Friday, 8 December 2017

HUDUBAH MAI TAKEN WATAN SHA'ABAN

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #WATAN SHA'ABAN
Godiya ta tabbata ga ALLAH madaukakin sarki,
Muna gode masa, Muna neman taimakon sa,
Muna kara gode masa da baiwar bamu Haske
(Qur'ani) daga garesa,
Na shaida annabi Muhammadu bawan ALLAH Ne
kuma manzo sane, Da iyalan sa da sahabbansa
da dukan wadanda suka biyo bayansu da
kyautatawa,
Yan uwa musulmi yau Khudbar mu zatayi
magana ne akan Watan sha'aban falalar sa da
kuma ayyukan da'ake bukata a aikata, Da kuma
wadanda yakamata a kaura cewa,
Watan sha'aban daya ne daga cikin watanin
musulunci, Kuma wata ne mai daraja, Wata ne
wanda ALLAH Yahada ya kasance kusa da watan
Ramadana mai alfarma!
Manzo tsira S.A.W Yana cewa ''LALLAI ALLAH
MADAUKAKIN SARKI YANA ZUBA WATA BAIWA
WATA NI'IMA A KOWANE WATA DAN HAKA MU
TASHI MU NEMETA A WATAN''
Yaku yan uwa musulmi Wannan hadisin mai
daraja yana koyar damu abubuwa guda biyu
kamar haka
1-Muyi kokari mu dinga rokon ALLAH Da dagewa
wajen bauta masa, Domin dacewa da lokachin da
ALLAH Ke raba wannan ni'imar,
Manzo S.A.W Yana yawaita azumin nafila a cikin
wannan wata mai daraja na Sha'aban! Har ma
Aisha R.A Tana cewa ''"KAI KACE YANA
AZUMTAR WANNAN WATAN NE BAKI DAYA
"" (Saboda yadda yakasance yana azumtar
wannan watan)!
Yan uwa musulmi yawaita azumtar wannan
watan zai sa dan Adam yaji sauki wajen yin
azumin farilla (Ramadana)!
2-Kowane bawa ya lizimci rokon ALLAH Kowane
lokachi, Dan dacewa da wannan lokachin, Dan
samun ingantuwar rayuwa mai albarka, Muna
Ya ALLAH Ya amintar damu tare da ruhin mu, Ya
kuma yarda damu Ameen!
A wani hadisi wanda Usama ya ruwaito yana
nuna mana muhimmancin dake tattare da azumi
a cikin wannan watan na sha'aban! Hadisin na
cewa "USAMA YANA CEWA YA MANZO ALLAH
S.A.W NAGA KANA YAWAITA AZUMI A WANNAN
WATAN (SHA'ABAN) SAI MANZO S.A.W YACE
EH NAGA MUTANE NA QIN AYYUKA A CIKIN
WATAN GASHI KUMA ANA DAGA AYYUKAN BAYI
A WATAN DAN HAKA NIKEYI DAN A DAGA
AYYUKANA AKWAI AZUMI A CIKI"
Yan uwa musulmi muyi kokari mu gyara zukatan
mu, Mu gyara ayyukan mu, Mu gyara taraiyar mu
ta yau da kullun!
Yaku yan uwa musulmi akwai wasu abubuwa
dake bijirowa a cikin addinin marar sa asali,
Wadanda shedar ke kawo mana, Daga cikin
akwai, Yana sanya mutane azumi a watan daya
gabata (Rajab), Wanda babu wani nassi
ingantacce dake magana akan haka,
Yan uwa musulmi wannan watan sunansa
Sha'aban larabawa sun kasance suna yawaita
ayyuka a ciki kama daga noma, Fatauci da kuma
komawa cikin yaqi, Saboda basu yaki a cikin
watan daya gabata!
Koda addinin musulunci yazo sai ya maida watan
sha'aban watan aiki, Amma na azumi,
Magabata na kiran wannan watan da suna watan
Qira'a, Ko kuma watan karatu, Saboda tanadi da
shiryawa zuwa watan Ramadan
Idan kai mai Qira'a ne ko tafsis yakamata kaci
gaba da yin gwaji karatun ka dan zuwan
Ramadana,
Yan uwa musulmi mu gyara bitar mu, Da tafsir
idan kai mai tafsir ne!
Ya ALLAH Ya gwada mana zuwan sa lafiya,
Watan sha'aban wata ne mai daraja kamar
manzo s.a.w yake cewa "WATAN SHA'ABAN
IDAN YAYI ALLAH NA GAFATARWA MUTANE
DUKA IN BANDA MAI GABA DA MAI SHIRKA"
Yan uwa musulmi kunji fa illar take tattare da
Shirka da kuma gaba, Dam haka duk mai shirka
ko gaba yakamata yayi gaugwar tuba,
Kada mu bari wannan garaba sar mai tarin yawa,
Mu gyara ayyukan mu ta hanyar bin abunda
musulunci yazo daci sau da qafa, Mu kiyaye
bidi'a kada muyi wa shedan biyyaya,
Akwai wasu karyayyaki da wai akwai wasu
sallalo da zikirai, Da wai akeyi a cikin wannan ,
Wanda wannan baida asali a musulunci!
Hanyoyi qalilan da aka amince a aikata a wannan
watan sune
-Tsayuwa a tauhidi
-Azumin nafila
-Yawaita rokon ALLAH
Yaku yan uwa musulmi mu fadawa iyalan mu, Da
yayan mu su sani cewa su ranka dukan azumi na
ramadana wanda ake bin su,
Dukkan wadanda keda matsala kama daga
matafiya, Mai jego, Mai haila da kuma marar sa
lafiya, Dasu ranka wadannan azumin da ake biyar
su, Domin akwai hadari ALLAH Yasamu bawa ana
binsa bashin azumi ga kuma wani ya taho,
Yaku yan uwa musulmi mu kiyaye daukar azumi
kafin kowa yadauka, Domin akwai masu daukar
azumi kafin kwana daya ko biyu, Wai da gudun
idan an samu matsalar lissafi bata shafe su ba,
To yakamata su sani cewa manzo s.a.w yana
cewa "DUK WANDA YAYI AZUMI YANA SHAKKA
YA SA6AMA BABBAN QASEEM S.A.W" Kunga
dole ne a dauka tare kuma a aje tare,
Hakama wani hadisin na cewa "AZUMIN DA
ALLAH KE KARBA SHINE WANDA AKA DAUKA
TARE KUMA AKA AJE TARE"
Musulmi kada muyi rigima, Ko bijerewa umarnin
shuwagabanin mu, Koda an samu karin bai wuce
kwana daya, Kuma akwai hadisin dake bayani kan
haka manzo s.a.w yana cewa "IDAN KUNGA
WATA KU DAUKI AZUMI IDAN KUKA DIBA BAKU
GANSA BA TO ANRUFE MAKU SHI TO KU CIKA
TALATIN"
Kungani yan uwa musulmi akwai umarni daga
manzo s.a.w! dan haka muyi biyayya ga
shuwagabanin mu dan tsira gobe kiyama,
Ya ALLAH Kabamu lafiya da zama lafiya, Kayiwa
shuwagabanin mu jagoranci, Kayi mana maganin
zafi na sama da kasa dan aljihu, Ka biya mana
bukatun mu.
ALHAMDULILLAH

©®IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA
08/Sha'aban/1438
05/05/2017.

No comments: