HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA
DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE
A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan WATAN RAJAB DA
HUKUNCIN SA.
Godiya ta tabbata ga ALLAH Madaukakin sarki,
Muna gode masa, Muna neman taimakon sa,
Muna neman ya kare daga sharrin kwunan mu,
Duk wanda ALLAH Ya shirya babu mai iya batar
dashi, Wanda kuma ALLAH Ya batar haqiqa babu
mai iya batar shi,
Na shaida ALLAH Shi kadai yake baida abokin
taraiya, Na shaida Annabi Muhammadu bawan
ALLAH Ne, Kuma manzon sa ne, Tsira da
amincin ALLAH Su kara tabbata gareshi da
alayen sa, Da sahabbansa da dukan wadanda
suka biyo bayan su da kyautatawa,
Yaku yan uwa musulmi muji tsoron ALLAH Kuma
mu sakankance cewa ALLAH Fa yana ganin mu a
duk abunda muke aikatawa,
ALLAH Madaukakin sarki ya zabi mala'iku a
matsayin yan aike, Hakama yafifita wasu
mutane, akan haka ya zabi wasu daga cikin
mutane a matsayin mazanni da Annabawa,
Hakama yana fifita gari kamar Makkah da
kowane gari, Hakama ya fifita wasu watanni
daga cikin sha biyu da muke dasu, Wadannan
watanni guda hudu ne sune-
Zhul hijja,
Rajab
Muharam,
Ramadan,
Wadannan watannin ALLAH Ya fifita su dan ana
ninki lada a ciki hakama ana ninka zunubi a ciki,
Ana bukatar kowane musulmi ya girmama
wadannan watanni,
Wadannan watanin ALLAH Ya karramasu kamar
yadda yake fada a cikin suratul taubah cewa
''LALLAI ADADIN WATANNIN SHA BIYU NE A
WURIN ALLAH KUMA AKWAI MAFIYA HUDU
DAGA CIKIN SU KADA SU ZALUNCI KAWUNAN
KU A CIKI''
Hakama manzon rahama yana cewa ''LALLAI
ZAMANI YANA YIN BAGA YANA TAFIYA''
Ya chanchanci kowane musulmi ya girmama su
ya kaucewa aikata duk wani sabawa ubangiji a
cikin su,
Masu hikima na cewa ALLAH Na lunka lada ga
zunubi a lokachi mai daraja (wato wadannan
watannin)
ALLAH Madaukakin sarki yana fada cewa ''SUNA
TAMBAYAR KA AKAN YIN YAQI CIKIN WATANNI
MASU DARAJA TO KAFADA MASU CEWA FADA
KISA KO FADA A CIKIN ABU NE MAI GIRMA''
Yan uwa musulmi mun shiga wata mai daraja
wato daya daga cikin wadancan watannin,
Yawaita azumi a cikin wannan watan a kullun
haramun ne,
Ibn asqalani ya rubuta littafi daya kawo karyakkin
da ake jingina hadisai wai daga annabi
Akwai hadisai na karya wadanda ake yadawa
kuma ga wasu daga cikin su.
-Annabi bai taba yin azumin watan biyu ba ajere
sune rajab da sha'aban, Wanda shima wannan
karya ne,
-Wai sunce yace falalar rajab da sauran watanni
kamas banbancin Qur'ani ne sauran littafan
annabawa wannan shima na karya ne
-Wai sunce Yace rajab watan ALLAH Shine
sha'aban, Rajab kuwa nawane, Ramadan kuwa na
al'ummata ne duk wanda yayi sallah raka'a biyu
a cikin daren farko da kuma sallar jumu'a ta
farko a cikin dare dan aljannah ne, Wannan shima
hadisin karya ne
-Hakama sunce wai manzo ALLAH Yace babu
wani da zaiyi azumi a ranar alhamis ta farko a
rajab, Sannao ya sallaci raka'a biyu za'a rubuta
mai ladar ibada ta shekara Dubu (1000), Wannan
shima na karya ne.
