Friday, 8 December 2017

HUDUBAH MAI TAKEN ILLOLIN GIBA KASHI NA BIYU

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #ILLOLIN_GIBA_KA
SHI_NA_BIYU
Godiya ta tabbata ga ALLAH ubangijin halitu, Mai
rahama mai jinkai Mamallakin ranar sakamako,
Muna gode masa muna neman taimakon sa,
Tsira da aminci su kara tabbata ga Manzo tsira,
ALLAH Yayi salati ga manzon rahama da
alayensa da sahabbansa da dukkan wadanda
suka biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar
sakamako.
Yan uwa musulmi a yau zamu chi gaba daga inda
muka tsaya a makwanin da suka gabata, La'akari
da wannan babin (Giba) yana bukatar fadaden
bayani sosai, To hakam tasa muka ci gaba daga
inda muka tsaya.
Hakika addinin musulunci ya wajabta kare harshe
da sauran abubuwan da musulunci ya shar'anta,
Musulunci ya haramta cutar da dan uwa musulmi
ta kowace fuska!
'Wata rana manzo s.a.w yana tare da sahabbai
R.a sai ya tambayesu shin mi kuka sani game da
giba? Sai sukace (Sahabbai) ALLAH Da manzon
sa ne suka sani, Sai Manzo s.a.w yace fadar
wani abu akan wani idan bayanan, Sai sukace
koda abun da kafada gaskiya ne? Sai manzo
s.a.w yace eh koda gaskiya ne, Idan kuwa ba
gaskiya bane to laifin biyu kenan (Laifin karya,
Da kuma na giba)!!
A yanzu Giba ta zama ruwan dare, Ta inda duk
wajen dakaje zakaji ana yinta ana fadar kalamai
kan wani ko wata.
ALLAH Madaukakin yana fada mana cewa "YAKU
MASU IMANI KU NISANCI ZATO DOMIN ZATO
YANKI NE NA ZUNUBI"
Hakama madaukakin sarki na cewa "SHIN
DAYANKU ZAICI NAMAN DAN UWANSA ALHALI
YANA RAYE"
Manzon rahama s.a.w ya fada mana dan
tsoratarwa game da # GIBA yana Cewa "Bani
(Bala'i) ya tabbata ga masu cin naman
dan'umansu"
A koda yaushe muna tare da masu sanya ido
akam mu domin rubuta duk abunda muke aikata
a fili ko a boye, Madaukakin sarki na cewa "KADA
KA FADI ABUNDA BAKA DA ILMI AKANSA
LALLAI DA SAURARE DA GANI DA ABUNDA
ZUCIYA TAYI DUKKAN SU ABUN TAMBAYA NE"
Hakama madaukakin sarki na cewa "DUK
ABUNDA ZAKU AIKATA KUNA TARE DA RAQIB-
ATID"
Tunda har ga masu daukar ayyukan mu tayaya
zamu yin sakaci, Mu rika fada abubuwa kan yan
uwan mu?
Wata rana sahabbai suna zaune da 'Manzo s.a.w
sai wasu sahabbai suka ce ai wane baya cin
abinci sai yaga mutane zasu ci, Kuma baya yin
tafiya sai yaga mutane zasuyi, Sai Manzo s.a.w
yace kunci namansa!!!'
Kudiba girma irin na sahabbai, Kuma abunda aka
fada halin sane, Amma manzo ya fada masu.
Jabir bn Abdullahi ya ruwaito cewa 'Wata rana
muna zaune a wajen Manzo s.a.w sai mukaji
wani wari mai marar dadi, Mai Manzo s.a.w yace
wannan warin wadanda ake konawa ne da juta
saboda sunci naman yan uwansu musulmi, Aka
turo'
Amru bn As wata rana ya tafiya tare da sahabbai
sai suka hadu da wani mushen Jaki a kan hanya,
Sai yace wa sahabbai shin kuna iya chin wannan
naman jakin? Sai suka ce a'a sai yace:Cin
naman sa yafi sauki bisa ga cin naman dan
uwanka musulmi'
Wata rana wani sahabi ya tambayi Manzo s.a.w
cewa 'Shin miye mafita daga Giba? Sai Manzo
s.a.w yace mafita itace ka kare kanka da
iyalanka daga aikata alfasha'
Bayan giba ta baki sai kuma Giba ta zuciya,
Minene giba ta zuciya??
Abunda ake cewa giba ta zuciya itace munana
zato ga musulmi..
Munana zato ga Musulmi ko kuma gibar zuciya,
