HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA
DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE
A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #RANAR_JUMU
'A_DA_HUKUKUNCE_HUKUNCETA
Muna godiya ga ALLAH Mai girman muna
godemasa a bisa ni'imar ta sanya mana ranar
Jumu'a a matsayin shugaban ranaku baki daya,
Sannam ya kebance mana ranar ta Jumu'a ga
al'ummar Manzo tsira a matsayio kyauta dan
muyi zikiri da ambaton ALLAH
Sallati da tsira su kasa tabbata ga mafificin
halitta Annabin mu Muhammad Sallallahu alaihi
wassalam.
YAKU YAN UWA MUSULMI Khudbar mu ta yau
tana magana ne akan Ranar JUMU'A
Yan uwa uwa musulmi ku sani ita ranar Jumu'a
rana ce ta musamman da ALLAH Ya bamu ita a
matsayin kyauta, Dan mu kara dagewa wajen
bauta masa, Saboda mune Al'umma datafi
kowace fifiko a wajen ALLAH
Hakika Hadisi ya tabbata daga Manzo tsira cewa
''MU WADANNAN AL'UMMAR MUNE NA KARSHE
KUMA MUNE NA FARKO A SHIGA AL'JANNAH''
Yahudawa Sun zabi ranar Assabar a matsayin
mafificiya, Su kuma Nasara sun zabi Lahadi A
matsayin mafifiyar rana!
Mu kuma Al'ummar Musulmi ALLAH Yazabar
mana Ranar Jumu'a a matsayin mafificiya.
Hakika ranar Jumu'a sama take ga kowace rana
daga cikin kwanaki bakwai.
Manzo tsira yana cewa a ''FIYAYYEN YINI DA
RANA KE FITOWA ITACE RANAR JUMU'A ''
YAN UWA MUSULMI Saboda girma da matsayi na
wannan ranar, A ranar ne aka halicci kakan mu
Annabi Adam (A.S),
Hakama A ranar ya shiga Aljannah, A kuma ranar
ya fita Aljannah,
YAN UWA MUSULMI Ranar Jumu'a ne za'ayi
tashin kiyama,
Idan ka cire mutun da Aljani to dukkanin halittu
suna cikin fargaba idan ranar Jumu'a tazo
saboda suna tsammanin a ranar kiyama zata
tsayu.
YAKU YAN UWA MUSULMI
Manzo tsira yana girmama wannan rana, Yana
yawaita salati ga kansa, Dan haka yazama Muma
wajibi garemu yawaita salati gareshi, Dan salati
Gareshi kamar Addu'a ce.
Daren Jumu'a nada matukar falala wato (Cikin
dare ranar Alhamis) Ana bukatar yawaita salati a
daren, Ana Bukatar kowane musulmi ya yawaita
neman lada a dare domin shirin zuwan ranar,
Kamar misali Daren Sallah ne da ake yin komai a
ranar Jajirbiri!
YAKU YAN UWA MUSULMI Akwai Wasu ayyuka
da Manzo tsira ya kasance yake aikata a cikin
dare da rana ta Jumu'a
1-Annabi na karanta surutul Sajada, Da kuma
Suratul kiyama, A cikin sallar asuba ta wannan
daren, Saboda wadannan surorin suna bayani
game da ranar kiyama,
Daren Jumu'a nada matukar falala, Kamar yadda
yazo a cikin hadisin sa ''MAFICIN SALLAH ITA
CE SAMUN SALLAR ASUBA A CIKIN JAM'I''
Yaku muminai kunji wannan falalar mai matukar
amfani wadda yakamata mukiyaye mu dinga
halarta sallar asuba cikin jam'i!
2-An so yawaita salati a ranar yana da kyau
takaita duk wata ibadah dan mukeyi a ranar dan
samun wannan garaba sar.
Domin salati kamar addu'a ce garesa,
Manzo Tsira da kansa yana fada cewa ''KUSANI
RANAR JUMU'A AKA HAIFI ADAM KUMA RANAR
ZA'A BUSA KAHO''
3-Anaso kowane musulmi yayi wanka, Yayi tsafta
yan sanya kaya mafi kyau, Ya sanya turare.