Ire iren su nada matukar yawa, Hakama ana
yada irin wadannan karyayyakin a shafukan sada
zumunta, Hakama dole ne a kiyaye saboda ba
kowane keda iya tsayawa ta tantance ba,
Yaku yan uwa musulmi aduk bakin dakaji
wadannan hadisan to dauka kaji bidi'a saboda
basu da asali ko kadan a cikin musulunci,
Musulmai na girmama magana wadda ta fito
daga bakin manzo ALLAH Saboda haka ne ake
fadar karya ake yadawa dan jahilai su dauka
ibadah ne su kama yi!
Idan kuka lura duk wadannan kalaman suna da
romo mai yawa wadanda ke kaiwa zuwa fadawa
bidi'ah!
Yaku yan uwa musulmi abunda akeso a sani
shine watan rajab daya ne daga cikin watanni
masu alfarma,
Mu kiyaye yada duk wadannan karyayyakin
musamman a shafukan sada zumunta,
Idan aka turo maka wadannan kalaman na karya
to kayi amfani da hadisin nan dake cewa ''DUK
WANDA YAGA ANA AIKATA WANI ABU MARAR
KYAU TO YA HAKA DA HANNUSA KO DA
HARSHEN KO KUMA YA NUNA KYAMA DA
ZUCIYAR SA, AMMA FA WANNAN SHINE
KARAMIN MATAKI NA IMANI''
Kada mu rudu da dukan abunda mukeji a daga
wajen malamai, Sannan yazama wajibi
shuwagabannin su tashi tsaye wajen hana
wandannan bidi'oin, Yakamata suyi koyi da
sayyidina Umar bn khaddab, Inda yake bi a ko'ina
dan hana masu azumtar wannan watan!
Dole ne gwamnatoci suyi koyi da hadisin nan
dake cewa ''DUKKANIN KU MAKIYAYA NE KUMA
ZA'A TAMBAYEKU KAN ABUNDA AKA BAKU
KIWO''
Yaku yan uwa musulmi shedan fa kamar
mahauniya yake ma'ana yana rikida, Ta kowace
fuska yana kokarin yaga dan adam ya mutu bai
tuba ba, Yana bullowa wa yan adam ta hanyoyi
da dama kamar su,
-Sallah Zakaga baligi yana takirus sallat idan yayi
wata ba yayin wata, ko kuma wani bayayi gaba
daya.
-Zakkah zakaga mai kudi ya tara su kamar suyi
magana amma baya fidda haqqi ALLAH, Ko kuma
yana badawa amma yana tafka kura kurai,
-Bidi'a, Ana shedan yana samun kafa dan ya
cusawa mutane wasu aiyuka wadanda a zahiri
zakaga kamar dai dai ne, Amma kuwa bidi'ah ce
subhannallah,
Yaku yan uwa musulmi shedan fa baya kyale dan
adam har sai yaga kabar duniya,
Ya ALLAH Ya azurtamu da kaucewa aikata
dukkan abunda musulunci ya haramta,
Amma babu laifi mai yin azumin litinin da
alhamis, ko kuma azumi ukku a wata yaci gaba a
wannan watan na rajab.
Daga Karshe muna rokon ALLAH Ya gafarta
mana yayi mana rahama, Ya ALLAH Ka karemu
daga aikata bidi'oi, Ya ALLAH Ka bamu lafiya da
zama lafiya, Ya ALLAH Ka karemu daga aikata
zunubai, Muna amfani da wannan damar muyi
addu'a ga mai martaba yandoton TSAFE Akan
ALLAH Ya bashi lafiya akan neman maganin da
yajeyi a kasar India, ALLAH Yasa asamu abunda
akaje nema, Muna rokon ALLAH Ya gafartawa
mamatan mu da wadanda suka samu hadarin
mota jiya da shekaran jiya da yau.
ALHAMDULILLAH
©®IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA
2/Rajab/1438
31/03/2017.
No comments:
Post a Comment