Friday, 8 December 2017

HUDUBA MAI TAKEN HARAMCIN CAMFI

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A DAGA MASJID
ABI HURAIRAH DAKE TSAFE ZAMFARA


DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE


A wannan makon limamin Massallacin Jumu'a na
Abi Hurairah dake unguwar Area2, Tsafe Sheik
Sani Na Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #CHAMFI
Godiya ta tabbata ga ALLAH Wanda ya halicci
duniya da abunda ke cikinta, Godiya ta tabbata
ga ubangiji daya ubangijin rana da wata, Godiya
ga wanda kagemu ya bamu ikon gudanar rayuwa.
Tsira da amincin ALLAH Su tabbata ga mafi
soyuwa wajen ubangiji, Annabi Muhammad s.a.w
da iyalansa da sahabban da duk wadanda suka
biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar
sakamako muna rokon ya shiryar damu hanya
madaidai ciya ameen.
Yan uwa musulmi masu albarka a yau Khudbar
tamu zatayi magana ne game da #CHAMFI!!!
#CHAMFI wato ana nufin danganta faruwa ko
afkuwar wani abu na rayuwa ko mako bayan ta,
Ga lokachi ko zamani ko kwana ko wata ko
shekara ko dan Adam, Ko aure ko mutuwa da
sauransu!!
Bayan Manzo s.a.w yafa mana cewa "Duk wanda
ke #CHAMFI to ya tabbatar yayi shirka"
Shirkar kuwa zata iya kasancewa rakama ko
kuma babbah!!
Jingina faruwar wani abu ga aure ko shugaba
duk wani musulmi mai tauhidi yasan babban
kuskure ne.
Wasu kuma da danganta rashin lafiya da
#CHAMFI da kuma masu danganta duk wani
abunda yasame da #CHAMFI!!
Yan uwa musulmi masu albarka
Babu inda ya halatta ga musulmi yayi #CHAMFI
sai a wuri daya shine kayi #CHAMFI ga kanka
wato duk abunda yasameka a rayuwa ka dauka
cewa daga laifukan da kake aikatawa na rayuwa!
Shi #CHAMFI tsohon abu ne dake da tsohon
tarihi wato ba daga hausawa ne aka fara yin
#CHAMFI ba, Bari muji kadan daga wasu
al'ummah dake aikata #CHAMFI-
Yahudawa sun # CHAMFA Annabi Salihu (a.s)
domin yazo ya isko su cikin bata da shirka,
Yafara yi masu wa'azi ba dare ba rana, Da suka
qi yin imani sai ALLAH Ya jarabce su da musibu!
To sai suka fara yin #CHAMFI cewa Annabi
Salihu (A.S) yakawo masu!
Mushrikai na Makkah suma sun #CHAMFA
Manzo (s.a.w) domin ya isko su cikin kafurci da
bata, Yayi masu wa'azi da suka qi karba sai
ALLAH Ya jarabce su da talauci da rashi!
Suma sai suka #CHAMFA Manzo (s.a.w) cewa
kafin yazo suna cikin arziki, Amma da yazo sun
fara fadawa talauci!
Idan muka diba rayuwar mu ta Najeriya zamu ga
cewa kwatan kwacin rayuwar nan ta same mu, A
baya yan kasa na cikin wadata amma a yanzu
talauci wane hali muke ciki??
To nan yakamata yayi tauhidi yayi amfani,
Garemu.
Yan uwa musulmi masu albarka, Yakamata mu
kara sani talauci da arziki da komai da komai duk
suna hannu ubangiji, Amma sai mu dora laifi kan
shugabanin mu, Shin mu manta cewa akwai yan
Najeriya masu aikata Shirka wanda sune
kolulowar laifi ga ubangiji.
Mun manta fadar ALLAH s.w.t daya fada cewa
"DUK ABUNDA YASAME KU DAGA ALLAH DA
AYYUKAN DA AIKE AIKATAWA"
Hakama madaukakin sarki na cewa "DUK
ABUNDA YASAMU KU MAI KYAU DAGA ALLAH
MARAR KYAU KUMA DAGA ABUNDA KUKE
AIKATAWA NE"
Shi #CHAMFI inkari ne tauhidin rububiya.
Yan uwa musulmi masu albarka, Akwai abunda
jahilai keyi na #CHAMFA Watan safar wato
watan da muke ciki, Ma'ana wata na biyu a
musulunci, Jahilai sun kasance suna kauracewa
aikata ayyuka kamar aure da tafiya da sauransu!!
Sai Manzo s.a.w yace "Babu komai a watan
Safar, Wata ne kamar saura"
Akwai masu alaqanta cuta da #CHAMFI, a yanzu
turawan yamma na farfaganda ta cewa suna
cuta kamar ta sauro da sauransu, Wai sai suce
sun karar da ita, Hakika ita cuta tana samuwane
da iko da iznin ALLAH.
A cikin ayyukan turawa akwai tuka da warwara.
A cikin wannan watan akwai musulmi da suke
cewa wai ALLAH Na saukar da annoba dubu
ashirin da uku (23, 00.000) wai suna cewa ayi
nafila raka'a 4 da fatiha kafa 7 idan kagama za'a
rubuta 'Salamun ala nuhin' a rubuta a sha.
To wannan baida asali a musulunce kuma bidi'ah
ce!
Su duka al'amura da faruwa ne da ikon Allah.
Babban tabi'i imam alhambali yace "Kebance
wani lokachi dan a aiyana cuta garesa kuskure
ne"
Wani fasihin mawaki na cewa 'Muna ta dorawa
zamani laifi mun manta mune ke aikata laifin ba
zamani ba'
Yan uwa musulmi masu albarka, A kowane
lokachi mu zama masu imani domin bamu san
inda ajalin mu yake ba!
A takaice dukan wani abu da ake aikata wato
#CHAMFI shirka ne kuma bata ne!!
ALLAH Yabiya bukatun mu ya gafarta mana yayi
rahama garemu, Yabamu zaman lahiya mai
dorewa.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe Alzamfari. 07064282182

