yin Yabo ga ALLAH
Madaukakin Sarki''
Sai Sheik Sani Ya Fara Da Cewa Yaku Yan Uwa
Ku Sani ALLAH Ya Halicci Bayi Sa Ne Don Kawai
Mu Bauta Mashi Ashe Kuwa Babu Wani Dalili
Dazai Sa Muyi Sakaci A Fagen Bautawa Mai''
Haka Kuma ALLAH S.W,T
Hakika Addinin Musulunci Shine Cikakken Addini
Kuma Karbarben A Wurin ALLAH Madaukakin
Sarki, Haqiqa Addinin Musulunci Yana Dokoki Da
Kowane Musulmi Yazama Wajibi Yakiyaye Su,
Musulunci Yayi Mana Gata, Ya Bamu Yanci Kuma
Ya Gindiya Mana Sharudda Wadanda Aka
Haramta Mana,
Musulunci Yana Da Watanni Har Guda Goma Sha
Biyu Kamar Yadda ALLAH Yafada Mana, A Cikin
Alqu'arni Mai Tsarki Cewa ''LALLAI WATANNI A
WURIN ALLAH SUNE GUDA GOMA SHA BIYU
DAGA CIKIN SU AKWAI HUDU MAFIYA ALBARKA
KADA KU CUCI KAWUNAN KU A CIKINSU''
Yan Uwa Musulmi Idan Muka Lura Da Wannan
Ayar Ta Nuna Mana Cewa Watanni Musulunci
Sha Biyu Ne, Sun Fara Daga Muharram Zuwa
Zhul Hijja,
Addinin Musulunci Kammalallen Addini Ne Kamar
Yadda Alqur'ani Yafada ''A YAU NA KAMMALA
MAKU ADDININKU NA TABBATAR MAKU DA
NI'IMAR KU(MUSULUNCI) NA WAJABTA MAKU
ADDININ MUSULUNCI YA ZAMA ADDININ''
Mai Ahdari Ya Fada Cewa BAI HALLATA GA
MUTUN YA AIKATA WANI AIKI FACE YASAN
HUKUNCIN ALLAH AKAN WANNAN AIKIN''
Addinin Musulunci Yazo Da Komai Kuskure
Jahilcine Wani Ya Fada Cewa Babu Siyasa A
Addini,
Musulunci Nada Komai,
A Wannan Lokaci Da Muke Ciki Arna Na Shirin
Fara Chrismat!
Wanda Abun Ban Takaici Zakaga Musulmai Wai
Suna Taya Arna Murnar Zagayowa Wannan Rana,
Ita Ranar Christmat Rana Ce Da Aka Haifi Annabi
Isah A.S
Shehul Islam Ibn Taimiyah Yafada Cewa
Hawwariyun Wato Wadanda Suka Taya Annabi
Isah Isar Da Sako Basayin Wannan Bikin, Kunga
Idan Kun Lura Suma Kansu Bidi'a Ce Suka Qago
Wa, Kansu,
Bayan Haka Akwai Wani Kuskure Da Zai
Jagoranci Fitar Mutun Musulunci Wato NEW
YEAR
A Wajen Musulunci Bikin NEW YEAR Haramunne,
A Wajen Arna Kuwa Suna Murna Haihuwar
Annabi Isah, Wanda Suke Dangantawa Wai
Dandan ALLAH A uzu Billahi Iyaza, Ameen,
Kunga Kenan Idan Ka Taya Arna Murnar NEW
YEAR Ko Kuma Christmat Kamar Ka Taya Su
Wancan Shirkar Dana Gaza Sake Rubutawa, A
Uzubillah,
Yaku Yan Uwa Musulmi Idan Muka Girmama
Addinin Mu Hakika Duniya Zata Girmama Shi,
Idan Muka Wofintar Dashi Kazalika Duniya!
Yana Da Kyau Mu Fara Gabatar Da Kwanan Wata
n Musulunci Kafin Nasu,
Yakamata Idan Yazama Wajibi Muyi Amfani Da
Sunayen Watanni Mu Fada Da Hausa, Misali
January Sai Muce Watan Daya,
Bawaye Bane Kuma Ba Gwaninta Bane Wai Ace
Mu Duk Daya, Ai Duk ALLAH Muke Bautawa
Wanda Wannan Kuskure Ne, Basason Mu Kuma
Basason Addinmu Ta Yaya Za'a Ce Mana Wai
Daya Muke?
Baka Tabajin Arne Ya Fadi Hijra Musulunci Ba,
Yaku Yan Uwa Musulmi Duk Abunda Aka Baku
Naci Ko Na Sanyawa Da Sunan Christmat
Haramun Ne,
Ku Tuna Suna Danganta ALLAH Dai Haihuwa Fa
A'uzubillah, ALLAH Kuma Ya Karyatasu A Wajaje
Da Dama Kamar Su Suratul Ikhlas Da Sauransu,
Hakama ALLAH Ya Fada Cewa'' SAMA NA SON
TSAGEWA KASA NA SON TSAGEWA DUWATSU
NA SHIRIN TSEREWA TA DALILIN DANGANTA
WA ALLAH DANDA''
''TA YAYA AKE DANGANTAWA ALLAH DA? BAYA
TABA YIWUWA ALLAH YA RIKI DA'''
'
'
Mu Kiyaye Yan Uwa Idan Kwadai Da Wulakanci,
Hakama Inda Kwadaiyi Akwai Jahannama
Manzo S.A.W Yace ''WANDA YAYI KAMA DA
MUTANE HAKIKA YANA CIKINSU''
NA SADAUKAR DA WANNAN RUBUTUN DA
NIYAR ALLAH YAKAI LADARSA GA MAHAIFINA,
Da Fatar Zamuyi Salati Ga Wanda Na Bada
Fansa Raina Data Iyayena A gareshi
ALLAHUMMA SALLI ALA MUHAMMAD WA ALA
ALI MUHAMMADIN WASSALIM

©®DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA
+2347064282182

23/Rabi'u Auwal/1438
23/12/2016.