Shima giba ce da ALLAH Baya yafewa! ALLAH
Madaukakin sarki na cewa "KU NISANCI ZATO
DOMIN YANKI NE NA ZUNUBI"
Hakama Manzo s.a.w yace "Kashedin ku da zato
domin yana daga cikin karyar magana"
Akwai wurare daya halatta kayi maganar mutu,
Wato an lissafa su a cikin Giba to babu laifi...
1-Zalunci-Idan an zalunce ya halatta kaje wajen
wani mai iko kamar sarki, Ko alqali ko iyaye ko
kotu dan a kwato maka hakkinka, Zakayi hakan
ne tare da maimaita duk abunda yafaru dai
dai,Aisha r.a ta ruwaito cewa 'Matar Abu sufyan
ta kawo karar mijinta ga Manzo s.a.w cewa
abincin da yake bata baya isa dan haka tana diba
ta kara dan ya ishesu, Sai Manzo s.a.w yace
mata ba komai dan haka"
Kunga anan akwai halacci mace ta kai kara irin
wannan ta mijinta,
2-Neman fatawa, Ya halarta ka baiyana halin
wani wajen neman fatawa, Misali babana ya
cuce ni, Ko yaya na ko mijina ko matata da niyar
neman fatarwar musulunci akan yadda zaka nemi
hakkin ka.
3-Neman taimako, Neman Taimako zuwa ga wani
shugaba kama ana aikata barna a wani wuri, Ana
shaye shaye ko zina, Zaka iya labartawa
shugaba cewa wane da wane na aikata, Kuma
kafadi hakan ne dan gusar da barnar da ake
aikatawa, To wannan ba'a kiranta Giba, Koda an
kirata to ba laifi akai.
4-Tsoratar da musulmi kan wani sharri, Kafadawa
wani game da wani sharri, Misali yazo neman
bincike game da aure halin wani ko wata, To
anan zaka fadi gaskiyar abunda kasani akai ko
minene babu laifi akan haka nan!
Sai dai idan anfada maka kada kuma ka koma
kafawa ita wada zaka aura ko iyayenta, Cewa
wane ai yace man kaza da kaza akanki, To
wannan kai kayi Gibar!!
Ko kuma kaga dalibin ilmi zaije wajen dan Shi'ah
neman fatawa, To kana iya neman sa kayi masa
bayani akan halinsa.
5-Mai baiyanar da barna qarara, Babu laifi kaga
kafadawa jama'a suyi hattara dashi, Musamman
idan kaga suna kokarin shige masa.
6- Shigiya, Babu laifin idan kaga ana cigiyar wani,
Ka ambaci kamar da dole sai da ita ake ganesa,
Kamar baki, Dogo, Mai qaton kai, Mai idanu da
sauransu, Amma fa da niyar kwatantawa bada
cin zarafi ba!
To a wadannan wuraren 6 kadai ne ake fadar
wani abu game da mutun!
Amma idan shugaba ya zaluncenka bai kamata
duk idan ka zauna kayita fadar saba, Kana
zaginsa alhali wanda kake fadawa baida wani iko
akan ya kwato maka hakkinka.
Hakama wasu sun dauka idan kawai kafadi
magana bayan mutun take giba! A'a Har a gaban
mutun idan kafadi magana wada bata dace kuma
ta bata masa rai to kayi gibar sa!!
Sannan kuma akwai masu gibar karamin yaro,
Suna cewa wancan yaron kaza da kaza suna
aiban tasa, Suna fadar miyagun kalamai kansa,
To duk wannan nau'i ne na giba!!
A wannan yanayin da muke ciki koda ka kare
kanka daga aikata giba, To wani na iya daukowa
yakawo yayi a gabanka, Dan haka sai a kiyaye a
san da suwa za'a zauna.....
Idan kayi gibar wani kuma baka nemi yafiyar sa,
To ranar kiyama za'a debo ladar ka a kara masa,
Idan kuma ta kare za'a debo zunubinka a zuba
masa!!!
Ya ALLAH Ya karemu daga aikata sharruka, Ka
kiyaye mu ka tsare mu, Ya ubangiji ka biya mana
bukatun mu, Kayi rahama garemu ka kyautata
karshe mu Ameen.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe Alzamfari. 07064282182

