HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA
DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE
A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan SABUBBAN DAKE
KAIWA ZUWA GA ALJANNAH DA KUMA CIKAWA
MAI KYAU DA KUMA MASU KAIWA ZUWA WUTA
DA CIKAWAR MARAR KYAU
Godiya ta tabbata ga ALLAH Muna gode masa
muna neman taimakon sa, Mune neman yakare
daga sharrin kawu nan mu,
Duk wanda ALLAH Ya shiryar babu mai batar
dashi, Duk wanda ALLAH Yabatar babu mai iya
shiryar dashi,
Tsira da amincin ALLAH Su kara tabbata ga
mafifin halittun manzo tsira, Da iyalan da
sahabban sa, Da dukan wadanda suka biyo
bayansu da kyautatawa.
Yan uwa musulmi muyi gaggawar tuba zuwa ga
ALLAH Dan neman yagafarta mana daga laifukan
da muke aikatawa,
Ibadar da muke aikata duka bata kara ALLAH Da
komai, Hakama Fandare mai bai ragesa da
komai, Kamar yadda yake fada cikin hadisul kudsi
cewa ''YAKU BAYINA IDAN ZAKU KURE WAJEN
BAUTA MANI BAZAKU KARANI DA KOMAI BA
KUMA IDAN KUKA KAFURCE MANI BAZAKU
RAGE NI DA KOMAI BA''
YAN UWA MUSULMI Hakika aikata ayyukan alheri
suke kai mutun ga samun aljannah, Kolololuwar
sune ayyukan zukata,
Sannan aiyukan jiki sune ke taimaka ma zuciya
hadisin sahihi ya tabbata cewa ''DUKAN AYYUKA
TARE DA NIYA SUKE TAFIYA''
Aiyukan marar sa kyau kama daga Cuta, zalunci,
Yaudara munafucci E.t.c suke haddasa halin da
muke ciki kamar yadda ayar Qur'ani take cewa
''BANNA TA BAIYANA A SARARI DA KUMA CIKIN
TEKU SABODA AYYUKAN DA HANNAYE KE
AIKATAWA''
Ya yan uwa musulmi yin bauta dan ALLAH Dayin
wasiyya ta kwarai na jagoranta zuwa ga aljannah
hadisin ingantacce na cewa ''ANA CIKA AYYUKA
DA AIKI NA KWARAI DA KUMA CIKI MUNANA
MUMMUNAN KARSHE''
Yan uwa musulmi muyi dukan mai yiwuwa wajen
ganin mun cika da kyawawan ayyukan da samun
tsira gobe kiyama, ALLAH Yana gargadar mu
cewa a suratu ali imran cewa '' KUJI TSORON
ALLAH KADA KU MUTU FACE KUNA MUSULMI''
Kunga kenan wajibi mu nemi yin ayyukan kirki,
Da neman yafiya dan haduwa dashi da imani!
Yaku yan uwa musulmi shagaltuwa da ayyuka na
alheri sa samun cikawa ta kwarai, Hakama
Annabawa kamar su Ibrahim A.S Da Yunus A.S
Sunyi wasiya ga ''Kada ku bautawa kowa in
banda ALLAH'' Kunga wasiya ce mai kyau,
Ababen dake sanya Cikawa mai kyau nada yawa
ga wasu daga ciki
1-KYAKYAWAR NIYA Niya mai kyau wajen aikata
aiyuka.
2-IHLASI wato yi dan ALLAH Kai tsaye
3-KULA DA TSARE LOKACHIN SALLOLI CIKIN
JAM'I wato yin sallah a lokacinta kuma cikin
mutane.
4-GYARA Jawo al'umma zuwa ga hanyar gyara
da zata taimaka masu wajen kara kusanci da
ALLAH Kamar yadda ayar Qur'ani ke cewa ''DUK
WANDA YAYI AIKI NA KWARAI BAI DA TSORON
LOKACHIN MUTUWA''
5-TSORON ALLAH FILI DA BOYE
6-LIZIMTAR SUNNAH DA KOYI DA MAGABATA
NA KIRKI
7-KYAUTAMA AL'UMMA Yi masu fara'a, Da
yawan yi masu kyauta, Da Sadaqah da kuma
yawan yi masu sallama, Duk yana cikin
kyautawa. ALLAH Yana cewa ''WADANNAN
MASU TAIMAKO A FILI DA BOYE TO BABU
TSORON RANAR MUTUWAR SU''
8-KAMEWA CUTAR DA AL'UMMA
9-YIN ADDU'A Kamar yadda ALLAH Ke cewa ''KU
ROKE NI ZAN KARBA MAKU WADANNAN MASU
GIRMAN KAI DA ROKON ALLAH ZASU SHIGA
JAHANNAMA''
10-ADDU'A GA JAMA'A Wato yin jam'in addu'a
ga kamar cewa ALLAH Ka yafe mana, kayi mana
rahama ka gafarta mana, Hadisi ya tabbata cewa
''AKWAI MALA'IKA WANDA DUK KAYI ROKO SAI
YACE KAIMA HAKA'' kunga kenan idan muka roki
ALLAH Da roko mai kyau ko marar kyau duka
zata iya dawowa garemu.
