Sunday, 9 February 2020

SUJADAR SAHU A SALLAH

*LIMAN NE YAKE SALLAH DA MUTANE, SALLAH MAI RAKA'A HUDU, BAYAN YA DAGO DAGA SUJADA TA BIYU A RAKA'A TA UKU SAI YA ZAUNA YANA ZATON A RAKA'A TA HUDU YAKE, SAI MAMU SUKAYI MASHI TASBIHI DA SAURI, SAI YA TASHI ZUWA RAKA'A TA HUDU DA SAURI, BAYAN WANCAN ZAMAN DA YAYI DAN KADAN(KAMAR ZAMAN JALSATIL ISTIRAHAH) ZAIYI SUJUDUS SAHAWY NE KO KUWA?*

*_AMSA_*

Idan liman ya zauna a Raka'a ta uku da mantuwa, zaiyi sujada biyu(kafin sallama). Saboda fadar Manzon Allah S.A.W cewa:
لكل سهو سجدتان
Ko wace mantuwa tana da sujada biyu, *Imamu Ahmad da Abu Daud suka fitar da hadisin*

Ibn Qudama Al-maqadisy(RH) a cikin *AL-MUGNY* yace: _Idan Liman ya zauna ba a wurin da ake tahiya ba kwatankwacin *JALSATIL ISTIRAHAH,* zaiyi sujada (kafin Sallama), duka dayane, koda zamu fadi cewa jalsatil istirahah Sunnah ce a cikin Sallah,(ko bamu ce ba) domin shi Mai sallar baiyi nufin cewa jalsatil istirahah yayi ba, yayi nufin waninta(zaton cewa Yana tahiya ta karshe ne) kenan ta zama mantuwa, koda bai yi sujada biyu kafin Sallama ba, sallar shi tayi, domin wani aiki ne yayi Dan kadan a cikin Sallah, shi Kuma aiki Dan kadan bai bata Sallah...._

Haka idan kuka duba a cikin:
كشاف القناع (1/395)
Ya kawo kwatankwacin wannan maganar, ya Kara da hadisin Abdullahi Dan Masa'ud dake cikin Muslim cewa:
فإذا زاد الرجل أو نقص في صلاته فليسجد سجدتين
Idan mutum yayi Qari ko ragi a cikin Sallah zaiyi sujada guda biyu.

Ash-Sheikh Muhammad bin Salih Almunajjid(Hafizahullah) yake cewa:
لكن إذا لم يسجد الإمام للسهو، ظنا منه أنه لا يلزمه السجود، أو نسيانا منه للسجود، فصلاته صحيحة.
Sai dai, idan Liman baiyi sujadar sahawun ba, ko yayi tunanin cewa ba dole bane sai yayi sujadar, ko Kuma ya manta, sallar shi ingantatta ce.

Wannan shine abin da yake na dai dai.

Allah yayi Mana muwafaqa a cikin Kyawawan ayyukan mu

#ABBAN_SINAN
+2348064734911
+2349030201868

Thursday, 30 January 2020

004 ZUMUNTA A MAHANGAR SHARI'AR MUSULUNCI

🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃
*ZUMUNTA A MAHANGAR SHARI'AR MUSULUNCI*
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂

Wallafar: *Ash-Sheikh Muhammad Sani Liman Tsafe (ABU HURAIRAH)*

_004_

*بسم الله الرحمن الرحيم*

✅ *SABUBBAN DA KE JANYO YANKE ZUMUNTA.*

   Idan kayi nazari akan sabubban dake janyo yanke zumunta zaka samu cewa akwai sabubba masu yawa. Ga kadan daga cikinsu
1. *JAHILCI:* Jahiltar mummunan sakamakon da mai yanke zumunta yake samu anan duniya da lahira, ko kuma rashin yin aiki da abin da mutum ya sani. An karbo daga Umar (R) ya kasance akan mimbari yana cewa: ku nemi sanin dangantakarku, sannan ku sadar da zumuntarku wallahi! Lallai zai kasance tsakanin mutum da dan uwansa wata rigima ta hadasu saboda rashin sanin juna, da yasan akwai zumunta tsakaninsu da wannan dalilin na alakar zumunta ya hanashi cin mutuncinsa *(Bukhari, Adabul mufrad 73)*