HUDUBAR JUMA'AH MAI TAKEN DOGARO GA ALLAH.

HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan
Muhimmancin #DOGARO_GA_ALLAH
Bayan Yin Salati ga Manzon Tsira Sallallahu
Alaihi Wassalam, Da Kuma Yin Yabo ga ALLAH
Madaukakin Sarki''
Sai Sheik Sani Ya Fara Da Cewa Yaku Yan Uwa
Ku Sani ALLAH Ya Halicci Bayi Sa Ne Don Kawai
Mu Bauta Mashi Ashe Kuwa Babu Wani Dalili
Dazai Sa Muyi Sakaci A Fagen Bautawa Mai''
Haka Kuma ALLAH S.W,T Ya Halicci Kome Da
Kowa Hakika Shine Maqagin Komai Da Kowa,
ALLAH S.W.T Cikin Hikimar Sa Ya Halicci Dan
Adam, Da Aljani Da Dabbobi Da Tsuntsaye, Da
Ruwa Da Iska, Da Abunda Na Kawo, Da Wanda
Ban Kawo Ba, Ya Halicci Abunda Muka Sani Ya
halicci Wanda Bamu Sani Ba,
ALLAH S.W.T Ya Qagi Wata Abu Da Ake Kira
Dogaro Ga Rai,
Hausawa Na Cewa Dogaro Ga ALLAH Jari,
Kwarai Kuwa Wannan Maganar Haka Take,
''ALLAH S.W.T Yace WANDA YAJI TSORON
ALLAH ZAI BASHI MAFITA KUMA ZAI
ARZIRTASA TA HANYAR DA BAYA TSAMMANI''
Yan Uwa Musulmi DOGARA GA ALLAH Ba Yana
Nufin Wai Kayi Kwance Yajira Wai ALLAH Zai
Kawo Masa Taimako, A'a Katashi Ka Nema Ka
Dogara ALLAH WALLAHI ALLAH Zai Taimakeki,
Akwai Abunda Ake Kira Musabbab, Ma'ana
Sanadi,
Manzo S.A.W Ya Fada Cikin Wani Hadisi Idan
Annabi S.A.W Yace ''TSUNTSAYE ZASU KWANA
BASU DA KOMAI AMMA ZASU KAI MARAICE
CIKIN SU, A CIKE''
Wannan Hadisin Ya Nuna Mana Cewa Tabbas
Idan Ka Dogara Ga ALLAH Zai Baka Mafita,
Kuma Ya Nuna Mana Cewa Ba'a Kwance Ashe
Wai ALLAH Kawo Mani,
Idan Muka Koma Kan Magana Ta Sanadi, Tana
Nufin Ka Tashi Ka Nema, Mai Da Kayanka Ga
ALLAH, Yarda Babu Mai Kawo Hasara Ko Riba
Sai ALLAH,
Kissar Annabi Yunusa Tazo A Cikin Alqur'ani Mai
Girma Cewa Lokachin Da KIFI YA HADEYASA YA
KOMA GA ALLAH INDA YAKAMA FADIN ''TSARKI
YA TABBATA GAREKA KAI KADAI, TSARKI YA
TABBATAR MAKA LALLAI NI NA ZALUNCI
KAINA''
Kunga Wannan Kisar Ta Nuna Mana Yadda
Annabi Yunusa Ya Maida Dogaron ALLAH Kuma
ALLAH Yabasa Mafita Ta Hanyar Fitar Dashi
Daga Bakin Kifin, Amma Duk Da Haka Yana Iya
Kokarinsa,
Yaku Yan Uwa Musulmi Idan Mukayi La'akari Da
Halin Da Muke Ciki A Wannan Zamanin Tabbas
Mafi Yawancin Mu, Mun Rasa Dogaro Ga ALLAH.
Yan Uwa Musulmi Wasu Daga Cikin Mu, Na Dora
Ko Kuma Aza Halin Da Muke Ciki Da Shugaban
Kasa Buhari!
Wanda Wannan Kuskure, Wallahi Sahabban
Annabi Sallallahu Alaihi Wasalam Sun Shiga Hali
Wanda Yafi Nanu Nesa Nesa, Ba Kusa Ba, Amma
Sun Maida Kayansu Ga ALLAH Kuma Yafitar
Dasu A Matsin Da Suka Tsinci Kansu,
A Yakin Badar Musulmi Sun Fito Su Dari Ukku Da
Sitti Wata Ruwaya, Arna Kuma Sun Kai Dubu Da
Wani Abu A Wata Ruwaya, Musulmi Qalilan Ne
Ke Saman Dawakai, Amma ALLAH S.W.T Ya
Basu Nasara Akan Kafurai Suna Ragargazasu
Suka Kore Su,
Duk Irin Hali Na Dadi, Ko Akasin Haka Mu Daina
Dangantawa Ga Mani Mu Maida Lamuran Mu Ga
ALLAH
YAN UWA DA FATAR KUN WUNI LAFIYA
NA SADAUKAR DA WANNAN RUBUTUN DA
NIYAR ALLAH YAKAI LADARSA GA MAHAIFINA,
Da Fatar Zamuyi Salati Ga Wanda Na Bada
Fansa Raina Data Iyayena A gareshi
ALLAHUMMA SALLI ALA MUHAMMAD WA ALA
ALI MUHAMMADIN WASSALIM

©®DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA

18/Rabi'u Auwal/1438
18/12/2016.