Jumu'ah 17-Zhul-Hijjah 1438 AH
Friday 8-September-2017

HUDUBA MAI TAKEN TASU'A DA ASHURA

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA


DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #AZUMIN_TASU
'A_DA_ASHURA_DA_BIDI_OIN_DA_AK
A_QAGO_ACIKI
Godiya ta tabbata ga ALLAH Madaukakin sarki
muna gode masa muna neman taimakon muna
neman gafarar sa, Muna neman yakare mu daga
miyagun aiyuka!!
Wanda ALLAH Ya shiryar shine shiryayye babu
mai iya batar dashi, Wanda kuma ALLAH Yabatar
babu mai iya shiryar dashi!
Na shaida babu abun bautawa da gaskiya sai
ALLAH, Kuma na shaida annabi Muhammad
bawan sa ne kuma manzon sa.
Bayan haka, Yan uwa musulmi masu albarka
muna cikin sabuwar shekarar musulunci kuma
watan farko na shekarar, Wata mai albarka mai
falala..
Watan muharram wata ne da ALLAH Ya girmama
ya kuma karrama, kamar yadda yake fada cewa
"LALLAI ADADIN WATANIN 12 NE A WURIN KU
KARRAMA SU KADA KU ZALUNCI KAWUNAN KU
A CIKI"
Ashe kuwa duk abunda ALLAH Ya karrama to
wajibin mu muma mu karrama su,
An karbo daga Aisha r.a tace 'Mutanen jahiliya
sun kasance suna girmama watan Muharram har
suna kiransa da suna Muharram watan ALLAH
Kuma sun kasance suna kauracewa aikata sabo
a cikin '
Yana da kyau mu yawaita azumi a cikin watan
Muharram, Har ma an ruwaito daga Manzo s.a.w
cewa 'Mafificin azumin bayan na watan
ramadana shine azumin watan muharram'
Ibn Rajab yayi sharhi watan Muharram wata ne
falala da ake bukatar yawaita ibadu da
kauracewa zunubi,
Yan uwa musulmi bayan mun azumci kwana
goma a watan Zhul hijja (Watan karshe), Yanzu
kuma sai mu azumci kwana biyu a watan
muharram (Watan farko) za'a rubuta mana ladar
mun fara shekara da ibadah kuma mun kammala
ta da ibadah, Daga hakanan sai a sanyamu cikin
bayi na kirki.
Lallai an mustahabanta muna azumtar wannan
rana domin dinbin falalar dake ciki, An ruwaito
daga Manzo s.a.w cewa 'Azumin 10 ga watan
Muharram ina da yaqinin ALLAH Yagafarta
abunda yagabata'.
Jabir r.a ya ruwaito cewa 'Ban taba ganin manzo
s.a.w na kirdadar zuwan wani azumi ba kamar na
goma ga muharram'
Harma kuraishawa kafin zuwan Manzo s.a.w
suna azumtar wannan rana.
Hakama sadda Manzo yayi hijra zuwa Madina ya
tarar yahudawa nayin wannan azumin, Sai ya
tambaye su miyasa kuke azumtar wannan ranar?
Sai suka ce munayi dan murnar nasarar da
ALLAH Yabaiwa annabi Musa A.s akan fir'auna,
Sai Manzo s.a.w yace 'Ai mune muka fi
chanchanta muyi domin Musa dan uwan mu'
Amma tun yana Makkah yana wannan azumi ya
tambaye su dan yaji hujjar da suka dogara da ita.
Azumtar wannan lokachin nada falala da dama
ga wasu daga cikin.
*Manzo s.a.w yayi, Kenan yasamu falala daga
Manzo s.a.w
A yanzu munyi sa'a kasancewa gobe ne tara ga
wata sai mu tashi da tasu'a jibi muyi ashura.
ABUBUWAN DA AKA KIRKIRO A WANNAN
WATAN
Wasu na shafa kwalli, Wasu na lalle wasu na