Jumu'ah 13-Safar1439 AH
Saturday 03-November-2017

HUDUBA MAI TAKEN LAYYA DA HUKUNCE HUKUNCENTA

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA


DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #LAYYA_DA_SALLAR
_IDI_DA_ABUBUWAN_BUKATA_A_WANN
AN_WATAN_DA_KYAWAWAN_HALAYE_A_
WAJEN_BIKIN_SALLAH
Godiya ta tabbata ga ALLAH Madaukakin
sarki,Muna gode masa,Muna neman taimakon
sa,Muna neman ya kare da sharrin kawunan mu
da miyagun ayyukan mu, Tsira da amincin ALLAH
Su kara tabbata ga manzo tsira, Annabin rahama
sallallalahu alaihi wassalam, Da iyalansa da
sahabban sa da dukkan wadanda suka biyo
bayan su da kyautatawa har zuwa ranar
sakamako.
Yan uwa musulmi yau Khudbar zata magana ke
wannan halin da ibadu dake gaban mu,
Yan uwa musulmi muji tsoron ALLAH Gaskiyar jin
tsoron sa, Kamar yadda umarce, Kuma mu kara
gode masa kamar yadda ya umarce mu, Sannan
abu ne mai kyau mu dage da ambaton ALLAH A
Wannan lokachin kamar ya umarce mu da cewa
"YAKU WADANDA KUKA YI IMANI KU AMBASHI
ALLAH AMBATO MAI WAYA KUYI KUMA TASBIHI
GARESHI"
Yan uwa masu albarka muyi tseararre a wannan
lokachin (Anan ana bukatar tsere) domin suna
cikin kwanakin da Allah ya kebance dan rahama
da tausayi ga bayin sa!
Yawaita ambaton ALLAH A cikin wannan lokachi
abu ne mai matukar muhimmanci, Hasalima an
ruwaito Abi Huraira R.a ya kasance yana shiga
ko ina yana yawaita yin kabbori, Har cikin
kasuwa yana shiga dan tunasar da yan kasuwa
da masu sayyayya, Yana daga murya yana cewa
'Allahu akbar Allahu akbbar, Allahu akbar wallahu
Akbar walil lahil hamdu'
>LAYYA
Daga cikin kwanakin goma akwai wata babbar
ibadah da ake aiwatar a wannan watan, Layya
nada sharudda
-Amfani da kudin halal wajen sayen dabbar
zakuyi amfani da ita,
Ita layya Sunnah ce daga sunnar annabawa,
Annabi Ibrahim A.s da kuma Annabi Muhammad
S.a.w , Inda tayo asali shine lokachin da annabi
Ibrahim yayi mafarkin ya yanka dansa wato
Annabi Isma'il A.s, Alqur"ani yabamu labarin
cewa Ya yanka dan nasa"SAI MUKA FANSHI
YARON DA ABUN YANKA MAI GIRMA (Rago)"
Layya abu ce dake kara kusanta bawa da
ubangijin sa, ALLAH Ya umarci Manzo s.a.w da
zuwa sallar idi, Da layya kamar yadda yake fada
cewa "KAYI SALLOLI KUMA KA YANKE LAYYA
KA DAN ALLAH DA KUMA TSARKAKA WAJEN
ALLAH"
Hadisi yazo daga sahabin manzo s.a.w cewa
"Mun kasance da ranar arfa da Manzo s.a.w
yace lallai yazama tillas ga kowane gida suyi
layya"
Ashe yazama wajibi ga kowane gida suyi layya,
Malamai sunce gida guda suna iya hadawa asayi
dabba dan ayi layya!
Hakama wani hadisi da yayo ya tsoratar da masu
tabi'ar matsolanci cewa "Manzo s.a.w yace 'Duk
wanda keda wadatar yin layya baiyi ba to kada
ma yaje massallachin idi' "
Sau da yawa zakaga magidan ci a ranar jajibiri
ya sawo wancan ya sawo wanchan, Dan adafa
abinci amma ya kasa yin layya, Ita wannan sallar
ba sallah bace ta dafe dafen abinci, Sallah ce
yanka layya!
Sheik Muhammad bn fodio yace: 'Idan bakayi
layya ba, Kuma ka dafa abinci ko wannan abincin
bidi'ah ce '!!
*Layya ta hau wajibi ga kowane musulmi, baligi,
Mai hankali, Mai wadata, Mazaunin gida, Amma
kananan yara sunnah ce, Yin layya koyi ne da
Manzon rahama s.a.w.
Ibn taimiyah yace 'A ibaduh na jiki babu kamar
sallah, A ibada ta kudi kuma babu kamar layya'
Layya ana yin tane daga dabbobin ni'imah wato
sune kamar haka-
~Rakumi rakuma
~Sa ko saniya
~Rago ko Tunkiya
~Bunsuru ko akuya.
Wadannan dasu ne kadai ake yin layya!
Sau da yawa zakaga wasu na sakaci wai da
sunam suna jin kunyar yanka bunsuru ko tinkiya
ko akuya, Dan basu da halin sayen Rago, Wannan
bai dace ba, Hausawa ma suna cewa dai dai kurji
dai dai ruwa!!
Yan uwa musulmi masu albarka, Sai dabbar layya
ta cika wadannan sharuddan sannan take layya,
~Rakumi ko rakuma sai sun kai shekara 5
~Sa ko saniya sai sunkai shekara 2 zuwa ta 3
~Bunsuru ko akuya sai sunkai shekara 1 zuwa
cikin ta 2
~Rago ko tunkiya sai sun kai shekara 1 !!
Duk da akwai basu dake cewa ana iya yanka mai
wata 6, Amma wannan bai inganta ba!
Dole ne dabba ta tsarkaka daga aibi, Wato wasu
kuma sharudda kamar haka,
~Ba'a layya da mai ido daya
~Rashin lafiyar da data baiyana
~Dabba mai gurgunta
~Tsohuwar dabba marar mai marar bargo
~Mai yankakke kunne, Ko bindi ko marar hauru
da sauran illoli baiya nan nu, DUK BA'A LAYYA
DA SU!!!
Ana son dabba wadda idan ka kalle ta zakaji