HUDUBAR JUMA'AH MAI TAKEN ZUMUNTA A MUSULUNCI.

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallacin Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani
Liman(ABU HURAIRA)

Yayi Hudubar Sane Akan
Muhimmancin Rike # ZUMUNTA_KO_KUMA
_SADA_ZUMUNTA
Bayan Yin Salati ga Manzon Tsira Sallallahu
Alaihi Wassalam, Da Kuma Yin Yabo ga ALLAH
Madaukakin Sarki''
Sai Sheik Sani Ya Fara Da Cewa Yaku Yan Uwa
Ku Sani ALLAH Ya Halicci Bayi Sa Ne Don Kawai
Mu Bauta Mashi Ashe Kuwa Babu Wani Dalili
Dazai Sa Muyi Sakaci A Fagen Bautawa Mai''
Haka Kuma ALLAH S.W,T Ya Wajabta Sada
Zumunta Tsakanin Yan Uwa Jini,
Sada ZUMUNTA Dai Bawai Kawai Ya Takaita Ga
Fada Cewa Wane Dan Uwa Nane, A.a, Dole Ne
Anga Wannan Kalma A Zahiri, Da Kuma
Aiwatarwa A Aikace,
Yaku Yan Uwa Musulmi Kusani Ana SADA
ZUMUNTA Ta Hanyoyi, Da Dama, Daga Cikin
Akwai Kyautatawa Ta Hamyar Basu Wani Ihsani,
Sannan Akwai Sakin Fuska, Akwai Jawo Su A
Jiki, Anan Akwai Gagarumar Matsala!
Sau Da Yawa Zakaga Wani Yana Kyautatawa Yan
Uwansa, Amma Baya Son Su Dinga Ziyatar Sa,
Ziyara Kuma Daya Ce, Daga Ciki Ko Kuma Itace
Ginshiki Wato PILLAR, Ta Zumunci!
Yan Uwa Musulmi Mu Jure Mu Yaki Shaidan A
Tsakanin Mu, Domin Shaidani Shine Babban
Wanda Ke Sanya Mana Dogon Lokaci Idan
Mukayi Niyar Zuwa Ziyara, Zakaga Kayi Niyar
Zuwa Ziyara Amma Shaidan L.A Sai Yace Maka
A.a Bari Ka Kara Samun Kudi, Wanda Babu
Ranar Dazaka Same Su, Muddin Kana Sanya
Rana Irin Haka!
Malamai Magada Annabawa Sunyi Mana Nasihohi
Kamar Haka,
1.DUK WANDA YA YANKE ZUMUNCI GAREKA TO
KA SADAR MASA
2.DUK MAI FUSHI DAKAI KAYI MASA MAGANA
KODA BAYA AMSAWA
3.YAWAN ZIYARA YANA KARA DANKON
ZUMUNTA
4.IDAN MA HAR BAKA SAMU DAMAR ZIYARAR
BA, TO KIRAN SU TA WAYA MA ZAI TAIMAKA
AMMA BAI WADATAR BA
5.A KALLA KA KIRA YAN UWANKA KODA SAU
DAYA NE BAYAN KWANAKI GOMA
6.JURIYA TARE DA HAKURI,TARE DA GANI
AMMA KAYI KAMAR BAKA GANI BA
Hadisi Yazo Daga Manzon Tsira Cewa ZUMUNTA
Tana Addu'a Kullun Tana Cewa YA ALLAH DUK
WANDA YASADA NI, KASADA SHI DA
RAHAMARKA, DUK WANDA YA KATSE NI, KA
KATSE SHI DAGA RAHAMARKA
Daga Karshe Muna Fatar Yan Uwa Zamu Gyara
Zumuntar Mu, Tsakanin Mu Dan Yan Uwan Mu.
NA SADAUKAR DA WANNAN RUBUTUN DA
NIYAR ALLAH YAKAI LADARSA GA MAHAIFINA,
Da Fatar Zamuyi Salati Ga Wanda Na Bada
Fansa Raina Data Iyayena A gareshi