dinki da dafe dafen abinci!
Wasu kuma baqin ciki a wannan rana, Har suna
koke koke da saran jikin juna da sauransu!
To a maganar gaskiya wannan baida asali daga
kowane magabaci na kwarai, Wasu kuwa na
cewa awadata gida da abinci wai saboda
shekarar zata kasance ma da kyau.
Wadanda sukeyi wannan kirkiren sune suka
kashe sayyidina Aliyu r.a suka kashe Hassan r.a
kuma suka kashe Hussaini R.a.
Su kuwa nawasib sune suke murna saboda sune
suka kashe ahlul baiti.
Yan shi'ah sune suka kashe sayyidina Hussani
r.a a Karbala kuma sun kashe mahaifinsa Aliyu
R.a, Dukkansu sunyi shahada.
Yan shi'ah sun tanadi ranar ashura a matsayin
ranar baqin ciki, Har suna yanka jikin su da
aikata rashin imani ga yara, Wannan yasabawa
musulunci da kuma lafiyayen hankali, Kuma
babbar alama ce dake nuna yadda addinin Shi'ah
yayi hannu riga da musulunci kuma yana nuna
cewa Shi'ah addini ne mai zaman kansa.
Annabi Zakariya A.s, Da Hassan r.a, Da Umar r.a
da Aliyu r.a duk kashe su akayi amma miyara
basu baqin cikin kashe su??
A musulunci babu wata rana da aka tanada dan
baqin ciki, Idan ma za'a sanya to ranar data fi
chanchanta itace ranar da Manzo s.a.w yabar
duniya. Domin Manzo s.a.w yace 'Duk wanda
wata musiba ta sama ko ta rashi to yayi hakuri
domin rashina shine babbar musiba'' !!!!
Shari'ah ta yarda idan akayi maka rassuwa kayi
jimami har da kuka tsawon kwana 3, Amma
abunda yafaru shekaru dubu daya da wani abu
da ya gabata.
Lallai muyi tsayin daka waje yakar shi'ah a
gidajen mu da yayan mu.
A ranar Ashura yan shi'ah nayi babbar bajakoli
da izgili da zagin sahabbai, Alhali Manzo s.a.w
yace "Kada ku zagi sahabbai na domin wallahi
koda dayanku yaciyar da kwatankwacin dutsen
uhudu na zinare bazai kai muddunsu daya ba, Kai
koda rabinsa!"
Wannan na nuna wallahi koda duk mutanen
duniya zamu bi ALLAH Da ibadah har tsawon
shekara bazamu kai nasu da kwana daya ba!! Ko
da rabi ma..
To mutane masu daraja irin haka kuma sune za'a
zaga??
Yan shi'ah na ziyartar makabartu har suna
ziyartar kabarin Hussaini r.a suna cewa' wai duk
wanda ziyarci kabarin sau daya yafi aiki hajji sau
ashirin' Kunj4 wani cin mutunci!!
A ranar ne suke aikata auren mutu'a!!
Lallai babban dalilin yin azumin shine ranar ne
ALLAH Ya halakar da fir'auna.
Yan uwa musulmi masu albarka an samu sabanin
lissafi inda wasu ke cewa yau tara ga wata, A'a
yau ne takwas ga wata kuma a kasar Saudiyya
yau tara ga wata, Sai dai zamuyi amfani da
abunda ke kasar mu!!
Muna rokon ALLAH Yabamu zaman lafiya, Yayi
jagora ga mai martaba Emir na Tsafe, Da kuma
gafarta margayin daya rassu, Ya ALLAH Yayi
salati ga Manzo rahama da iyalansa da
sahabbansa da wadanda suka biyo bayansu da
kyautata, Ka rahama mana ka biya mana bukatun
mu.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe Alzamfari. 07064282182