wadata.
Idan ka sawo dabba sai daya daga cikin matsalar
chan ta same ta, Malamai sunce ba ba komai
abunda dai ba'a so shine kaje saye kaganta da
wannan illar kuma ka sawo.
Hikmar dake cikin layya:
1-Kusanta bawa da ALLAH Domin ciki umarni ne
Na ubangiji kamar yadda madaukakin sarki ke
cewa "ALLAH BAYA BUKATAR NAMA KO JINI
YANA BUKATAR TSARKAKE NIYA"
2-Dan samarwa mabukata, Wato rabawa
wadanda basu yi ba, Saboda rashin hali
3-Kara soyyyaya tsakanin musulmi, Duk wanda
ya dauki nama ka bashi zaiji farin ciki da kara
sonka
4-Alamace ta daga addinin Allah, Domin yin layya
daga addini ne,
5-Koyi ce da jagorori wato annabi Ibrahim A.s da
Annabi Isma'il A.s, Mu diba fa annabi Ibrahim a.s
ce masa akayi yayi layya da dansa,Kuma ya
dauki azamar yi,
6-Yin layya ko ne da alhazai, Su suna yin hadaya,
mu kuma dake gida muna yin layya.
SALLAR IDI
Sai kuma bangare na biyu, Manzo s.a.w ya
wajabta mana sallar idi, akwai hadisi daga
manzo s.a.w da yake cewa "Manzo s.a.w yazo
garin yasrib (Madina) ya iske suna yi wassani
biyu a shekara, Sai manzo s.a.w yace ku aje
wadannan ga wasu nan wato ranakun sallah"
Manzo s.a.w yayi umarni a fita a ranar sallah
zuwa idi, Har wata mata tambaye sa to ni ina
son fita amma banda hijabi sai yace kije ki aro.
harda mata masu haila suna iya fita,
IDAN RANAR JUMU'A TA HADU DA RANAR EID
Manzo s.aw. idan ranar JUMU'AT Ta hadu da
ranar Eid to kana da zabi, Ba sai kayi jumu'a ba,
Amma Abu hurairah yace mu muna yi dan samun
lada mai yawa, Anyi haka dan falala garemu,
Saboda hidimar sallah wani na'iya mantawa da
sallar jumu'ar mah,
MIYAGUN DABI'U RANAR SALLAH
Ranar sallah rana ce ta farin ciki da murna,
Wadda musulunci ya ware muna a shekaru sai
biyu wato sallar azumi wato karamar sallar sai
kuma sallar layya ko kuma babbar sallah,
A lokachin sallah ana ado sosai kuma ana
ziyartar yan uwa da abokan arziki, Ko kiran waya
da dai sauran hanyoyin sada zumunta, Sai da
kash!
Ana samun masu amfani da wannan damar suna
wuce wuri har suna afkawa cikin haramun, Kusan
yazama al'adar wasu iyaye ta kyale yayan su
suyi abunda suka ga dama a ranar sallah ba tare
da taka masu burki ba,
A ranar sallah zakaga matasa musamman yan
mata sun chaba ado sun fito, Kirjin su a waje,
Bayan su a zahiri, Duk suna murnar sallah!
Wasu kuma a ranar suke fara iya shaye shaye
musamman samari, Wasu ma matasan a ranar
suke iya zina, Anan arewa cin Najeriya musan
yadda yayan mu suka tarbiyan tu da rufe jikin su
ta hanyar hijabi, Amma abun takaici zakaga wasu
ko gyale ma basu sawa,
Suwa keda laifi??
Manyan manyan masu laifi sune iyaye, Idan aka
ce iyaye ana nufin iyaye maza da iyaye mata,
Laifin uba anan shine shine ke sawo kayan to
dole kai zaka saka ido kan yadda za'a dunka
kayan dama yadda za'a sanya su, Zakaga uba
yasawo kaya kawai ya baiwa yayan, Haka bai
dace ba sam!
Ita kuma uwa ita ce ake kai dinkin agabanta,
Wajen sanya kayan ma agabanta, Amma bata iya
tsawatarwa akan abunda ke yi na kuskure, Iyaye
ku tuna Manzo Allah s.a.w yace mana "Dukkan
ku masu kiwo ne kuma za'a tambaye ku game da
abunda aka baku kiwo"
Masu laifi na biyu sune shuwagabani, Dole ne
shugabanin ku dauki matakan gyara tarbiyar
al"ummar su ta hanyar sanya idanu aka harkokin
su, mai makon haka sun bar al'umma kara zube
Na ukku sune malamai, Malamai sune suka san
hukuncin addini, Kuma sune masu wayar da kai
ta hanyar nasihohi da khudbobi da sauransu, Dole
ne malamai su zage damtse ka'in da na'in wajen
tabbatar da tarbiyar al'umma dan samun manya
gobe na kirki,
Manzo s.a.w yana cewa '"Mata ku zauna cikin
gida jen ku kada hali inyi na jahiliyah (fita
barkata)"
Sannan manzo s.a.w yakawo hadisi mai
tsoratarwa da yake cewa "Mata 2 yan wuta ne,
Ni ban gansu ba, Idan kun gansu ku tsine masu,
Sune masu sanya tufa amma basu sanya ba, Na
biyu sune masu fitar da gashi waje basu shiga
aljannah ko kan shinta bazasu ji ba, Duk da
akwai nisa daga kaza zuwa kaza"
Abun takaici wasu yan mata har dakunan samari
suke shiga da sunan yawon sallah,
Wasu kuma baso da murnar sallah basu yin
sallah suna ji ana kira amma basu zuwa, Dukka
dai muna fatar za'a gyara.
ALLAH Madaukakin sarki ya gafarta mana ya
rahama, Ya biya mana bukatun mu, Yayi rahama
ga mamatan mu.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe Alzamfari. 07064282182