4-Aswaki
5-Zuwa massallaci da wuri
6-Inda hali kazo kasa.
Kamar yadda hadisi ya tabbata cewa ''BABU
WANI DA ZAIYI WANKA RANAR JUMU'A
SANNAN YAZO YA SALLACI SALLAR WAJIBI
FACE SAI AN GAFARTAMASA HAR ZUWA WANI
SATIN''
YAN UWA MUSULMI Ya chanchanta muzama
cikin masu zuwa da wuri saboda samun damar
zaunawa a massallaci dan yin salati, Sannan
kuma Mala'iku suna yiwa wanda ke zaune
massallaci addu'a.
To amma abun takaici wasu na kauracewa zuwa
da wuri, Zakaga wasu basu wuri sai anfara
khudbar, Wasu kuma sai anyi rabi wasu kuma sai
an gama, Wasu kuma sai Tada sallah, Kai wasu
ma sai an yi raka'a daya!
Shedan ya hana musulmi more ma wannan
romon!
Yaku yan uwa musulmi muji tsoron ALLAH .
Hadisi daga manzo tsira na cewa ''DUK WANDA
YAYI WANKA IRIN NA JANABA (Dama wankan
tsarki iri daya ne a musulmi) ZA'A BASHI LADAR
WANDA YABADA KYAUTAR RAKUMI, WANDA
YAZO NA BIYU ZA'A BASHI LADAR WANDA
YABADA SADAKAR SA, NA UKU KUMA ZAI SAMU
LADAR WANDA YABADA KATON RAGO NA HUDU
KUWA ZAI SAMU LADAR WANDA YABADA KAZA/
ZAKARA NA BIYAR KUMA ZAI SAMU LADAR
WANDA YABADA KWAI''
Wanda kuma sai da limamin yazo ba'a sanyi shi
cikin lissahi.
Akwai abubuwa guda biyar da ake saran da adam
zai dace da Aljannah a ranar jumu'a akwai,
1-Gaida marar lafiya (ranar jumu'a)
2-Zuwa jana'iza (ranar jumu'a)
3-Azuni
4-Zuwa Massallaci da wuri
5-Inta bawa ko baiwa, (Taimakawa wajen biyan
bashi)
Tafiya Kasa zuwa massallaci ranar jumu'a nada
matukar falala kamar yadda yazo a cikin hadisi
cewa ''DUK WANDA YATASO DAGA GIDA DA
KAFAFUNSA SUKAYI KURA (DAUDA) TO
KAFAFUN SUN HARAMATA SHIGA''
JUMU'A Nada sharadi kamar haka
Yin shiru a lokachin huduba, Kamar yadda ALLAH
Madaukakin sarki yake cewa ''IDAN ANA
KARANTA QUR'ANI KU SAURARA WATA QILA SU
SAMU RAHAMA'' Kunga kuma huduba ana kawo
ayoyin Qur'ani. Kai wajibi ne yin shiru idan ana
huduba!
Banda wasa, ko gaishe gaishe,
Ba hallata kayi tafiya dab da lokachin Jumu'a sai
inda ta zama wajibi, Saboda karamawa da
girmama wannan ranar!
Yana da kyau karanta suratul kahfi a ranar
Jumu'a, Saboda Annabi na cewa ''DUK WANDA
YAKARANTA SURATUL KAHFI RANAR JUMU'A
ALLAH ZAI HASKAKA MASA HAR WANI SATIN''
Muna rokon ALLAH Tare da tuwassalin da
wannan khudbar ka biya mana bukatun mu, Ya
ALLAH Ka baiwa Mai martaba Emir na Tsafe
lafiya, Kasa asamo abunda akaje nema a kasar
india, Ya ALLAH Kasanya garin mu Albarka ka
yafemana kayi jagora ga shuwagabbani mu Baki
daya, Ka jikan mamatan mu Baki dayan su.
ALHAMDULILLAH
©®IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA
18/Jimada Akhair/1438
17/03/2017.
ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAHI WABARAKATUHU. MU KOYI IBADA A SAUKAKE
Friday, 8 December 2017
HUDUBAH MAI TAKEN JUMA'AH DA HUKUNCE HUKUNCENTA
Subscribe to:
Post Comments (Atom)
No comments:
Post a Comment