HUDUBAR JUMA'AH MAI TAKEN BIYAYYA GA IYAYE

HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Masallacin Jumu'a Na
Ukku Dake  Area II Tsafe Sheik Sani
Liman(ABU HURAIRAH)
Yayi Hudubar Sane Akan
Muhimmancin #BIYAYYA_GA_IYAYE
Bayan Yin Salati ga Manzon Tsira Sallallahu
Alaihi Wassalam, Da Kuma Yin Yabo ga ALLAH
Madaukakin Sarki''
Sai Sheik Sani Ya Fara Da Cewa Yaku Yan Uwa
Ku Sani ALLAH Ya Halicci Bayi Sa Ne Don Kawai
Mu Bauta Mashi Ashe Kuwa Babu Wani Dalili
Dazai Sa Muyi Sakaci A Fagen Bautawa Mai''
Hakan Tasa Ya Umurci Bayin Sa , Dayimai
Biyayya,
Sai Kuma Yasanya Biyayya Ga Iyaye Tare Da
Tasa, Yin Biyayya Ga Iyaye Dole Dole Dole Ne,
Ana Yiwa Iyaye Biyayya Akowane Halli in Banda
idan suka umarce ka da Sabon ALLAH''
Ana Fifita yiwa uwa biyayya fiye da uba kamar
yadda daya daga cikin hadisan annabin rahama,
ya nuna mana,
Zakalika annabi rahama yafada a wani hadisin
cewa YAR DAR ALLAH TANA TARE DA YARDAR
IYAYE HAKAMA FUSHIN ALLAH YANA TARE DA
FUSHIN IYAYE''
Akwai Wani nauyi wanda iyaye keda shi kan
mutun idan sun rassu , daga cikin wadannan
nauyin akwai, Yi Masu Addu'a Bayan Basu
duniya, Sada zumuntar da suke sadawa idan su
nan, girmama yan uwansu da abonkasu, da dai
saurasu,
Yaku Yan Uwa Musulmi Ku Sani duk wanda ya
mutu iyayensa basajin dadin sa, to TABBAS
BAYA SHIGA
Yaku yan uwa kunji wata babbar magana!
Daga karshe ina fatar kowa zai kara gyara
zamantakewar sa da iyayens, wanda kuma nasa
basanan zai bi waccan hadisin daya gabata,
muna rokon ALLAH Yagafarta masu gaba daya,
Nima Mahaifina Ya Rassu Ina roko masa gafarar
ALLAH,Game da kurakurar daya gabatar a
rayuwar sa,
NA SADAUKAR DA WANNAN RUBUTUN DA
NIYAR ALLAH YAKAI LADARSA GA MAHAIFINA,
Da Fatar Zamuyi Salati Ga Wanda Na Bada
Fansa Raina Data Iyayena A gareshi
ALLAHUMMA SALLI ALA MUHAMMAD WA ALA
ALI MUHAMMADIN WASSALIM

©®DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA

11/Safar/1438

11/11/2016.

Wednesday, 6 December 2017

HANI KAN TSAGA JIKI DAGA LITTAFAN SHI'AH

HANI KAN DUKAN JIKI KO TSAGA TUFA KO
IHOCE-IHOCE YAYIN WATA MUSIBA, BAFA CIKIN
LITATTAFAN SUNNAH KURUM YAZOBA, YA
TABBATA HATTA CIKIN LITATTAFAN
SHI'A.........