2. *KARANCIN TSORON ALLAH;*
  Idan tsoron Allah yayi rauni sannan addini yayi saku-saku ba zai damu ba idan ya yanke abin da Allah yayi umarnin asadar, kuma baya kwadayin ladar da ake samu idan an sadar da zumunta kuma baya tsoran mummunan sakamakon da zai same shi a dalilin yanke zumunta.
An karbo daga sa’id bn sam’an, yace: Naji Abu Hurairah yana neman tsarin Allah daga shugabancin yara da wawaye (jahilai) sai aka ce masa mine ne alamar yin haka? sai yace dan za’a dinga yanke zumunta a kuma dinga yin da’a ga mai halakarwa a saba ma mai shiryarwa *(Adabul-mufad 66)*

3. *GIRMAN KAI;*
  Sashen mutane idan mutum ya samu wani matsayi babba ko ya samu wata daukaka ko kuma ya zama babban dan kasuwa sai yayi girman kai ga yan'uwanshi, ya kyamaci ziyartarsu, kuma ya kyamaci zuwa garesu, yana ganin shi ke kan gaskiya kuma shi ya can-canta a ziyarta.

4. *YANKEWA MAI TSAWO;*
A nan akwai wanda yake yanke ma yan'uwansa lokaci mai tsawo al’amarin ya dore akan haka har ya kai ga yanke zumuntarshi dasu gaba daya, har ya saba da yankewa sai yayi nesa dasu. An karbo daga Mikdam, lallai yaji manzon Allah (SAW) yana cewa lallai Allah yana maku wasiyya da iyayenku mata sannan yana maku wasiyya da iyayenku maza, sannan yana maku wasiyya da yan'uwanku *(Adabul mufrad 60)*

5. *AIBANTAWA MAI TSANANI;*
Sashen wasu mutane idan dan'uwansu ya ziyarcesu bayan a baya ya yanke zumuntarshi dasu lokaci mai tsawo sai su yawaita zar ginshi har zargin yayi tsanani wanda wannan sai yasa shi kaurace masu saboda tsoron mummunan zargi da suke mashi.

6. *DORA MA RAI NAUYIN DAYA WUCE QA’IDA;*
A nan akwai wanda idan dan'uwansu ya ziyarcesu sai su dora ma kansu yin hidindimu da suka wuce karfinsu domin su ga cewa sun karrama dan'uwan nasu sama da karfinsu ko karancin abun hannunsu, wannan shi ke sanya yan'uwan nasu su dinga takaitawa da ziyartarsu domin tsoron kada su dora masu ire-iren wadannan nauye-nauyen. Saboda Annabi yace mafi karancin sadar da zumunci shine sallama mafi girman zumunta shine  sadarma wanda ya yanke maka.

7. *KARANCIN KULA DA WADANDA SUKA KAWO MAKA ZIYARA;*
  Akwai daga cikin mutane wanda idan yan'uwanshi suka ziyarceshi baya bayyanar da farin cikinsa akan ziyarar, bai tsayawa ya tattauna dasu ko ya sakar masu fuska, sai dai za ka ga yana bata rai yana kyamarsu, wannan yana zama sanadin yan'uwa ba zasu kara ziyartarshi ba dan tsoron irin wannan wulakancin.
Manzon Allah yace, kada ku wulakanta wani abu na alkhairi ko da sakin fuskane idan ka hadu da dan'uwanka.

8. *TSANANIN ROWA;*
  Wasu daga cikin mutane idan Allah ya azurtasu da dukiya mai yawa ko wani matsayi zaka same su suna gudun yan'uwansu, ba wai dan girman kai ba a'ah! Domin jin tsoron kada yan'uwan suyi amfani da wannan damar domin bayyanar da bukatunsu zuwa garesu, ko kuma domin kada ya temakesu. Maimakon ya basu dama idan sun ziyarceshi yakarbi bakuncinsu, ya yalwata masu, yayi masu hidima gwargwadon halinsa,ko kuma ya basu uzuri akan abin da ba ya da ikon yi masu amma sai kaga yana kauda kansa, yana kaurace masu domin kada su rokeshi kamar yadda yake riyawa. Mine ne amfanin dukiya ko matsayi da mutum zai samu idan har zai haramta ma yan'uwansa amfana da ita.
9. *JINKIRIN RABON GADO;*
Hakika zaka samu wasu daga cikin mutane suna jinkirta rabon gado kodai  domin kasala, ko kuma wani daga cikin magadan yana da wani mummunan kuduri game da yan'uwansa ko makamacin haka.
Duk lokacin da aka jinkirta rabon gado to kiyayya da adawa zata watsu tsakaninsu domin idan wannan yana da hali ko yafi karfin gadon wani shi kuma yana bukatar raba gadon domin bashi na shi kason ya samu ya bude kasuwanci ko makamanci haka.