Jumu'a 3-Zhul-Hijjah 1438 AH
Friday 25-August-2017

HUDUBAH MAI TAKEN RAMADANA DA ABUNDA YA KUNSA

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA


DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #FALALAR WATAN
RAMADAN DA ABUNDA YA KUNSA
Godiya ta tabbata ga ALLAH Wanda ya sanyawa
bayin sa alamomi da zasu zama alama garesu da
yin bauta a lokachin,
Tsira da aminci su tabbata ga wanda ALLAH Ya
aiko da gaskiya da iyalansa da sahabbansa da
dukkan wadanda suka biyo bayansa da
kyautatawa sallallahu alaihi wassalam,
Yan uwa musulmi muna fuskantar wani yanayi
mai matukar alfanu, Wanda yana kyau muci ribar
wadannan kwanuka mu yawaita taimakon kanmu,
Mu yiwa kawunan mu hisabi, Yakamata muyi
amfani da wannan dama wajen neman gafara da
yafiya daga ubangiji ALLAH,
Watan ramadana wata ne mai alfarma wanda
ALLAH Yasanya shi daga cikin rukunan
musulunci, Ramadana wata ne na tausayi da
rahama da taimakon juna.
A cikin watan ramadan akwai wata rana wadda
tafi dare dubu,
Yan uwa musulmi mu karrama wannan watan da
abubuwa guda biyu (2), Na daya ALLAH Ya ara
mana rayuwa ta kawuwa wannan watan, Sai
kuma zuwan watan na ramadan mai albarka,
Yan uwa musulmi akwai abubuwan da yakamata
mu aikata a cikin wannan watan mai kamawa,
Daga cikin su akwai;
-Mu roki ALLAH Ya yarda damu, Ya karbi dukkan
ibadun da mukayi, Duk wanda aka karbi ibadun
su a cikin watan ramadan to yayi murna yayi
farin ciki,
Lallai kololowar murna ita ce kayi murna da
zuwansa, Da kuma ni'imar halartar sa, Akwai
wanda yafara jin kanshin sa Amma ALLAH Bai
nuna masa ba, Baya daga cikin addini yin murna
walau ta samun matsayi ko dukiya kamar yadda
aya take cewa "GASUNAN SUNA FARIN CIKIN
DAN SAMUN DUNIYA ALHALI BA KOMAI BACE
IDAN KA KWATANTA DA LAHIRA"
-Kiyaye salloli na farilla a cikin lokachi, Idan har
baka sallah cikin jam'i to yakamata kayi amfani
da watan ramadan dan koya da yin sallah cikin
jam'i
-Kaucewa yin sabo, Kaucewa aikata sabo kowane
irin, Ba kauracewa ci da sha ne kurum azumi ba,
A'a harda kiyaye gabobi baki daya daga aikata
zunubai,
-Mai hankali baligi ya sanya a ransa zaiyi azumi
dan ALLAH, Dan kwadayin lada, Da kuma
kaucewa fadawa azabar ALLAH.
Muddin aka samu mutun kawai zai yi azumi dan
yazama dole, Dan kada ace wane baiyi to akwai
matsala, Yakamata a gyara dan samun ladar da
ake nema.
Azumin watan ramadan yana farawa ne da zarar
wata sha'aban yakai ashirin da tara idan ba'a ga
wata ba kuma yakai talatin, kamar yadda hadisi
daga manzo rahama na cewa "KUYI AZUMI IDAN
KUNGA WATA KU AJE IDAN KUNGA WATA"
Idan har mai alfarma sarkin Musulmi yabada
umarnin daukar azumi, To kada ayi wata wata
wajen dauka,
Idan aka bada umarni to akwai abubuwan da
yakamata ayi kamar;
-Kulla niyyah a zuciya, Ba ambatawa da baki ba,
-Sallar tarawihi, Ko a daren yau za'a iya fara
tarawihi dama ana bukatar a tari wannan watan
da aiyuka na alheri dan su zame ma jiki, Idan
watan yazo zaka iya,
>Yan uwa musulmi abunda ake cewa azumi shine
barin chi da sha da kame gabobi, ALLAH
Madaukakin sarki na cewa "KUCI KUSHA HAR
SAI BAKIN ZARE YA FITO DAGA ALFIJIR"
=Hakama yakamata ladanai kuji tsoron ALLAH
kada ladanai su kuskura su kira sallah kafin
lokachi yayi ko bayan lokachi, A yanzu muna
cikin yanayi na damina wanda gari ke laulayewa,
Jiya anan Tsafe anyi ruwa, Wasu ladanai sunyi
kiran sallah tun karfe 6:30pm, Maimakon
6:55pm.
Anan fa mutane uku ne keda laifi na daya Ladani
shi da ya kira sallah kafin lokachi yayi,
Sai kuma limani wanda shine jagora yaje yabada
sallah,
Sai kuma mamu wanda yakamata ku lura da
jadawali, Kafin sallah!
Anan jahar, Gwamnati tana raba jadawali a duk
wani massallaci komai yadda yake cikin lungu,
Kada kuma sai ladani yaci yakoshi har lokachi ya
wuce sannan yace zai kira sallah,
Idan ladani ya kira sallah lokachi baiyi ba, To
Ladani ne keda alhaki na karewar azumin su,
Alfijir na fitowa ne 04:55/6, Magrib 06:55, duk
yanayi n chanzawa, A kula sosai idan ladanai
sunyi kuskure mafita kurum a dinga diba
jadawalin da gwamnati ke kawo, Kowane lokachi
basai radaman ba.
-Tarawihi babbar sunnah ce dake nuna alamar
tsayawar ramadan, Ana samun falala a ciki.
Limamai aji tsoron ALLAH
Limamai aji tsoron ALLAH
Limamai aji tsoron ALLAH
Sau da yawa zakaga limamai na wulakanta
sallah, Ta hanyar yin qoton kurciya da yin ta
yadda aka ga dama,
Manzo rahama na cewa "KUYI SALLAH KAMAR
YADDA KUKAGA INAYI"
To sai ayita gwargwadon hali,
Wani mutun yazo yana sallah yagama yazo
wajen manzo ALLAH Sai manzo s.a.w yace ka
koma kayi sallah dan bakayi sallah ba, Sai da
akayi sau 3, Daga nan manzo s.a.w ya gwada
masa yadda zaiyi da kyau ta hanyar jeranta
kira'a da yi anatse da cikin ruku'u da sujjada,
=Yana da kyau a rage sautin amsa kuwa (Loud
speaker), Domin kada karatu na chan dana chan
su hade sai kaji duk abu ya rikice.
Wata rana Manzo s.a.w ya shigo massallaci ya
tarar kowa na sallar sa anan yahada su kan
limami daya wato Ubaiy bn Ka'af R.A
Hakama wajen yin tahujjud akiyaye.
Yan uwa musulmi manzo s.a.w ya kai karshe
komai game da ganin wata, Idan an samu rikici
to ko kaine ko wani ne ya rikice, Manzo rahama
s.a.w na cewa "IDAN KUKA DAUKA BA'A GANI
BA KU CIKA TALATIN"
Idan sarki musulmi ya bada sanarwar angani ka
sallama kawai ka dauka,
Kasar Saudiyya Yau watan su talatin yake amma
mu 29, Idan mungani zamu dauka anan Najeriya,
Yan uwa musulmi a cikin watan ramadana ana
bukatar taimakon juna, A taimakawa talakawa da
abinci koda koko da kosai ne, Domin wani ko
abincin buda baki baida shi, "Manzo s.a.w ya
kasance idan watan ramadan yazo yakan yawaita
alheri kai kace iska ne ya taso".
Ka taimaki yan uwa musulmi anan za'a gane
kana taimako.
Kuma taimako bawai sai masu kudi ba kowa
yasan wanda yafi sai ka taimaka masa, ALLAH
Madaukakin sarki na cewa "KU TAIMAKA A KASA
NI DAKE SAMA ZAN TAIMAKA MAKU"
Muna rokon ALLAH Sunayen kyawawa, Tsarkaka
ya biya mana bukatun mu, Yayi mana gafara da
rahama, Ya karbi ibadun mu wadanda mukayi da
wadanda zamuyi,
Ya ALLAH Yabaiwa shugaban kasa da Mai
martab emir na Tsafe lafiya, Yayi jagora ga
shuwagabanni mu, Ya shiryamu hanya madaidai
ciya.
ALHAMDULILLAH

©®IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA
29/Sha'aban/1438
26/05/2017.