Yaku yan uwa musulmi muyi hattara tare da
kiyaye aikata miyagun aiyuka, Da zarar ka mutu
babu imani to haqira kayi babbar hasara,
Suna da matukar yawa amma ga wasu daga
cikin su.
1-MUNAFURCI Wanda yanzu yazama ruwan dare,
A tsakanin al'umma wanda yake kaiwa ga
mummunar makoma
2-TOZARTAR DA SALLAR FARILLA Tozarta salla
ta farilla yana kaiwa zuwa ga zuwa wuta.
3-JAHILCI Wato rashin karatun addini, Da kin
gaskiya.
4-RASHIN SALLAR JUMU'A Tabbas rashin sallar
jumu'a yana kaiwa kai tsaye zuwa ga wuta.
5-RASHIN JAM'I Sai kaga kawai mutun yaki zuwa
massallaci, Yayi zaune yana sallah a gida.
6-SATA
7-CHIN MUTUNCI
8-KARYA wadda yanzu ta zama kamar ado a
tsakanin mutane musamman matasa.
9-KARKATUWA ZUWA GA DUNIYA DA KIN
LAHIRA.
10-GABATAR DA SON DUNIYA BISA GA TA
LAHIRA.
11-CUTAR ZUCIYA cutar zuciya tana da fadi da
kuma yawa ga misalan ta kamar haka
-GIRMAN KAI Wanda hausawa ke cewa rawanin
tsiya ''DUK MAI GIRMAN KAI DAI DAI DA
KWAYAR ZAIRA BAYA SHIGA ALJANNAH''
-HASSADA Wadda itama kanta yanzu ta zama
ruwan dare, Da zarar wani yaga kafara samun
wani abun hannu to shikenan kyashi da hassada,
Zasu fara biyo baya.
-JI DA KAI
-YAUDARA
-MAKIRCI
-ALGUSSU
-KIN ABUNDA ALLAH KESO
-SON ABUNDA ALLAH BAYASO
Ranar kiyama Kudi da yaya basu da tasiri kamar
yadda Qur'ani ke cewa.
12-SABAMA IYAYE A wannan lokachin
musamman matasa, Suna sabawa iyayen su
wanda iyaye sune suka rene su, Suka bada
kudaden su wajen samar wa yayan su da ilmi,
Amma da zarar sun girma sai su fara wulakanta
su, Har wata rana zakaji iyaye na bidar yayan
alhali suna cikin garin, Matasa yakamata muji
tsoron Hadisi daga manzo tsira na cewa
''ALJANNAR MU NA KARKASHIN KAFAFUN
MAHAIFAN MU''
13-YANKE ZUMUNTA A wannan zamanin yanke
zumunta yana da matuqar yawa a tsakanin
al'umma, Zakaga wa da qane uwa daya uba
daya, Ko kuma uba daya ko uwa daya, Ko kuma
wata dangantaka ta jini suna gaba da juna babu
magana a tsakani, Wanda haka na jagoranta
zuwa ga mummunar makoma, Da kuma zuwa
Jahannama, ALLAH Ya karemu ALLAH
Madaukakin sarki na cewa A cikin aya mai
matukar ban tsoro ''KUJI TSORON YININ DA ZA'A
MAIDA KU WAJEN ALLAH ZA'A CIKAWA WA
KOWA DA ABUNDA YA AIKATA BAZA'A ZALUNCI
KOWA BA''
Daga karshe muna rokon ALLAH Ya gafartamana,
Ya yafe mana, Yayi mana rahama, Ya ALLAH
Muna tuwasulli da wannan aiki daya biya mana
bukatun mu, Ya gafarta ma mamatan mu, Ya
rage mana zafin nan na sama da kasa dana
Aljihu, Ya ALLAH Ka yiwa jagororin linzami ka
daukaka musulunci da musulmai, Ka kara
kasqanta kafurci da kafurai, Ya ALLAH Ka kawo
ma musulman kasar Somalia mafita akan bala'in
yunwar dake damuwar su.
ALHAMDULILLAH
©®IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA
25/Jimada Akhair/1438
24/03/2017.
No comments:
Post a Comment