10. *MUTUWAR AUREN ZUMUNCI;*
  Hakika mutuwar auren zumunci yana haifar da matsaloli a tsakanin yan'uwa na bangaren miji dana bangaren mata musamman in akwai 'ya'ya a tsakaninsu ko kuma saboda wasu matsaloli da suka shafi sakin auren.

A NAN ZAMU DAKATA SAI A LOKACI NA GABA INDA ZAKUJI CIGABAN *SABUBBAN DAKE JANYO YANKE ZUMUNTA*

DOMIN CIGABA DA SAMUN WANNAN RUBUTU KUNA IYA AIKEWA DA SAQON WHATSAPP ZUWA GA: +2349030201868 DOMIN SHIGA GROUP DIN *MU KYAUTATA NIYYA*

#ABBAN_SINAN
https://fb.me/abbansinan

003 ZUMUNTA A MAHANGAR SHARI'AR MUSULUNCI

🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃
*ZUMUNTA A MAHANGAR SHARI'AR MUSULUNCI*
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂

Wallafar: *Ash-Sheikh Muhammad Sani Liman Tsafe (ABU HURAIRAH)*

_003_

*بسم الله الرحمن الرحيم*

✅ *HADARIN  DA KE CIKIN YANKE ZUMUNTA*

Hakika Allah (SWT) da manzonsa (SAW) sun tsoratar dangane da hadarin yanke zumunci, suka sanya matsayin yanke zumunci dai dai da Fasadi/barna a bayan kasa.
Allah (SWT) yace to shin kuna fatan idan kun juya daga (umarnin) zakuyi barna a cikin kasa, kuma ku yanke zumuntarku? Wadannan sune wadanda Allah ya la'anesu, kuma ya kurmantar dasu, kuma ya makantar da ganinsu. *(Suratu Muhammad 22-23)*

An karbo hadisi daga Aisha (R) manzon Allah (SAW) yace zumunta tana rataye da al’arshin Allah. Tana cewa wanda ya sadar dani Allah ya sadar dashi, wanda ya yanke ni Allah ya yankeshi *(Muslim 2555)*
An karbo daga MUD’IM (R) manzon Allah (SWA) yace mai yanke zumunta baya shiga Aljanna *(Muslim 2556)*
Haka nan kuma, an karbo  daga Abubakrata, Manzon Allah yace, Babu wani laifi daya can-canta Allah ya gaggauta ma ma'abocin sa uquba tun anan duniya tare da  cewa yayi mashi tanadin uqubar a lahira kamar wanda ya yanke zumunta da kuma azzalimi *(Bukhari adabul mufrad 67)*
An karbo daga Abu Huraira; lallai wani mutum yace ya manzon Allah lallai ni ina da yan'uwa kuma ina sadar da zumuntarsu amman suna yanke mani, ina kyautata masu amma suna munana mani, ina yin hakuri dasu amma suna jahiltata? Sai Annabi yace, idan har ka kasance kamar yadda ka fada to lallai kamar kana zuba masu toka ce mai zafi, Allah ba zai gushe ba yana taimakonka akansu matukar ka dauwwama akan haka *(Muslim 2558)* Ma’ana: kamar kana ciyar dasu toka mai zafi saboda abin da suke haduwa dashi na laifi.
Haka nan kuma an karbo daga Abdullahi ibn Amru binul As, Manzon Allah (SAW) yace, bai zama mai sadar da zumunta ba wanda yake so aranka mashi, sai dai mai sadar da zumunta shine wanda idan an yanke mashi, shi yana sadarwa *(Bukhari 541)*
An karbo daga salmanu ibn Amir, Manzon Allah yace, yin sadaka ga miskinai sadakace kamar sauran sadakoki, amma yin sadaka ga dan'uwa tana da darajoji biyu (2) ladar sadaka da kuma ladar sadar da zumunci *(Abu Dawud 2555 da Tirmidhi 658)*
An karbo daga Abu Hurairah yace, lokacin da wannan ayar ta sauka,,, kayi gargadi ga yan'uwanka makusanta, Annabi (SAW) ya kira Quraishawa, suka hadu gaba dayansu, yayi musu wa’azi gaba dayansu kuma yayi ma dai-dai kunsu yace ya Fatima ki tsamar da kanki daga wuta, lallai ni bani wadatar daku a wurin Allah da komai sai dai lallai kuna da wata zumunta da sannu zan sadar da ita *(Muslim)*