HUDUBAH MAI TAKEN SABUBBAN DAKE SA A SHIGA ALJANNA

HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan SABUBBAN DAKE
KAIWA ZUWA GA ALJANNAH DA KUMA CIKAWA
MAI KYAU DA KUMA MASU KAIWA ZUWA WUTA
DA CIKAWAR MARAR KYAU
Godiya ta tabbata ga ALLAH Muna gode masa
muna neman taimakon sa, Mune neman yakare
daga sharrin kawu nan mu,
Duk wanda ALLAH Ya shiryar babu mai batar
dashi, Duk wanda ALLAH Yabatar babu mai iya
shiryar dashi,
Tsira da amincin ALLAH Su kara tabbata ga
mafifin halittun manzo tsira, Da iyalan da
sahabban sa, Da dukan wadanda suka biyo
bayansu da kyautatawa.
Yan uwa musulmi muyi gaggawar tuba zuwa ga
ALLAH Dan neman yagafarta mana daga laifukan
da muke aikatawa,
Ibadar da muke aikata duka bata kara ALLAH Da
komai, Hakama Fandare mai bai ragesa da
komai, Kamar yadda yake fada cikin hadisul kudsi
cewa ''YAKU BAYINA IDAN ZAKU KURE WAJEN
BAUTA MANI BAZAKU KARANI DA KOMAI BA
KUMA IDAN KUKA KAFURCE MANI BAZAKU
RAGE NI DA KOMAI BA''
YAN UWA MUSULMI Hakika aikata ayyukan alheri
suke kai mutun ga samun aljannah, Kolololuwar
sune ayyukan zukata,
Sannan aiyukan jiki sune ke taimaka ma zuciya
hadisin sahihi ya tabbata cewa ''DUKAN AYYUKA
TARE DA NIYA SUKE TAFIYA''
Aiyukan marar sa kyau kama daga Cuta, zalunci,
Yaudara munafucci E.t.c suke haddasa halin da
muke ciki kamar yadda ayar Qur'ani take cewa
''BANNA TA BAIYANA A SARARI DA KUMA CIKIN
TEKU SABODA AYYUKAN DA HANNAYE KE
AIKATAWA''
Ya yan uwa musulmi yin bauta dan ALLAH Dayin
wasiyya ta kwarai na jagoranta zuwa ga aljannah
hadisin ingantacce na cewa ''ANA CIKA AYYUKA
DA AIKI NA KWARAI DA KUMA CIKI MUNANA
MUMMUNAN KARSHE''
Yan uwa musulmi muyi dukan mai yiwuwa wajen
ganin mun cika da kyawawan ayyukan da samun
tsira gobe kiyama, ALLAH Yana gargadar mu
cewa a suratu ali imran cewa '' KUJI TSORON
ALLAH KADA KU MUTU FACE KUNA MUSULMI''
Kunga kenan wajibi mu nemi yin ayyukan kirki,
Da neman yafiya dan haduwa dashi da imani!
Yaku yan uwa musulmi shagaltuwa da ayyuka na
alheri sa samun cikawa ta kwarai, Hakama
Annabawa kamar su Ibrahim A.S Da Yunus A.S
Sunyi wasiya ga ''Kada ku bautawa kowa in
banda ALLAH'' Kunga wasiya ce mai kyau,
Ababen dake sanya Cikawa mai kyau nada yawa
ga wasu daga ciki
1-KYAKYAWAR NIYA Niya mai kyau wajen aikata
aiyuka.
2-IHLASI wato yi dan ALLAH Kai tsaye
3-KULA DA TSARE LOKACHIN SALLOLI CIKIN
JAM'I wato yin sallah a lokacinta kuma cikin
mutane.
4-GYARA Jawo al'umma zuwa ga hanyar gyara
da zata taimaka masu wajen kara kusanci da
ALLAH Kamar yadda ayar Qur'ani ke cewa ''DUK
WANDA YAYI AIKI NA KWARAI BAI DA TSORON
LOKACHIN MUTUWA''
5-TSORON ALLAH FILI DA BOYE
6-LIZIMTAR SUNNAH DA KOYI DA MAGABATA
NA KIRKI
7-KYAUTAMA AL'UMMA Yi masu fara'a, Da
yawan yi masu kyauta, Da Sadaqah da kuma
yawan yi masu sallama, Duk yana cikin
kyautawa. ALLAH Yana cewa ''WADANNAN
MASU TAIMAKO A FILI DA BOYE TO BABU
TSORON RANAR MUTUWAR SU''
8-KAMEWA CUTAR DA AL'UMMA
9-YIN ADDU'A Kamar yadda ALLAH Ke cewa ''KU
ROKE NI ZAN KARBA MAKU WADANNAN MASU
GIRMAN KAI DA ROKON ALLAH ZASU SHIGA
JAHANNAMA''
10-ADDU'A GA JAMA'A Wato yin jam'in addu'a
ga kamar cewa ALLAH Ka yafe mana, kayi mana
rahama ka gafarta mana, Hadisi ya tabbata cewa
''AKWAI MALA'IKA WANDA DUK KAYI ROKO SAI
YACE KAIMA HAKA'' kunga kenan idan muka roki
ALLAH Da roko mai kyau ko marar kyau duka
zata iya dawowa garemu.
Yaku yan uwa musulmi muyi hattara tare da
kiyaye aikata miyagun aiyuka, Da zarar ka mutu
babu imani to haqira kayi babbar hasara,
Suna da matukar yawa amma ga wasu daga
cikin su.
1-MUNAFURCI Wanda yanzu yazama ruwan dare,
A tsakanin al'umma wanda yake kaiwa ga
mummunar makoma
2-TOZARTAR DA SALLAR FARILLA Tozarta salla
ta farilla yana kaiwa zuwa ga zuwa wuta.
3-JAHILCI Wato rashin karatun addini, Da kin
gaskiya.
4-RASHIN SALLAR JUMU'A Tabbas rashin sallar
jumu'a yana kaiwa kai tsaye zuwa ga wuta.
5-RASHIN JAM'I Sai kaga kawai mutun yaki zuwa
massallaci, Yayi zaune yana sallah a gida.
6-SATA
7-CHIN MUTUNCI
8-KARYA wadda yanzu ta zama kamar ado a
tsakanin mutane musamman matasa.
9-KARKATUWA ZUWA GA DUNIYA DA KIN
LAHIRA.
10-GABATAR DA SON DUNIYA BISA GA TA
LAHIRA.
11-CUTAR ZUCIYA cutar zuciya tana da fadi da
kuma yawa ga misalan ta kamar haka
-GIRMAN KAI Wanda hausawa ke cewa rawanin
tsiya ''DUK MAI GIRMAN KAI DAI DAI DA
KWAYAR ZAIRA BAYA SHIGA ALJANNAH''
-HASSADA Wadda itama kanta yanzu ta zama
ruwan dare, Da zarar wani yaga kafara samun
wani abun hannu to shikenan kyashi da hassada,
Zasu fara biyo baya.
-JI DA KAI
-YAUDARA
-MAKIRCI
-ALGUSSU
-KIN ABUNDA ALLAH KESO
-SON ABUNDA ALLAH BAYASO
Ranar kiyama Kudi da yaya basu da tasiri kamar
yadda Qur'ani ke cewa.
12-SABAMA IYAYE A wannan lokachin
musamman matasa, Suna sabawa iyayen su
wanda iyaye sune suka rene su, Suka bada
kudaden su wajen samar wa yayan su da ilmi,
Amma da zarar sun girma sai su fara wulakanta
su, Har wata rana zakaji iyaye na bidar yayan
alhali suna cikin garin, Matasa yakamata muji
tsoron Hadisi daga manzo tsira na cewa
''ALJANNAR MU NA KARKASHIN KAFAFUN
MAHAIFAN MU''
13-YANKE ZUMUNTA A wannan zamanin yanke
zumunta yana da matuqar yawa a tsakanin
al'umma, Zakaga wa da qane uwa daya uba
daya, Ko kuma uba daya ko uwa daya, Ko kuma
wata dangantaka ta jini suna gaba da juna babu
magana a tsakani, Wanda haka na jagoranta
zuwa ga mummunar makoma, Da kuma zuwa
Jahannama, ALLAH Ya karemu ALLAH
Madaukakin sarki na cewa A cikin aya mai
matukar ban tsoro ''KUJI TSORON YININ DA ZA'A
MAIDA KU WAJEN ALLAH ZA'A CIKAWA WA
KOWA DA ABUNDA YA AIKATA BAZA'A ZALUNCI
KOWA BA''
Daga karshe muna rokon ALLAH Ya gafartamana,
Ya yafe mana, Yayi mana rahama, Ya ALLAH
Muna tuwasulli da wannan aiki daya biya mana
bukatun mu, Ya gafarta ma mamatan mu, Ya
rage mana zafin nan na sama da kasa dana
Aljihu, Ya ALLAH Ka yiwa jagororin linzami ka
daukaka musulunci da musulmai, Ka kara
kasqanta kafurci da kafurai, Ya ALLAH Ka kawo
ma musulman kasar Somalia mafita akan bala'in
yunwar dake damuwar su.
ALHAMDULILLAH

©®IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA
25/Jimada Akhair/1438
24/03/2017.