Yau Jumu'a 8-Al-Muharram 1439 AH
Friday 29-September-2017

HUDUBA MAI TAKEN HARAMCIN CAMFI

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A DAGA MASJID
ABI HURAIRAH DAKE TSAFE ZAMFARA


DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE


A wannan makon limamin Massallacin Jumu'a na
Abi Hurairah dake unguwar Area2, Tsafe Sheik
Sani Na Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #CHAMFI
Godiya ta tabbata ga ALLAH Wanda ya halicci
duniya da abunda ke cikinta, Godiya ta tabbata
ga ubangiji daya ubangijin rana da wata, Godiya
ga wanda kagemu ya bamu ikon gudanar rayuwa.
Tsira da amincin ALLAH Su tabbata ga mafi
soyuwa wajen ubangiji, Annabi Muhammad s.a.w
da iyalansa da sahabban da duk wadanda suka
biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar
sakamako muna rokon ya shiryar damu hanya
madaidai ciya ameen.
Yan uwa musulmi masu albarka a yau Khudbar
tamu zatayi magana ne game da #CHAMFI!!!
#CHAMFI wato ana nufin danganta faruwa ko
afkuwar wani abu na rayuwa ko mako bayan ta,
Ga lokachi ko zamani ko kwana ko wata ko
shekara ko dan Adam, Ko aure ko mutuwa da
sauransu!!
Bayan Manzo s.a.w yafa mana cewa "Duk wanda
ke #CHAMFI to ya tabbatar yayi shirka"
Shirkar kuwa zata iya kasancewa rakama ko
kuma babbah!!
Jingina faruwar wani abu ga aure ko shugaba
duk wani musulmi mai tauhidi yasan babban
kuskure ne.
Wasu kuma da danganta rashin lafiya da
#CHAMFI da kuma masu danganta duk wani
abunda yasame da #CHAMFI!!
Yan uwa musulmi masu albarka
Babu inda ya halatta ga musulmi yayi #CHAMFI
sai a wuri daya shine kayi #CHAMFI ga kanka
wato duk abunda yasameka a rayuwa ka dauka
cewa daga laifukan da kake aikatawa na rayuwa!
Shi #CHAMFI tsohon abu ne dake da tsohon
tarihi wato ba daga hausawa ne aka fara yin
#CHAMFI ba, Bari muji kadan daga wasu
al'ummah dake aikata #CHAMFI-
Yahudawa sun # CHAMFA Annabi Salihu (a.s)
domin yazo ya isko su cikin bata da shirka,
Yafara yi masu wa'azi ba dare ba rana, Da suka
qi yin imani sai ALLAH Ya jarabce su da musibu!
To sai suka fara yin #CHAMFI cewa Annabi
Salihu (A.S) yakawo masu!
Mushrikai na Makkah suma sun #CHAMFA
Manzo (s.a.w) domin ya isko su cikin kafurci da
bata, Yayi masu wa'azi da suka qi karba sai
ALLAH Ya jarabce su da talauci da rashi!
Suma sai suka #CHAMFA Manzo (s.a.w) cewa
kafin yazo suna cikin arziki, Amma da yazo sun
fara fadawa talauci!
Idan muka diba rayuwar mu ta Najeriya zamu ga
cewa kwatan kwacin rayuwar nan ta same mu, A
baya yan kasa na cikin wadata amma a yanzu
talauci wane hali muke ciki??
To nan yakamata yayi tauhidi yayi amfani,
Garemu.
Yan uwa musulmi masu albarka, Yakamata mu
kara sani talauci da arziki da komai da komai duk
suna hannu ubangiji, Amma sai mu dora laifi kan
shugabanin mu, Shin mu manta cewa akwai yan
Najeriya masu aikata Shirka wanda sune
kolulowar laifi ga ubangiji.
Mun manta fadar ALLAH s.w.t daya fada cewa
"DUK ABUNDA YASAME KU DAGA ALLAH DA
AYYUKAN DA AIKE AIKATAWA"
Hakama madaukakin sarki na cewa "DUK
ABUNDA YASAMU KU MAI KYAU DAGA ALLAH
MARAR KYAU KUMA DAGA ABUNDA KUKE
AIKATAWA NE"
Shi #CHAMFI inkari ne tauhidin rububiya.
Yan uwa musulmi masu albarka, Akwai abunda
jahilai keyi na #CHAMFA Watan safar wato
watan da muke ciki, Ma'ana wata na biyu a
musulunci, Jahilai sun kasance suna kauracewa
aikata ayyuka kamar aure da tafiya da sauransu!!
Sai Manzo s.a.w yace "Babu komai a watan
Safar, Wata ne kamar saura"
Akwai masu alaqanta cuta da #CHAMFI, a yanzu
turawan yamma na farfaganda ta cewa suna
cuta kamar ta sauro da sauransu, Wai sai suce
sun karar da ita, Hakika ita cuta tana samuwane
da iko da iznin ALLAH.
A cikin ayyukan turawa akwai tuka da warwara.
A cikin wannan watan akwai musulmi da suke
cewa wai ALLAH Na saukar da annoba dubu
ashirin da uku (23, 00.000) wai suna cewa ayi
nafila raka'a 4 da fatiha kafa 7 idan kagama za'a
rubuta 'Salamun ala nuhin' a rubuta a sha.
To wannan baida asali a musulunce kuma bidi'ah
ce!
Su duka al'amura da faruwa ne da ikon Allah.
Babban tabi'i imam alhambali yace "Kebance
wani lokachi dan a aiyana cuta garesa kuskure
ne"
Wani fasihin mawaki na cewa 'Muna ta dorawa
zamani laifi mun manta mune ke aikata laifin ba
zamani ba'
Yan uwa musulmi masu albarka, A kowane
lokachi mu zama masu imani domin bamu san
inda ajalin mu yake ba!
A takaice dukan wani abu da ake aikata wato
#CHAMFI shirka ne kuma bata ne!!
ALLAH Yabiya bukatun mu ya gafarta mana yayi
rahama garemu, Yabamu zaman lahiya mai
dorewa.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe Alzamfari. 07064282182