Daga: Malam Abdurrazak Uba Musa

Bari indan fitoda koda dozin dayane daga cikin
ruwayoyin :
ﺍﻟﻨﻴﺎﺣﺔ ﻣﻦ ﻋﻤﻞ ﺍﻟﺠﺎﻫﻠﻴﺔ . ‏( ﻭﺳﺎﺋﻞ ﺍﻟﺸﻴﻌﺔ ١٢ /٩١٥
ﺑﺤﺎﺭ ﺍﻷﻧﻮﺍﺭ ٨٢ /١٠٣ )
Ihoce-ihoce na daga aikin jahiliyya.
ﻧﻬﻰ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺁﻟﻪ ﻋﻦ ﺍﻟﺮﻧﺔ ﻋﻨﺪ ﺍﻟﻤﺼﻴﺒﺔ ﻭﻧﻬﻰ ﻋﻦ
ﺍﻟﻨﻴﺎﺣﺔ ﻭﺍﻻﺳﺘﻤﺎﻉ ﺇﻟﻴﻬﺎ . ‏( ﻭﺳﺎﺋﻞ ﺍﻟﺸﻴﻌﺔ ٢ /٩١٥ )
Annabi yayi hani ga daga sauti yayin kuka,da
ihoce-ihoce,da kuma jiyarda kukan yayin faruwar
musiba.
ﻗﺎﻝ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺁﻟﻪ ﻭﺳﻠﻢ : ‏( ﺻﻮﺗﺎﻥ
ﻣﻠﻌﻮﻧﺎﻥ ﻳﺒﻐﻀﻬﻤﺎ ﺍﻟﻠﻪ ،ﺃﻋﻮﺍﻝ ﻋﻨﺪ ﻣﺼﻴﺒﺔ ﻭﺻﻮﺕ ﻋﻨﺪ
ﻧﻌﻤﺔ، ﻳﻌﻨﻲ " ﺍﻟﻨﻮﺡ ﻭﺍﻟﻐﻨﺎﺀ ‏) ‏( ﻣﺴﺘﺪﺭﻙ ﺍﻟﻮﺳﺎﺋﻞ
ﻟﻠﻨﻮﺭﻱ . ١/١٤٤ ، ﺑﺤﺎﺭ ﺍﻷﻧﻮﺍﺭ ٨٢ /١٠١ )
Sautika 2 ababen tsinewane,Allah baya sansu,
daga murya da kuka yayin wata musiba,da daga
murya yayin farinciki.
ﻋﻦ ﺃﺑﻲ ﻋﺒﺪ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﺍﻟﺴﻼﻡ ﻗﺎﻝ : ﻻ ﻳﺼﻠﺢ ﺍﻟﺼﻴﺎﺡ
ﻋﻠﻰ ﺍﻟﻤﻴﺖ ﻭﻻ ﻳﻨﺒﻐﻲ، ﻭﻟﻜﻦ ﺍﻟﻨﺎﺱ ﻻ ﻳﻌﺮﻓﻮﻥ .
‏(ﺍﻟﻜﺎﻓﻲ ٣/٢٢٦ ، ﺍﻟﻮﺍﻓﻲ ١٢ /٨٨ ، ﻭﺳﺎﺋﻞ ﺍﻟﺸﻴﻌﺔ ٢ /٩١٦ )
Bai kyautuba kururuwa yayin mutuwa,bakuma ta
kamata ba,Amma kash 'yan Shi'a basu saniba.
}ﻛﺘﺎﺏ ﺍﻹﻣﺎﻡ ﻋﻠﻲ ﻋﻠﻴﻪ ﺍﻟﺴﻼﻡ ﺇﻟﻰ ﺭﻓﺎﻋﺔ ﺑﻦ ﺷﺪﺍﺩ :{
ﻭﺇﻳﺎﻙ ﻭﺍﻟﻨﻮﺡ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﻤﻴﺖ ﺑﺒﻠﺪ ﻳﻜﻮﻥ ﺻﻮﺕ ﻟﻚ ﺑﻪ
ﺳﻠﻄﺎﻥ
‏( ﻣﺴﺘﺪﺭﻙ ﺍﻟﻮﺳﺎﺋﻞ ١/١٤٤ )
Rubutun sayyidi Ali zuwa ga rifa'a, yace dashi:-
Kashedinka ga kuka yayin mutuwa.
ﻋﻦ ﺍﻟﺼﺎﺩﻕ ﻋﻠﻴﻪ ﺍﻟﺴﻼﻡ ﻗﺎﻝ :
ﻣﻦ ﺿﺮﺏ ﻳﺪﻩ ﻋﻞ ﻓﺨﺬﻩ ﻋﻨﺪ ﺍﻟﻤﺼﻴﺒﺔ ﺣﺒﻂ ﺃﺟﺮﻩ .
‏( ﻭﺳﺎﺋﻞ ﺍﻟﺸﻴﻌﺔ ٢ /٩١٤ )
Duk Wanda ya doki cinyarsa da hannunsa yayin
musiba,to ya rushe ladansa.
ﻋﻦ ﺃﺑﻲ ﻋﺒﺪ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﺍﻟﺴﻼﻡ ﻗﺎﻝ : ﻻ ﻳﻨﺒﻐﻲ ﺍﻟﺼﻴﺎﺡ
ﻋﻠﻰ ﺍﻟﻤﻴﺖ ﻭﻻ ﺗﺸﻖ ﺍﻟﺜﻴﺎﺏ .
‏( ﺍﻟﻜﺎﻓﻲ ٣ /٢٢٥ ، ﻭﺳﺎﺋﻞ ﺍﻟﺸﻴﻌﺔ ٢ /٩١٦ )
Bai kamata ba kuka yayin mutuwa da kuma yaga
tufafi.
ﺃﻥ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺁﻟﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻗﺎﻝ : ﻟﻌﻦ