HUDUBAH MAI TAKEN WATAN SHA'ABAN

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #WATAN SHA'ABAN
Godiya ta tabbata ga ALLAH madaukakin sarki,
Muna gode masa, Muna neman taimakon sa,
Muna kara gode masa da baiwar bamu Haske
(Qur'ani) daga garesa,
Na shaida annabi Muhammadu bawan ALLAH Ne
kuma manzo sane, Da iyalan sa da sahabbansa
da dukan wadanda suka biyo bayansu da
kyautatawa,
Yan uwa musulmi yau Khudbar mu zatayi
magana ne akan Watan sha'aban falalar sa da
kuma ayyukan da'ake bukata a aikata, Da kuma
wadanda yakamata a kaura cewa,
Watan sha'aban daya ne daga cikin watanin
musulunci, Kuma wata ne mai daraja, Wata ne
wanda ALLAH Yahada ya kasance kusa da watan
Ramadana mai alfarma!
Manzo tsira S.A.W Yana cewa ''LALLAI ALLAH
MADAUKAKIN SARKI YANA ZUBA WATA BAIWA
WATA NI'IMA A KOWANE WATA DAN HAKA MU
TASHI MU NEMETA A WATAN''
Yaku yan uwa musulmi Wannan hadisin mai
daraja yana koyar damu abubuwa guda biyu
kamar haka
1-Muyi kokari mu dinga rokon ALLAH Da dagewa
wajen bauta masa, Domin dacewa da lokachin da
ALLAH Ke raba wannan ni'imar,
Manzo S.A.W Yana yawaita azumin nafila a cikin
wannan wata mai daraja na Sha'aban! Har ma
Aisha R.A Tana cewa ''"KAI KACE YANA
AZUMTAR WANNAN WATAN NE BAKI DAYA
"" (Saboda yadda yakasance yana azumtar
wannan watan)!
Yan uwa musulmi yawaita azumtar wannan
watan zai sa dan Adam yaji sauki wajen yin
azumin farilla (Ramadana)!
2-Kowane bawa ya lizimci rokon ALLAH Kowane
lokachi, Dan dacewa da wannan lokachin, Dan
samun ingantuwar rayuwa mai albarka, Muna
Ya ALLAH Ya amintar damu tare da ruhin mu, Ya
kuma yarda damu Ameen!
A wani hadisi wanda Usama ya ruwaito yana
nuna mana muhimmancin dake tattare da azumi
a cikin wannan watan na sha'aban! Hadisin na
cewa "USAMA YANA CEWA YA MANZO ALLAH
S.A.W NAGA KANA YAWAITA AZUMI A WANNAN
WATAN (SHA'ABAN) SAI MANZO S.A.W YACE
EH NAGA MUTANE NA QIN AYYUKA A CIKIN
WATAN GASHI KUMA ANA DAGA AYYUKAN BAYI
A WATAN DAN HAKA NIKEYI DAN A DAGA
AYYUKANA AKWAI AZUMI A CIKI"
Yan uwa musulmi muyi kokari mu gyara zukatan
mu, Mu gyara ayyukan mu, Mu gyara taraiyar mu
ta yau da kullun!
Yaku yan uwa musulmi akwai wasu abubuwa
dake bijirowa a cikin addinin marar sa asali,
Wadanda shedar ke kawo mana, Daga cikin
akwai, Yana sanya mutane azumi a watan daya
gabata (Rajab), Wanda babu wani nassi
ingantacce dake magana akan haka,
Yan uwa musulmi wannan watan sunansa
Sha'aban larabawa sun kasance suna yawaita
ayyuka a ciki kama daga noma, Fatauci da kuma
komawa cikin yaqi, Saboda basu yaki a cikin
watan daya gabata!
Koda addinin musulunci yazo sai ya maida watan
sha'aban watan aiki, Amma na azumi,
Magabata na kiran wannan watan da suna watan
Qira'a, Ko kuma watan karatu, Saboda tanadi da
shiryawa zuwa watan Ramadan
Idan kai mai Qira'a ne ko tafsis yakamata kaci
gaba da yin gwaji karatun ka dan zuwan
Ramadana,
Yan uwa musulmi mu gyara bitar mu, Da tafsir
idan kai mai tafsir ne!
Ya ALLAH Ya gwada mana zuwan sa lafiya,
Watan sha'aban wata ne mai daraja kamar
manzo s.a.w yake cewa "WATAN SHA'ABAN
IDAN YAYI ALLAH NA GAFATARWA MUTANE
DUKA IN BANDA MAI GABA DA MAI SHIRKA"
Yan uwa musulmi kunji fa illar take tattare da
Shirka da kuma gaba, Dam haka duk mai shirka
ko gaba yakamata yayi gaugwar tuba,
Kada mu bari wannan garaba sar mai tarin yawa,
Mu gyara ayyukan mu ta hanyar bin abunda
musulunci yazo daci sau da qafa, Mu kiyaye
bidi'a kada muyi wa shedan biyyaya,
Akwai wasu karyayyaki da wai akwai wasu
sallalo da zikirai, Da wai akeyi a cikin wannan ,
Wanda wannan baida asali a musulunci!
Hanyoyi qalilan da aka amince a aikata a wannan
watan sune
-Tsayuwa a tauhidi
-Azumin nafila
-Yawaita rokon ALLAH
Yaku yan uwa musulmi mu fadawa iyalan mu, Da
yayan mu su sani cewa su ranka dukan azumi na
ramadana wanda ake bin su,
Dukkan wadanda keda matsala kama daga
matafiya, Mai jego, Mai haila da kuma marar sa
lafiya, Dasu ranka wadannan azumin da ake biyar
su, Domin akwai hadari ALLAH Yasamu bawa ana
binsa bashin azumi ga kuma wani ya taho,
Yaku yan uwa musulmi mu kiyaye daukar azumi
kafin kowa yadauka, Domin akwai masu daukar
azumi kafin kwana daya ko biyu, Wai da gudun
idan an samu matsalar lissafi bata shafe su ba,
To yakamata su sani cewa manzo s.a.w yana
cewa "DUK WANDA YAYI AZUMI YANA SHAKKA
YA SA6AMA BABBAN QASEEM S.A.W" Kunga
dole ne a dauka tare kuma a aje tare,
Hakama wani hadisin na cewa "AZUMIN DA
ALLAH KE KARBA SHINE WANDA AKA DAUKA
TARE KUMA AKA AJE TARE"
Musulmi kada muyi rigima, Ko bijerewa umarnin
shuwagabanin mu, Koda an samu karin bai wuce
kwana daya, Kuma akwai hadisin dake bayani kan
haka manzo s.a.w yana cewa "IDAN KUNGA
WATA KU DAUKI AZUMI IDAN KUKA DIBA BAKU
GANSA BA TO ANRUFE MAKU SHI TO KU CIKA
TALATIN"
Kungani yan uwa musulmi akwai umarni daga
manzo s.a.w! dan haka muyi biyayya ga
shuwagabanin mu dan tsira gobe kiyama,
Ya ALLAH Kabamu lafiya da zama lafiya, Kayiwa
shuwagabanin mu jagoranci, Kayi mana maganin
zafi na sama da kasa dan aljihu, Ka biya mana
bukatun mu.
ALHAMDULILLAH

©®IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA
08/Sha'aban/1438
05/05/2017.