ANAN ZAMU DAKATA SAI A LOKACI NA GABA INDA ZAKUJI *SABUBBAN DAKE JANYO YANKE ZUMUNTA*

DOMIN CIGABA DA SAMUN WANNAN RUBUTU KUNA IYA AIKEWA DA SAQON WHATSAPP ZUWA GA: +2349030201868
DOMIN SHIGA GROUP DIN *MU KYAUTATA NIYYA*

#ABBAN_SINAN
https://fb.me/abbansinan

KARATUTTUKAN MASALLACIN ABU HURAIRAH TSAFE

*MASJID ABU HURAIRAH TSAFE*

Wannan Masallaci karkashin kwamitin social media na masallacin sunyi kokarin tattara karatuttukan da *Ash-Sheikh Muhammad Sani Liman Tsafe (ABU HURAIRAH)* yake gabatarwa a wannan Masallaci har kusan littafai *36* gasu kamar haka:

1. *Aqeedatud dahawiyya*

2. *Ahkamul idaini*

3. *Alfurqan baina auliya'allahi wa'auliya'ish-shaidan*

4. *Ahkamul uduhiyya*

5. *Al'imamu wa'af'alihi*

6. *Al'ilmam, bi'ahkami wadabus siyam*

7. *Aljawabul khafi*

8. *Alwajibatul mutahattimatul ma'arifah.*

9. *Bugyatul mushtak*

10. *Bulugul maram*

11. *Daura- akan Magunguna da ruqya*

12. *Daura- akan Maulidi*

13. *Hisnul Muslim*

14. *Hiqbatun minat-tarikh*

15. *Hudubobi guda 166*

16. *Imani haske*

17. *La'ilaha ilallah*

18. *Manasikul hajji*

19. *Mayatamayyazu bihil muslimu anil mushrik*

20. *Mu'amalatul hukkam*

21. *Muhadarori*

22. *Nabiyur Rahma*

23. *Qa'idatul jalila*

24. *Ru'usul aqlam*

25. *Riyadus saliheen*

26. *Ramadhan Tafseer, 2007,10,13,16,17,18, da 2019*

27. *Salatut Tarawih*

28. *Sahihul bukhari*

29. *Shama'ilul Muhammadiyya*

30. *Sifatu saumun Nabiyy, kala biyu*

31. *Tarbiyatul aulad, kala 3*

32. *Tafseer weekly na ibn Katheer*

33. *Tuhfatul iraqiyya*

34. *Usulul iman*

35. *Usulus salasa*

36. *Wasiyyatul kubrah*

37. *Aqeedatul wasidiyya na (ibn taimiyya).*

38. *Adabuzzifaf na (Albany)*

39. *Fadlul Islam na (Muhammad bn abdulwahab)*

40. *Nawaqidul Islam na(Muhammad bn Abdulwahab)*

41. *kitabuttauhid na (Muhammad bn abdulwahab)*

42. *kitabuttauhid na (sheikh salhul fauzan)*

43. *Albida'ah*

44. *Sharhin sunnah na (Barbahary)*

45. *Kama takunu yuwalla alaikum na (dr. Ramadani)*

46. *Jilbabul m ar'atil Muslima na (Albany)*

47. *Huququn da'at ilaiha fidra waqarrarat'ha shari'a na(sheikh uthaimin)*

48. *Siyamu Ramadan*

49. *Qiyamu Raman.*

50. *Ahkamul jana'iz na (Albany)*

51. *Tafsirul kalimatul shahada.*

52. *Sifatus salatin nabiyy na (Albany)*

53. *Sharhi masa'ilil  jahiliyya na (Muhammad bn Abdul wahab)*

54. *Auradu ahlussunah.*

55. *Tabyini kazibul muftary bima nusiba ila ibn taimiyya na (M Kabir Maru).*

zamu cigaba da kawo wadan da muka tuna  daga baya insha Allahu

Wannan kwamiti na Nan na kokari kafin zuwa Ramadan za'a gabatar maku da 16GB memory card Mai dauke da Wadannan karatuttukan da ma wasu wadanda bamu shigar ba a Nan.