ﺍﻟﻨﺎﺋﺤﺔ ﻭﺍﻟﻤﺴﺘﻤﻌﺔ . ‏(ﻣﺴﺘﺪﺭﻙ ﺍﻟﻮﺳﺎﺋﻞ ١/١٤٤ )
An tsinewa mai koke-koke da kuma mai jiyar da
kukan.
ﻋﻦ ﺃﺑﻲ ﺟﻌﻔﺮ ﻋﻠﻴﻪ ﺍﻟﺴﻼﻡ ﻗﺎﻝ : ﺃﺷـﺪ ﺍﻟﺠﺰﻉ ﺍﻟﺼﺮﺍﺥ
ﺑﺎﻟﻮﻳﻞ ﻭﺍﻟﻌﻮﻳﻞ ﻭﻟﻄﻢ ﺍﻟﻮﺟﻪ ﻭﺍﻟﺼﺪﺭ، ﻭﺟﺰ ﺍﻟﺸﻌﺮ ﻣﻦ
ﺍﻟﻨﻮﺍﺻﻲ، ﻭﻣﻦ ﺃﻗﺎﻡ ﺍﻟﻨﻮﺍﺣﺔ ﻓﻘﺪ ﺗﺮﻙ ﺍﻟﺼﺒﺮ، ﻭﺃﺧﺬ ﻓﻲ
ﻏﻴﺮ ﺍﻟﻄﺮﻳﻘﺔ . ‏( ﺍﻟﻜﺎﻓﻲ ٣/٢٢٣ ، ﻭﺳﺎﺋﻞ ﺍﻟﺸﻴﻌﺔ ٢ /٩١٥ ،
ﺑﺤﺎﺭ ﺍﻷﻧﻮﺍﺭ ٨٢ /٧٦ ) .
Duk Wanda ya tsayu ga koke-koke Haqiqa yabar
haquri,kuma yayi ruqo da hanyar da ba ta gaskiya
ba.
ﻋﻦ ﺃﺑﻲ ﺍﻟﻤﻘﺪﺍﻡ ﻗﺎﻝ : ﺳﻤﻌـﺖ ﺃﺑﺎ ﺍﻟﺤﺴﻦ ﻭﺃﺑﺎ ﺟﻌﻔﺮ
ﻋﻠﻴﻬﻤﺎ ﺍﻟﺴﻼﻡ ﻳﻘﻮﻝ ﻓﻲ ﻗﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﺰ ﻭﺟﻞ }: ﻭﻻ
ﻳﻌﺼﻴﻨﻚ ﻓﻲ ﻣﻌﺮﻭﻑ { ‏( ﻗﺎﻝ : ﺇﻥ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺁﻟﻪ
ﻟﻔﺎﻃﻤﺔ ﻋﻠﻴﻬﺎ ﺍﻟﺴﻼﻡ : ﺇﺫﺍ ﺃﻧﺎ ﻣُـﺖ ﻓـﻼ ﺗﺨﻤﺸﻲ ﻋﻠﻲّ
ﻭﺟﻬﺎ ﻭﻻ ﺗﺮﺧﻲ ﻋﻠﻲّ ﺷﻌﺮﺍ ﻭﻻ ﺗﻨﺎﺩﻱ ﺑﺎﻟﻮﻳﻞ ﻭﻻ ﺗﻘﻴﻤﻦ
ﻋﻠﻲّ ﻧﺎﺋﺤﺔ، ﻗﺎﻝ : ﺛﻢ ﻗﺎﻝ : ﻫﺬﺍ ﻫﻮ ‏( ﺍﻟﻤﻌﺮﻭﻑ ‏) ﺍﻟﺬﻱ
ﻗﺎﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﺰ ﻭﺟﻞ (( ﻭﻻ ﻳﻌﺼﻴﻨﻚ ﻓﻲ ﻣﻌﺮﻭﻑ .
)) ﻭﺳﺎﺋﻞ ﺍﻟﺸﻴﻌﺔ ٢ /٩١٥ -٩١٦ ، ﻣﺴﺘﺪﺭﻙ ﺍﻟﻮﺳﺎﺋﻞ ١/١٤٤ )
Annabi yace da Nana Fadima : Idan nakoma ga
Allah kar kiyi kiran Na mutu na Lalace,kar kuma
kiyimin kururuwa.
ﻗﻮﻝ ﺍﻟﺤﺴﻴﻦ ﻋﻠﻴﻪ ﺍﻟﺴﻼﻡ ﻷﺧﺘﻪ ﺯﻳﻨﺐ : ‏( ﻳﺎ ﺃﺧﺘﺎﻩ
ﺃﻗﺴﻤﺖ ﻋﻠﻴﻚ ﻓﺄﺑﺮﻱ ﻗﺴﻤﻲ، ﻻ ﺗﺸﻘﻲ ﻋﻠﻲّ ﺟﻴﺒﺎ ﺟﻴﺒﺎ
ﻭﻻ ﺗﺨﻤﺸﻲ ﻋﻠﻲّ ﻭﺟﻬﺎ، ﻭﻻ ﺗﺪﻋﻲ ﻋﻠﻲّ ﺑﺎﻟﻮﻳﻞ ﻭﺍﻟﺜﺒﻮﺭ
ﺇﺫﺍ ﻫﻠﻜﺖ ‏) ﻣﺴﺘﺪﺭﻙ ﺍﻟﻮﺳﺎﺋﻞ ١/١٤٤ )
Imam Husain ya fadawa 'yar uwarsa zainab
cewa: idan nakoma ga Allah to karki keta
tufarki,karkiyi kyruruwar jahiliyya.
ﺃﻥ ﻋﻠﻴﺎً ﻋﻠﻴﻪ ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻪ ﻗﺎﻝ : ﻣﻦ ﺿﺮﺏ ﻳﺪﻩ ﻋﻨﺪ
ﻣﺼﻴﺒﺔ ﻋﻠﻰ ﻓﺨﺬﻩ ﻓﻘﺪ ﺣﺒﻂ ﻋﻤﻠﻪ . ‏(ﺍﻟﺨﺼﺎﻝ ﻟﻠﺼﺪﻭﻕ
ﺹ ٦١٢ , ﻭﺳﺎﺋﻞ ﺍﻟﺸﻴﻌﺔ ٣/٢٧٠ ) .
Sayyidi Ali yace: Duk Wanda wata musiba
tazomasa sai ya maka hannunsa kan cinyarsa,to
babu shakka ya rushe aikinsa.
BABBAN ABIN TAMBAYAR ANAN SHINE :-
WANNAN ABIN DA 'YAN SHI'A SUKEYI NA
AZABTAR DAKAI A INA SUKA SAMOSHI ??
ME YASA BASA AIKI DA WADANNAN
RUWAYOYIN DA DUKAI HANI KAN HAKA ??