HUDUBA MAI TAKEN WATAN RAJAB

HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan WATAN RAJAB DA
HUKUNCIN SA.
Godiya ta tabbata ga ALLAH Madaukakin sarki,
Muna gode masa, Muna neman taimakon sa,
Muna neman ya kare daga sharrin kwunan mu,
Duk wanda ALLAH Ya shirya babu mai iya batar
dashi, Wanda kuma ALLAH Ya batar haqiqa babu
mai iya batar shi,
Na shaida ALLAH Shi kadai yake baida abokin
taraiya, Na shaida Annabi Muhammadu bawan
ALLAH Ne, Kuma manzon sa ne, Tsira da
amincin ALLAH Su kara tabbata gareshi da
alayen sa, Da sahabbansa da dukan wadanda
suka biyo bayan su da kyautatawa,
Yaku yan uwa musulmi muji tsoron ALLAH Kuma
mu sakankance cewa ALLAH Fa yana ganin mu a
duk abunda muke aikatawa,
ALLAH Madaukakin sarki ya zabi mala'iku a
matsayin yan aike, Hakama yafifita wasu
mutane, akan haka ya zabi wasu daga cikin
mutane a matsayin mazanni da Annabawa,
Hakama yana fifita gari kamar Makkah da
kowane gari, Hakama ya fifita wasu watanni
daga cikin sha biyu da muke dasu, Wadannan
watanni guda hudu ne sune-
Zhul hijja,
Rajab
Muharam,
Ramadan,
Wadannan watannin ALLAH Ya fifita su dan ana
ninki lada a ciki hakama ana ninka zunubi a ciki,
Ana bukatar kowane musulmi ya girmama
wadannan watanni,
Wadannan watanin ALLAH Ya karramasu kamar
yadda yake fada a cikin suratul taubah cewa
''LALLAI ADADIN WATANNIN SHA BIYU NE A
WURIN ALLAH KUMA AKWAI MAFIYA HUDU
DAGA CIKIN SU KADA SU ZALUNCI KAWUNAN
KU A CIKI''
Hakama manzon rahama yana cewa ''LALLAI
ZAMANI YANA YIN BAGA YANA TAFIYA''
Ya chanchanci kowane musulmi ya girmama su
ya kaucewa aikata duk wani sabawa ubangiji a
cikin su,
Masu hikima na cewa ALLAH Na lunka lada ga
zunubi a lokachi mai daraja (wato wadannan
watannin)
ALLAH Madaukakin sarki yana fada cewa ''SUNA
TAMBAYAR KA AKAN YIN YAQI CIKIN WATANNI
MASU DARAJA TO KAFADA MASU CEWA FADA
KISA KO FADA A CIKIN ABU NE MAI GIRMA''
Yan uwa musulmi mun shiga wata mai daraja
wato daya daga cikin wadancan watannin,
Yawaita azumi a cikin wannan watan a kullun
haramun ne,
Ibn asqalani ya rubuta littafi daya kawo karyakkin
da ake jingina hadisai wai daga annabi
Akwai hadisai na karya wadanda ake yadawa
kuma ga wasu daga cikin su.
-Annabi bai taba yin azumin watan biyu ba ajere
sune rajab da sha'aban, Wanda shima wannan
karya ne,
-Wai sunce yace falalar rajab da sauran watanni
kamas banbancin Qur'ani ne sauran littafan
annabawa wannan shima na karya ne
-Wai sunce Yace rajab watan ALLAH Shine
sha'aban, Rajab kuwa nawane, Ramadan kuwa na
al'ummata ne duk wanda yayi sallah raka'a biyu
a cikin daren farko da kuma sallar jumu'a ta
farko a cikin dare dan aljannah ne, Wannan shima
hadisin karya ne
-Hakama sunce wai manzo ALLAH Yace babu
wani da zaiyi azumi a ranar alhamis ta farko a
rajab, Sannao ya sallaci raka'a biyu za'a rubuta
mai ladar ibada ta shekara Dubu (1000), Wannan
shima na karya ne.
Ire iren su nada matukar yawa, Hakama ana
yada irin wadannan karyayyakin a shafukan sada
zumunta, Hakama dole ne a kiyaye saboda ba
kowane keda iya tsayawa ta tantance ba,
Yaku yan uwa musulmi aduk bakin dakaji
wadannan hadisan to dauka kaji bidi'a saboda
basu da asali ko kadan a cikin musulunci,
Musulmai na girmama magana wadda ta fito
daga bakin manzo ALLAH Saboda haka ne ake
fadar karya ake yadawa dan jahilai su dauka
ibadah ne su kama yi!
Idan kuka lura duk wadannan kalaman suna da
romo mai yawa wadanda ke kaiwa zuwa fadawa
bidi'ah!
Yaku yan uwa musulmi abunda akeso a sani
shine watan rajab daya ne daga cikin watanni
masu alfarma,
Mu kiyaye yada duk wadannan karyayyakin
musamman a shafukan sada zumunta,
Idan aka turo maka wadannan kalaman na karya
to kayi amfani da hadisin nan dake cewa ''DUK
WANDA YAGA ANA AIKATA WANI ABU MARAR
KYAU TO YA HAKA DA HANNUSA KO DA
HARSHEN KO KUMA YA NUNA KYAMA DA
ZUCIYAR SA, AMMA FA WANNAN SHINE
KARAMIN MATAKI NA IMANI''
Kada mu rudu da dukan abunda mukeji a daga
wajen malamai, Sannan yazama wajibi
shuwagabannin su tashi tsaye wajen hana
wandannan bidi'oin, Yakamata suyi koyi da
sayyidina Umar bn khaddab, Inda yake bi a ko'ina
dan hana masu azumtar wannan watan!
Dole ne gwamnatoci suyi koyi da hadisin nan
dake cewa ''DUKKANIN KU MAKIYAYA NE KUMA
ZA'A TAMBAYEKU KAN ABUNDA AKA BAKU
KIWO''
Yaku yan uwa musulmi shedan fa kamar
mahauniya yake ma'ana yana rikida, Ta kowace
fuska yana kokarin yaga dan adam ya mutu bai
tuba ba, Yana bullowa wa yan adam ta hanyoyi
da dama kamar su,
-Sallah Zakaga baligi yana takirus sallat idan yayi
wata ba yayin wata, ko kuma wani bayayi gaba
daya.
-Zakkah zakaga mai kudi ya tara su kamar suyi
magana amma baya fidda haqqi ALLAH, Ko kuma
yana badawa amma yana tafka kura kurai,
-Bidi'a, Ana shedan yana samun kafa dan ya
cusawa mutane wasu aiyuka wadanda a zahiri
zakaga kamar dai dai ne, Amma kuwa bidi'ah ce
subhannallah,
Yaku yan uwa musulmi shedan fa baya kyale dan
adam har sai yaga kabar duniya,
Ya ALLAH Ya azurtamu da kaucewa aikata
dukkan abunda musulunci ya haramta,
Amma babu laifi mai yin azumin litinin da
alhamis, ko kuma azumi ukku a wata yaci gaba a
wannan watan na rajab.
Daga Karshe muna rokon ALLAH Ya gafarta
mana yayi mana rahama, Ya ALLAH Ka karemu
daga aikata bidi'oi, Ya ALLAH Ka bamu lafiya da
zama lafiya, Ya ALLAH Ka karemu daga aikata
zunubai, Muna amfani da wannan damar muyi
addu'a ga mai martaba yandoton TSAFE Akan
ALLAH Ya bashi lafiya akan neman maganin da
yajeyi a kasar India, ALLAH Yasa asamu abunda
akaje nema, Muna rokon ALLAH Ya gafartawa
mamatan mu da wadanda suka samu hadarin
mota jiya da shekaran jiya da yau.
ALHAMDULILLAH

©®IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA
2/Rajab/1438
31/03/2017.