Allah ya sakawa Malam da Alkhairi

#MABUHURAIRAHTSAFE_SOCIAL_MEDIA

005 ZUMUNTA A MAHANGAR SHARI'AR MUSULUNCI

🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃
*ZUMUNTA A MAHANGAR SHARI'AR MUSULUNCI*
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂

Wallafar: *Ash-Sheikh Muhammad Sani Liman Tsafe (ABU HURAIRAH)*

_005_

*بسم الله الرحمن الرحيم*

✅ *CIGABA DA BAYANI AKAN SABUBBAN DA KE JANYO YANKE ZUMUNTA.*

11. *NISAN WURIN ZAMA DA KUMA KASALAR ZUWA ZIYARA*
Akwai daga cikin mutane wadanda idan gidan su ko garin su yana nesa sai a dinga jin kasalar zuwa ziyartarsu, wanda wannan sai ya nisantasu da yan'uwansu.
Nisan wuri bai kamata ba ya zama dalili na yanke zumunta, musamman wannan zamanin da ake da hanyoyin sadarwa daban daban, Allah ya bamu ikon kulawa da zumunta.

12. *MAKWABTAKA A TSAKANIN YAN UWA*
Da yawa Makwabtaka tana gadar da yankewar zumunta a tsakanin yan'uwa. Umar Dan khaddab yace ku umurci yan'uwanku su dinga ziyartar yan'uwansu amma kada suyi makwabtaka da juna a gidajensu, sannan sau dayawa kusanci a tsakanin gidajen yan'uwa yana haifar da sashen wasu matsaloli wadanda suke haifar da fada a tsakanin 'ya'yansu wanda wannan yakan zarce har zuwa ga iyayensu sai wannan ya haifar da gaba da yanke zumunci a tsakaninsu.

13. *KARANCIN KAUDA KAI DA HAKURI A KANSU:*
Sashen wasu mutane suna da karancin kauda kai da kuma hakuri akan abin da yan'uwansu suka yi masu. Wasu yan'uwan da an samu sabani tsakaninsu ko wani kuskure da ya afku sai su yanke zumunta, su kaurace ma yan'uwansu.

14. *HASSADA:*
   Akwai daga cikin yan’uwa wanda Allah yake azirtawa da ilimi ko wani babban matsayi ko dukiya mai yawa sai ka same shi yana yima yan'uwansa hidima yana kyautata ma su, sannan ka samu sashen yan'uwansa suna nuna masa hassada da kiyayya da haifar da rikici tsakanin shi da su, suna cewa duk abin da yake yi masu ba domin Allah yake yi ba.

15. *YAWAN WASA:*
Lallai yawan wasa (da sunan wai abokin wasa) yana haifar da mummunan abu a tsakanin yan'uwa domin wani yana iya fadar kalma mai muni ga dan'uwansa ba tare da ya kula da hadarinta ba agare shi, wannan sai ya gadar da kiyayya da gaba a tsakaninsu a sanadiyyar wannan Kalmar.

16. *ANNAMIMANCI DA KARBAR GULMA:*
Akwai da yawa daga cikin yan'uwa wadanda dabi'arsu shine yawo da annamimanci a tsakanin yan'uwa domin su kawo rabuwar kai da gurbata tsakanin yan’uwa wanda wannan yana gadar da yanke zumunta, sai dai abu mafi muni shine karbar gulma da yadda da ita shi ke haifar da yankewar zumunta.

17. *SHAGALTUWA DA DUNIYA:* Shagaltuwa da duniya da son yawan tara abin duniya yana hana mutun sadar da zumunta, da kuma samun lokacin ziyartar yan'uwansa da nuna soyayyar shi zuwa gare su.