MATSAYAR SALAFIYYA KAN KASHE JIKAN MANZON ALLAH S.A.W

MATSAYAR SALAFIYYA KAN KASHE JIKAN
MANZAN ALLAH ALHUSSAIN ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻪ .......

Daga:Malam Abdurrazak Uba Musa

Shehin musulunci ibn taimiya yake cewa:-
ﻓﻼ ﺭﻳﺐ ﺃﻥ ﻗﺘﻞ ﺍﻟﺤﺴﻴﻦ ﻣﻦ ﺃﻋﻈﻢ ﺍﻟﺬﻧﻮﺏ ﻭﺃﻥ ﻓﺎﻋﻞ
ﺫﻟﻚ ﻭﺍﻟﺮﺍﺿﻲ ﺑﻪ ﻭﺍﻟﻤﻌﻴﻦ ﻋﻠﻴﻪ ﻣﺴﺘﺤﻖ ﻟﻌﻘﺎﺏ ﺍﻟﻠﻪ . @
‏(ﻣﻨﻬﺎﺝ ﺍﻟﺴﻨﺔ ﺍﻟﻨﺒﻮﻳﺔ ٤ /٥٦٠ )
Babu makawa/shakka tabbas kashe Alhussain na
daga mafi girman zunubai,kuma Haqiqa Wanda
yayi kisan,da Wanda ya yarda da kisan,da Wanda
ya taimaka da wani Abu wajan kisan, duk sun
can-can ci azabar Allah.
Anan Shehin ya bayyana cewa:- kisan yana cikin
ﺃﻋﻈﻢ ﺍﻟﺬﻧﻮﺏ mafiya girman zunubai.
Sannan ya bayyana cewa:- Wanda yayi da Wanda
ya taimaka da Wanda ya yarda,duk sun can-can
ci Allah ya azabtar dasu.
Shehin yakuma cewa :-
ﻭﺃﻣﺎ ﻣﻘﺘﻞ ﺍﻟﺤﺴﻴﻦ ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻪ ﻓﻼ ﺭﻳﺐ ﺃﻧﻪ ﻗﺘﻞ
ﻣﻈﻠﻮﻣﺎ ﺷﻬﻴﺪﺍ ﻛﻤﺎ ﻗﺘﻞ ﺃﺷﺒﺎﻫﻪ ﻣﻦ ﺍﻟﻤﻈﻠﻮﻣﻴﻦ ﺍﻟﺸﻬﺪﺍﺀ
ﻭﻗﺘﻞ ﺍﻟﺤﺴﻴﻦ ﻣﻌﺼﻴﺔ ﻟﻠﻪ ﻭﺭﺳﻮﻟﻪ ﻣﻤﻦ ﻗﺘﻠﻪ ﺃﻭ ﺃﻋﺎﻥ
ﻋﻠﻰ ﻗﺘﻠﻪ ﺃﻭ ﺭﺿﻰ ﺑﺬﻟﻚ @. ‏( ٤ /٥٥٠ )
Amma kisan Alhussain ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻪ babu
makawa tabbas An kashe Alhussain yana abin
zalunta kuma shaheedi,kamar yanda aka kashe
makamantansa suna ababan zalunta kuma
shahidai.
Kashe Alhussain Sabon Allah ne da manzo,ga
Wanda yai kisan ko ya taimaka kan kisan ko ya
yarda da kisan.
Anan kuma Shehin ya bayyana cewa :- Kashe
Alhussain zaluncine.
Sannan kuma ya bayyana cewa:- Alhussain
shahadace yayi.
Sannan Shehin ya bayyana cewa:- Mai kisan da
Wanda ya taimaka masa,da Wanda ya yarda,duk
sun sabawa Allah da manzan Allah.
Anyiwa shin musulunci tambaya hukuncin Wanda
ya kashe jikan manzan Allah Alhussain ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ
ﻋﻨﻪ, sai yace:-
ﻭﺃﻣﺎ ﻣﻦ ﻗﺘﻞ " ﺍﻟﺤﺴﻴﻦ " ﺃﻭ ﺃﻋﺎﻥ ﻋﻠﻰ ﻗﺘﻠﻪ ﺃﻭ ﺭﺿﻲ
ﺑﺬﻟﻚ ﻓﻌﻠﻴﻪ ﻟﻌﻨﺔ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺍﻟﻤﻼﺋﻜﺔ ﻭﺍﻟﻨﺎﺱ ﺃﺟﻤﻌﻴﻦ ؛ ﻻ
ﻳﻘﺒﻞ ﺍﻟﻠﻪ ﻣﻨﻪ ﺻﺮﻓﺎ ﻭﻻ ﻋﺪﻻ . @. ‏( ﻣﺠﻤﻮﻉ ﻓﺘﺎﻭﻯ
١/٣٩٢ )
Amma Wanda ya kashe Alhussain, ko yataimaka
kan kisan ko ya yarda da kisan,to tsinuwar Allah
data mala'iku,data baki dayan mutane ta tabbata
akansa,kuma Allah bazai karbi farillarsaba da
nafilarsa.
Anan kuma Shehin ya bayyana cewa:- Wanda
yayi kisan da Wanda ya taimaka kan kisan da
Wanda ya yarda da kisan, duk tsinannune.
ALLAH TA'ALA KA QARA TABBATAR DA
AZABARKA GA MAKASAN JIKAN MANZAN
ALLAH DA WADANDA SUKA TAIMAKA WAJAN
KISAN

AQEEDUN YAN TIJJANIYYA

AQEEDU GOMA DAGA AQEEDUN TIJJANIYYA!! ANYI WALQIYA.....!!;> AQEEDA TA FARKO ...................................... SHEIKH AHMADU TIJJANI ACIKIN CONSITUITION DIN TIJJANIYYA WATO JAWAHIRIL MA,ANIY YACE: ﺇﻥ ﻫﺬﺍ ﺍﻟﻮﺭﺩ ﺍﺩﺧﺮﻩ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻟﻲ ﻭ ﻟﻢ ﻳﻌﻠﻤﻪﻷﺣﺪ ﻣﻦ ﺃﺻﺤﺎﺑﻪ ( – ﺇﻟﻰ ﺃﻥ ﻗﺎﻝ :- ) ﻟﻌﻠﻤﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﺑﺘﺄﺧﻴﺮ ﻭﻗﺘﻪﻭﻋﺪﻡ ﻭﺟﻮﺩ ﻣﻦ ﻳﻈﻬﺮﻩ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﻳﺪﻳﻪ WANNAN WURIDIN ANNABINE YA ADANA MINI SHI BAI SANAR DA KOWA BA DAGA ­SAHABBANSA-----­
SABODA ANNABI YASAN LOKACINSA BAIZOBA SABODA BABU WANDA ZAI IYA BAIYANASHI AWANCAN LOKACIN!!!