Jumu'ah 13-Safar1439 AH
Saturday 03-November-2017

HUDUBA MAI TAKEN LAYYA DA HUKUNCE HUKUNCENTA

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA


DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #LAYYA_DA_SALLAR
_IDI_DA_ABUBUWAN_BUKATA_A_WANN
AN_WATAN_DA_KYAWAWAN_HALAYE_A_
WAJEN_BIKIN_SALLAH
Godiya ta tabbata ga ALLAH Madaukakin
sarki,Muna gode masa,Muna neman taimakon
sa,Muna neman ya kare da sharrin kawunan mu
da miyagun ayyukan mu, Tsira da amincin ALLAH
Su kara tabbata ga manzo tsira, Annabin rahama
sallallalahu alaihi wassalam, Da iyalansa da
sahabban sa da dukkan wadanda suka biyo
bayan su da kyautatawa har zuwa ranar
sakamako.
Yan uwa musulmi yau Khudbar zata magana ke
wannan halin da ibadu dake gaban mu,
Yan uwa musulmi muji tsoron ALLAH Gaskiyar jin
tsoron sa, Kamar yadda umarce, Kuma mu kara
gode masa kamar yadda ya umarce mu, Sannan
abu ne mai kyau mu dage da ambaton ALLAH A
Wannan lokachin kamar ya umarce mu da cewa
"YAKU WADANDA KUKA YI IMANI KU AMBASHI
ALLAH AMBATO MAI WAYA KUYI KUMA TASBIHI
GARESHI"
Yan uwa masu albarka muyi tseararre a wannan
lokachin (Anan ana bukatar tsere) domin suna
cikin kwanakin da Allah ya kebance dan rahama
da tausayi ga bayin sa!
Yawaita ambaton ALLAH A cikin wannan lokachi
abu ne mai matukar muhimmanci, Hasalima an
ruwaito Abi Huraira R.a ya kasance yana shiga
ko ina yana yawaita yin kabbori, Har cikin
kasuwa yana shiga dan tunasar da yan kasuwa
da masu sayyayya, Yana daga murya yana cewa
'Allahu akbar Allahu akbbar, Allahu akbar wallahu
Akbar walil lahil hamdu'
>LAYYA
Daga cikin kwanakin goma akwai wata babbar
ibadah da ake aiwatar a wannan watan, Layya
nada sharudda
-Amfani da kudin halal wajen sayen dabbar
zakuyi amfani da ita,
Ita layya Sunnah ce daga sunnar annabawa,
Annabi Ibrahim A.s da kuma Annabi Muhammad
S.a.w , Inda tayo asali shine lokachin da annabi
Ibrahim yayi mafarkin ya yanka dansa wato
Annabi Isma'il A.s, Alqur"ani yabamu labarin
cewa Ya yanka dan nasa"SAI MUKA FANSHI
YARON DA ABUN YANKA MAI GIRMA (Rago)"
Layya abu ce dake kara kusanta bawa da
ubangijin sa, ALLAH Ya umarci Manzo s.a.w da
zuwa sallar idi, Da layya kamar yadda yake fada
cewa "KAYI SALLOLI KUMA KA YANKE LAYYA
KA DAN ALLAH DA KUMA TSARKAKA WAJEN
ALLAH"
Hadisi yazo daga sahabin manzo s.a.w cewa
"Mun kasance da ranar arfa da Manzo s.a.w
yace lallai yazama tillas ga kowane gida suyi
layya"
Ashe yazama wajibi ga kowane gida suyi layya,
Malamai sunce gida guda suna iya hadawa asayi
dabba dan ayi layya!
Hakama wani hadisi da yayo ya tsoratar da masu
tabi'ar matsolanci cewa "Manzo s.a.w yace 'Duk
wanda keda wadatar yin layya baiyi ba to kada
ma yaje massallachin idi' "
Sau da yawa zakaga magidan ci a ranar jajibiri
ya sawo wancan ya sawo wanchan, Dan adafa
abinci amma ya kasa yin layya, Ita wannan sallar