18. *MIYAGUN HALAYE NA MATAR SHI:*
Wasu daga cikin mutane ana jarabtarsu da muguwar mata mai mummunan dabi’a mai yawan sukar yan'uwansa, bata son yayi mu’amala da yan'uwansa ko wasu, tana dogewa wajan ganin ta raba shi da yan'uwansa tana hana shi ziyartarsu, da sadar da zumunta zuwa garesu, idan yan uwan sa suka ziyarceshi sai tayi ta fushi tana murtike fuska. Bugu da kari akwai mazajen da suke mika ragamar zumuncinsu ga matarsu sai wanda ta yarda dashi yake sadarmawa, wanda bata yarda da shi ba sai ya yanke ma sa.

19. *MANTAWA DA WASU YAN'UWA A LOKACIN WALIMA KO WATA HIDIMA:*            Hakika wani daga cikin yan'uwa yakan shirya walima ko wata hidima ya gayyaci yan'uwansa sai ya manta da wani ko wasu, sai su da ba’a gayyata ba su munana masa zato, su nuna kamar an wulakantasu an zabi wasu wadanda suka fisu, wannan  nasa ya kaurace masu da yanke zumunta a tsakaninsu.
Wadannan sune  kadan daga cikin abubuwan dake janyo kauracewa juna da kuma yanke zumunta. Ya kamata a basu kulawa ta musamman da hattara da fadawa cikinsu.

A NAN ZAMU DAKATA SAI A LOKACI NA GABA INDA ZAKUJI *ABUBUWAN DA SUKE TAIMAKAWA WAJAN SADAR DA ZUMUNTA*

DOMIN CIGABA DA SAMUN WANNAN RUBUTU KUNA IYA AIKEWA DA SAQON WHATSAPP ZUWA GA: +2349030201868 DOMIN SHIGA GROUP DIN *MU KYAUTATA NIYYA*

#ABBAN_SINAN

https://fb.me/abbansinan

LADUBBAN NEMAN ILIMI DA BADA ILIMI

*KWAMITIN HARKOKIN ADDINI DA ZAMANTAKEWA NA MASALLACIN ABU HURAIRAH TSAFE*

*LADUBBAN NEMAN ILIMI DA BADA ILIMI*

✅ *IKHLASI:*
yi don Allah, mai neman ilimi da malamin dake bada ilimi ya zama dukan su sunayi don Allah, domin neman yaddar Allah. Rasulullahi (S.A.W) yace "Duk wanda ya nemi ilimi don neman yaddar Allah, daga baya ya canza niyarsa don neman duniya, ba zaiji kanshin Al-Janna ba" *(Abu Dawuud: 3664)*

✅ *NIYYAR DAUKE JAHILCI:*
  Duk wanda zai nemi ilimi ko zai bada ilimi ya zamanto don ya dauke ma kansa jahilci da waninisa. Imam Ahmad Bin Hambali Yace "Shi ilimi babu abun dake dai-dai dashi ga daraja musamman ga wanda ya kyautata niyar sa". Dalibansa sukace kamar yaya? Yace "Wanda yayi da manufa (Niyar) ya dauke makansa jahilci ko waninsa"

✅ *NEMAN ILIMI DA MANUFAR KARE ADDINI:*
  Ya kamata ga mai bada ilimi ko dalibi ya kasance da manufar ba addini kariya ya keyi, Rasulullahi (S.A.W) yace: "Yaku wanda sukayi imani ku kasance masu taimakon addinin Allah, *Q: Suratul Saffi;14".*

✅ *AIKI DA ILIMI:* Na daga cikin ladubban ilimi ga malami da dalibi aiki da  ilimi Rasulullahi (S.A.W) yace Alqur'ani hujjane gareka ko akan ka” *(Muslim: 223)* hujjane gare ka in kayi aiki dashi kashiga Aljanna. Akan ka in bakayi aiki dashi ba ka shiga wuta.

✅ *HAKURI:*
Dole ne malami da mai neman ilimi suyi hakuri: malami yayi hakuri wajen bada ilimi, dalibi yayi hakuri wajen neman ilimi. Hakuri kan neman ilimi ya kasu gida ukku (3):

1. Hakuri da talauci da yinwa

2. Hakuri akan dagewa har sai ka samu

3. Rashin yanke kauna ga abin da kake nema

Imam Ahmad bin Hambali yace Na shekara tara (9) ina karatun *Kitabul Haid* har saida na gane shi

✅ *TAWALIU DA NISANTAR GIRMAN KAI:*
Ana son malami da dalibi su sanya tawali'u da nisantar girman kai ga abin da suke nema. Imam Mujahid yace Mai girman kai ko mai kunya baya samun ilimi.