DUBI YANDA YA JINGINAWA MANZON ALLAH BOYE ILIMI BAYAN ALLAH YANA CEWA: : ﻳﺎ ﺃﻳﻬﺎ ﺍﻟﺮﺳﻮﻝﺑﻠﻎ ﻣﺎ ﺃﻧﺰﻝ ﺇﻟﻴﻚ ﻣﻦ ﺭﺑﻚ SURATL MA IDA: 67 DUBI YADDA YA FIFITA KANSA AKAN ABUBAKAR DA UMAR DA USMAN DA ALI DA AHLUL BAITI DA SAURAN SAHABBAI DUK ANNABI BAI KOYA MUSU WURIDIN TIJJANIYYA BA SABODA BAZASU IYA KOYAWA MUTANE BA SAI BAYAN ANNABI YABAR DUNIYA SAMA DA SHEKARA DUBU! AKA HAIFI TIJJANI SAI ANNABI YA DAWO DUNIYA YA BASHI WANNAN WURIDI!!!!!

YANZU YA KAMATA MAI LAFIYAYYEN  HANKALI YA YARDA DA WANNAN?

AQEEDA TA BIYU ------------------- AHAMADU TIJJANI YACE: ﺇﻥ ﺍﻟﻤﺮﺓ ﺍﻟﻮﺍﺣﺪﺓ ﻣﻦ ﺻﻼﺓ ﺍﻟﻔﺎﺗﺢ ﺗﻌﺪﻝ ﻛﻞ ﺗﺴﺒﻴﺢ ﻭﻗﻊ ﻓﻲ ﺍﻟﻜﻮﻥ ﻭﻛﻞ ﺫﻛﺮ ﻭﻛﻞ ﺩﻋﺎﺀ ﻛﺒﻴﺮ ﺃﻭ ﺻﻐﻴﺮ ﻭﺗﻌﺪﻝ ﺗﻼﻭﺓ ﺍﻟﻘﺮﺁﻥ ﺳﺘﺔ ﺁﻻﻑ ﻣﺮﺓ " SALATUL FATI DAI DAI YAKE DA KOWANE IRIN TASBIHI DA AKAI ABAYAN QASA, HAKA KOWACE ADDU,A BABBA DA QARAMAR TA KUMA YIN SALATIL FATI DAYA DAI DAI YAKE DA SAUKE ALQUR,ANI SAU DUBU SHIDA!!! duba jawahiril ma,ani: shafi:96 bugun attaqaddumul,ilmiyya. Bugu na farko. Dubi yanda wannan mutum ya fifita salatilfati akan qur,ani mai girma!!!!

ﺇﻥ ﺍﻟﺬﻳﻦ ﻳﻔﺘﺮﻭﻥ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﻜﺬﺏ ﻻﻳﻔﻠﺤﻮﻥ ﻣﺘﺎﻉ ﻗﻠﻴﻞ ﻭﻟﻬﻢ ﻋﺬﺍﺏ
ﺃﻟﻴﻢ{ ] ﺍﻟﻨﺤﻞ 116 117].

AQEEDA TA UKU ------------------- AHAMDU TIJJANI YACE: ﻗﺎﻝ ﻓﻲ ﺍﻹﻓﺎﺩﺓ : ) ﻣﻦ ﻟﻢ ﻳﻌﺘﻘﺪﺃﻧﻬﺎ – ﺃﻱ ﺻﻼﺓ ﺍﻟﻔﺎﺗﺢ – ﻣﻦ ﺍﻟﻘﺮﺁﻥ ﻟﻢ ﻳﺼﺐ ﺍﻟﺜﻮﺍﺏ ﻓﻴﻬﺎ ( " ﺹ 80 ".

DUK WANDA BAI YADDA SALATIL FATI ITAMA QUR,ANI BACE KO YAYI BASHI DA LADA!!! duba ifadatul ahmadiyya shafina:80
TO INA MASU SALATIL FATI? KODAI KU YADDA SALATIL FATI QUR,ANI CE WALLAHI IN KUKA FADI KUNYI RIDDA! KO KUMA BAKU YADDABA TO ANAN KUMA KUDA TIJJANI TUNDA GA ABINDA YA FADA: BAKU DA LADA!!! ZAKUJI SAURAN INSHA ALLAHU AKAN AQEEDA TA HUDU IN SHA ALLAH

ﻭﻻ ﺗﻘﻮﻟﻦ ﻟﺸﻲﺀ ﺇﻧﻲ ﻓﺎﻋﻞ ﺫﺍﻟﻚ ﻏﺪﺍ . ﺇﻻ ﺃﻥ ﻳﺸﺎﺀ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺍﺫﻛﺮ ﺭﺑﻚ ﺇﺫﺍ ﻧﺴﻴﺖ ﻭﻗﻞ ﻋﺴﻰ ﺃﻥ ﻳﻬﺪﻳﻨﻲ ﺭﺑﻲ ﻷﻗﺮﺏ ﻣﻦ ﻫﺬﺍ ﺭﺷﺪﺍ

ALLAH YA QARA KAREMU DAGA WADANNAN AQEEDUN NA SUFAYE!!!