HUDUBAH MAI TAKEN JUMA'AH DA HUKUNCE HUKUNCENTA

HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA
DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE
A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #RANAR_JUMU
'A_DA_HUKUKUNCE_HUKUNCETA
Muna godiya ga ALLAH Mai girman muna
godemasa a bisa ni'imar ta sanya mana ranar
Jumu'a a matsayin shugaban ranaku baki daya,
Sannam ya kebance mana ranar ta Jumu'a ga
al'ummar Manzo tsira a matsayio kyauta dan
muyi zikiri da ambaton ALLAH
Sallati da tsira su kasa tabbata ga mafificin
halitta Annabin mu Muhammad Sallallahu alaihi
wassalam.
YAKU YAN UWA MUSULMI Khudbar mu ta yau
tana magana ne akan Ranar JUMU'A
Yan uwa uwa musulmi ku sani ita ranar Jumu'a
rana ce ta musamman da ALLAH Ya bamu ita a
matsayin kyauta, Dan mu kara dagewa wajen
bauta masa, Saboda mune Al'umma datafi
kowace fifiko a wajen ALLAH
Hakika Hadisi ya tabbata daga Manzo tsira cewa
''MU WADANNAN AL'UMMAR MUNE NA KARSHE
KUMA MUNE NA FARKO A SHIGA AL'JANNAH''
Yahudawa Sun zabi ranar Assabar a matsayin
mafificiya, Su kuma Nasara sun zabi Lahadi A
matsayin mafifiyar rana!
Mu kuma Al'ummar Musulmi ALLAH Yazabar
mana Ranar Jumu'a a matsayin mafificiya.
Hakika ranar Jumu'a sama take ga kowace rana
daga cikin kwanaki bakwai.
Manzo tsira yana cewa a ''FIYAYYEN YINI DA
RANA KE FITOWA ITACE RANAR JUMU'A ''
YAN UWA MUSULMI Saboda girma da matsayi na
wannan ranar, A ranar ne aka halicci kakan mu
Annabi Adam (A.S),
Hakama A ranar ya shiga Aljannah, A kuma ranar
ya fita Aljannah,
YAN UWA MUSULMI Ranar Jumu'a ne za'ayi
tashin kiyama,
Idan ka cire mutun da Aljani to dukkanin halittu
suna cikin fargaba idan ranar Jumu'a tazo
saboda suna tsammanin a ranar kiyama zata
tsayu.
YAKU YAN UWA MUSULMI
Manzo tsira yana girmama wannan rana, Yana
yawaita salati ga kansa, Dan haka yazama Muma
wajibi garemu yawaita salati gareshi, Dan salati
Gareshi kamar Addu'a ce.
Daren Jumu'a nada matukar falala wato (Cikin
dare ranar Alhamis) Ana bukatar yawaita salati a
daren, Ana Bukatar kowane musulmi ya yawaita
neman lada a dare domin shirin zuwan ranar,
Kamar misali Daren Sallah ne da ake yin komai a
ranar Jajirbiri!
YAKU YAN UWA MUSULMI Akwai Wasu ayyuka
da Manzo tsira ya kasance yake aikata a cikin
dare da rana ta Jumu'a
1-Annabi na karanta surutul Sajada, Da kuma
Suratul kiyama, A cikin sallar asuba ta wannan
daren, Saboda wadannan surorin suna bayani
game da ranar kiyama,
Daren Jumu'a nada matukar falala, Kamar yadda
yazo a cikin hadisin sa ''MAFICIN SALLAH ITA
CE SAMUN SALLAR ASUBA A CIKIN JAM'I''
Yaku muminai kunji wannan falalar mai matukar
amfani wadda yakamata mukiyaye mu dinga
halarta sallar asuba cikin jam'i!
2-An so yawaita salati a ranar yana da kyau
takaita duk wata ibadah dan mukeyi a ranar dan
samun wannan garaba sar.
Domin salati kamar addu'a ce garesa,
Manzo Tsira da kansa yana fada cewa ''KUSANI
RANAR JUMU'A AKA HAIFI ADAM KUMA RANAR
ZA'A BUSA KAHO''
3-Anaso kowane musulmi yayi wanka, Yayi tsafta
yan sanya kaya mafi kyau, Ya sanya turare.
4-Aswaki
5-Zuwa massallaci da wuri
6-Inda hali kazo kasa.
Kamar yadda hadisi ya tabbata cewa ''BABU
WANI DA ZAIYI WANKA RANAR JUMU'A
SANNAN YAZO YA SALLACI SALLAR WAJIBI
FACE SAI AN GAFARTAMASA HAR ZUWA WANI
SATIN''
YAN UWA MUSULMI Ya chanchanta muzama
cikin masu zuwa da wuri saboda samun damar
zaunawa a massallaci dan yin salati, Sannan
kuma Mala'iku suna yiwa wanda ke zaune
massallaci addu'a.
To amma abun takaici wasu na kauracewa zuwa
da wuri, Zakaga wasu basu wuri sai anfara
khudbar, Wasu kuma sai anyi rabi wasu kuma sai
an gama, Wasu kuma sai Tada sallah, Kai wasu
ma sai an yi raka'a daya!
Shedan ya hana musulmi more ma wannan
romon!
Yaku yan uwa musulmi muji tsoron ALLAH .
Hadisi daga manzo tsira na cewa ''DUK WANDA
YAYI WANKA IRIN NA JANABA (Dama wankan
tsarki iri daya ne a musulmi) ZA'A BASHI LADAR
WANDA YABADA KYAUTAR RAKUMI, WANDA
YAZO NA BIYU ZA'A BASHI LADAR WANDA
YABADA SADAKAR SA, NA UKU KUMA ZAI SAMU
LADAR WANDA YABADA KATON RAGO NA HUDU
KUWA ZAI SAMU LADAR WANDA YABADA KAZA/
ZAKARA NA BIYAR KUMA ZAI SAMU LADAR
WANDA YABADA KWAI''
Wanda kuma sai da limamin yazo ba'a sanyi shi
cikin lissahi.
Akwai abubuwa guda biyar da ake saran da adam
zai dace da Aljannah a ranar jumu'a akwai,
1-Gaida marar lafiya (ranar jumu'a)
2-Zuwa jana'iza (ranar jumu'a)
3-Azuni
4-Zuwa Massallaci da wuri
5-Inta bawa ko baiwa, (Taimakawa wajen biyan
bashi)
Tafiya Kasa zuwa massallaci ranar jumu'a nada
matukar falala kamar yadda yazo a cikin hadisi
cewa ''DUK WANDA YATASO DAGA GIDA DA
KAFAFUNSA SUKAYI KURA (DAUDA) TO
KAFAFUN SUN HARAMATA SHIGA''
JUMU'A Nada sharadi kamar haka
Yin shiru a lokachin huduba, Kamar yadda ALLAH
Madaukakin sarki yake cewa ''IDAN ANA
KARANTA QUR'ANI KU SAURARA WATA QILA SU
SAMU RAHAMA'' Kunga kuma huduba ana kawo
ayoyin Qur'ani. Kai wajibi ne yin shiru idan ana
huduba!
Banda wasa, ko gaishe gaishe,
Ba hallata kayi tafiya dab da lokachin Jumu'a sai
inda ta zama wajibi, Saboda karamawa da
girmama wannan ranar!
Yana da kyau karanta suratul kahfi a ranar
Jumu'a, Saboda Annabi na cewa ''DUK WANDA
YAKARANTA SURATUL KAHFI RANAR JUMU'A
ALLAH ZAI HASKAKA MASA HAR WANI SATIN''
Muna rokon ALLAH Tare da tuwassalin da
wannan khudbar ka biya mana bukatun mu, Ya
ALLAH Ka baiwa Mai martaba Emir na Tsafe
lafiya, Kasa asamo abunda akaje nema a kasar
india, Ya ALLAH Kasanya garin mu Albarka ka
yafemana kayi jagora ga shuwagabbani mu Baki
daya, Ka jikan mamatan mu Baki dayan su.
ALHAMDULILLAH
©®IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA
18/Jimada Akhair/1438
17/03/2017.