✅ *TAFIYA DON NEMAN ILIMI:*
Wajibi ne ga malami ko dalibin ilimi da suyi tafiya don neman ilimi musamman ilimin da babu a  inda suke. Rasulullahi (S.A.W) yace Neman ilimi wajibine ga dukkan musulmi” *(Muslim)*

✅ *RASHIN KARBAR ILIMI GA DAN BIDI'AH:*
Bai halitta ga dalibi ya nemi ilimi ga dan bidi'ah, yan bidi'ah sune wadanda suke saba ma gaskiya kuma suka kirkira abubuwan da musulunci bai zo dasu ba, kamar: Yan shi'ah, Khawarij, da sauran darikun Sufaye.
Muhd Bin Sirin yace: Kada ku kuskura ku zauna da yan bidi'ah kada kuyi karatu garesu kar ku sauraresu domin Ahlis-sunnah sunyi ittifaki a kaurace masu da kuma nesa dasu”.

Allah ya bamu ilimi Mai amfani Kuma Mai albarka 🤲🤲🤲

*MASJID ABU HURAIRAH TSAFE SOCIAL MEDIA COMMITTEE*
+2348064734911
https://fb.me/masjidabuhurairahtsafe

Friday, 10 January 2020

021 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN *MU KYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_021_

RASHIN LAFIYA (CIWO)

Ciwo daga Allah ya ke babu wanda ya fi qarfin Allah ya jarrabe shi da ciwo ko wane iri ne, in muka bibiyi tarihi za mu ga bayin Allah da dama sun yi fama da rashin lafiya ba don kome ba sai dai don Allah ya daukaka darajarsu da kuma kankare ma su zunubansu. Gwargwadon imanin mutum gwargwadon yadda Allah zai jarraba shi. Manzon Allah sallal Lahu alayhi wa alihi wa sallam ya gaya mana cewa girman lada na tare da girman jarrabawar da Allah ya jarrabe ka da ita, haqiqa idan Allah ya so wasu mutane sai ya jarraba su (da wata cuta), wanda ya yarda da hukuncin Allah to yana da yarda, wanda ya yi hushi to yana da sakamakon fushinsa.
[Tirmidhi ya ruwaito]

Don haka ciwo ba abin zargi ba ne domin akwai wani sakamako wanda Allah ya ke bai wa wanda ya yi ciwo,
haka ma’aiki sallal Lahu alaihi wa alihi wa sallam ya fada mana a wani hadisi da aka samo daga Anas Allah ya qara masa yarda ya ce, “Manzon Allah sallal Lahu Alayhi wa alihi wa sallam ya ce, ‘Idan Allah ya so bawansa da alheri sai ya sa masa wata cuta (uquba) a nan duniya, amma idan Allah ya nufi bawansa da sharri sai ya qyale shi da zunubinsa har ya cika masa da shi ranar qiyama.’”
[Tirmidhi ya ruwaito]

Wannan magana ta manzon Allah sallal Lahu alaihi wa alihi wa sallam ta nuna mana ashe duk wanda ciwo ya same shi ya yi haquri ba kansa ne farau ba, manyan mutane su ma sun yi ciwo na tsawon lokaci mai tsawo, misali kamar Annabi Ayyub da Allah ya gaya mana ya yi ciwo na tsawon lokaci wanda har ya kai na shekara 18 ba ya fita saboda ciwo, wanda har ya kai ga gaba dayan dukiyarsa ta qare ‘ya’yansa duk suka mutu baki dayansu saboda tsananin ciwo, sai da ta kai gaba dayan jikinsa ba ya amfani sai zuciyarsa kawai, wasu malaman tafsirin ma cewa suka yi sai da ya kai jikinsa ya kasance yana yankewa yana faduwa qasa. Wata rana matarsa ta ce masa ya roqi Allah ya ba shi lafiya mana, sai ya ce shekarata saba’in lafiyata lau amma in kasa haquri da rashin lafiya ta shekara sha bakwai? [IBN KATHER]

ﺍﻟﻠﻪ ﺃَﻛْﺒَﺮُ
Bayin Allah ke nan shekara da shekaru suna fama da rashin lafiya amma suka yi haquri, haka aka san bayin Allah cikin haquri ko da yaushe.

Kusan idan muka bibiyi tarihi zamu ga yadda Allah Ya ke jarraba bayinsa da cututtuka ba don komai ba sai don Ya qara masu daraja da daukaka. Manzon Allah sallal Lahu alaihi wa alihi wa salam ya yi ciwo, haka shi ma babban sahabinsa Abubakar shi ma haka, haka shi ma Imam Malik ya yi rashin lafiya har ya kai ba ya zuwa masallaci sai a gidansa yake yin sallah,haka ya mutu cikin wannan rashin lafiya. Allah Ya rahamshe shi amin. Shi ma dalibinsa Imamu Shafi’i ya yi rashin lafiyar da ta kai in ya hau doki jini na zuba a duburarsa, har ya cika masa huffinsa (takalminsa). A qarshe dai ina mai cewa ciwo ko rashin lafiya daga Allah ne kuma ba abin zargi ba (ba aibu ba ne) ne domin jarrabawa ce daga Allah, kuma akwai sakamako mai yawa ga wanda ya yi haquri kuma ya miqa al’amarinsa ga Allah. Imam Ahmad shi ma ya yi ciwo mai tsanani har ta kai ga yana nishi da qyar, kuma a cikin wannan ciwon ya rasu Allah Ya rahamshe shi amin.
Ana so mara lafiya ya yi haquri da cutar da ta same shi ya miqa lamarinsa ga Allah kuma ya yi haquri, babu abu mafi tsada fiye da Allah Ya ba ka haquri, kuma Allah Ya yabi masu haquri a cikin littafinsa kuma Ya yi ma su bushara da lada mai yawa kuma Manzon Allah sallal Lahu alayhi wa alihi wa sallam ya fadi irin falalar haquri, shi mumini duk abin da ya same shi lada ne.
Manzon Allah sallal Lahu alayhi wa alihi wa sallam ya ce, “Abin sha’awa ga al’amarin mumini komai nashi lada ne. Idan abin farin ciki ya same shi ya gode wa Allah alkhairi ne a gare shi, in kuma abin baqin ciki ko damuwa ya same shi ko ciwo ne ya yi haquri alkhairi ne a gare shi.” [Muslim]
Manzon Allah sallal Lahu alaihi wa alihi wa sallam ya ce wanda Allah ya nufe shi da alkhairi sai ya sanya ma shi wata cuta. [Bukhari da Muslim]
Babu wata damuwa ko baqin ciki ko ciwo ko wani abu mai cuta da zai sami mumini face lada ne a gare shi. Har qaya idan ya taka face Allah Ya kankare masa kurakuransa. [Bukhari da Muslim]
Ibn Mas’ud ya shiga wajen Manzon Allah sallal Lahu alayhi wa alihi wa sallam ya taras da shi yana zazzabi, sai ya ce ma shi, “ Ashe kai ma kana zazzabi zazzabi mai tsanani haka?” Sai Manzon Allah sallal Lahu alaihi wa alihi wa sallam ya ce, “Haka ne abin yake, ni ciwon mutane biyu nake yi.” Sai Ibn Mas’ud ya ce, “Kana nufin kana da lada biyu ke nan?” Sai Manzon Allah sallal Lahu alaihi wa alihi wa sallam ya ce, “Na’am.” Sannan
sai ya ce, “Babu wani ciwo ko qaya da zai sami musulmi face Allah ya kankare masa munanan ayyukansa kamar yadda itaciya take kakkabe ganyayen ta. [Bukhari da Muslim]

Zamu dakata anan, idan Allah ya kaimu wani sati zamu cigaba Insha Allahu.

Wannan duka yana zuwa muku ne a cikin littafin: *HUKUNCE HUKUNCEN JANAZA A MUSULUNCI* Wallafar: _Malam Haruna Abubakar Shika._

MASU BUKATAR SHIGA GROUP DIN *MU KYAUTATA NIYYA* SAI SU TURA CIKAKKEN SUNA DA GARI ZUWA GA
+2349030201868 A WHATSAPP

Https://fb.me/abbansinan