ba sallah bace ta dafe dafen abinci, Sallah ce
yanka layya!
Sheik Muhammad bn fodio yace: 'Idan bakayi
layya ba, Kuma ka dafa abinci ko wannan abincin
bidi'ah ce '!!
*Layya ta hau wajibi ga kowane musulmi, baligi,
Mai hankali, Mai wadata, Mazaunin gida, Amma
kananan yara sunnah ce, Yin layya koyi ne da
Manzon rahama s.a.w.
Ibn taimiyah yace 'A ibaduh na jiki babu kamar
sallah, A ibada ta kudi kuma babu kamar layya'
Layya ana yin tane daga dabbobin ni'imah wato
sune kamar haka-
~Rakumi rakuma
~Sa ko saniya
~Rago ko Tunkiya
~Bunsuru ko akuya.
Wadannan dasu ne kadai ake yin layya!
Sau da yawa zakaga wasu na sakaci wai da
sunam suna jin kunyar yanka bunsuru ko tinkiya
ko akuya, Dan basu da halin sayen Rago, Wannan
bai dace ba, Hausawa ma suna cewa dai dai kurji
dai dai ruwa!!
Yan uwa musulmi masu albarka, Sai dabbar layya
ta cika wadannan sharuddan sannan take layya,
~Rakumi ko rakuma sai sun kai shekara 5
~Sa ko saniya sai sunkai shekara 2 zuwa ta 3
~Bunsuru ko akuya sai sunkai shekara 1 zuwa
cikin ta 2
~Rago ko tunkiya sai sun kai shekara 1 !!
Duk da akwai basu dake cewa ana iya yanka mai
wata 6, Amma wannan bai inganta ba!
Dole ne dabba ta tsarkaka daga aibi, Wato wasu
kuma sharudda kamar haka,
~Ba'a layya da mai ido daya
~Rashin lafiyar da data baiyana
~Dabba mai gurgunta
~Tsohuwar dabba marar mai marar bargo
~Mai yankakke kunne, Ko bindi ko marar hauru
da sauran illoli baiya nan nu, DUK BA'A LAYYA
DA SU!!!
Ana son dabba wadda idan ka kalle ta zakaji
wadata.
Idan ka sawo dabba sai daya daga cikin matsalar
chan ta same ta, Malamai sunce ba ba komai
abunda dai ba'a so shine kaje saye kaganta da
wannan illar kuma ka sawo.
Hikmar dake cikin layya:
1-Kusanta bawa da ALLAH Domin ciki umarni ne
Na ubangiji kamar yadda madaukakin sarki ke
cewa "ALLAH BAYA BUKATAR NAMA KO JINI
YANA BUKATAR TSARKAKE NIYA"
2-Dan samarwa mabukata, Wato rabawa
wadanda basu yi ba, Saboda rashin hali
3-Kara soyyyaya tsakanin musulmi, Duk wanda
ya dauki nama ka bashi zaiji farin ciki da kara
sonka
4-Alamace ta daga addinin Allah, Domin yin layya
daga addini ne,
5-Koyi ce da jagorori wato annabi Ibrahim A.s da
Annabi Isma'il A.s, Mu diba fa annabi Ibrahim a.s
ce masa akayi yayi layya da dansa,Kuma ya
dauki azamar yi,
6-Yin layya ko ne da alhazai, Su suna yin hadaya,
mu kuma dake gida muna yin layya.
SALLAR IDI
Sai kuma bangare na biyu, Manzo s.a.w ya
wajabta mana sallar idi, akwai hadisi daga
manzo s.a.w da yake cewa "Manzo s.a.w yazo
garin yasrib (Madina) ya iske suna yi wassani
biyu a shekara, Sai manzo s.a.w yace ku aje
wadannan ga wasu nan wato ranakun sallah"
Manzo s.a.w yayi umarni a fita a ranar sallah
zuwa idi, Har wata mata tambaye sa to ni ina
son fita amma banda hijabi sai yace kije ki aro.
harda mata masu haila suna iya fita,
IDAN RANAR JUMU'A TA HADU DA RANAR EID
Manzo s.aw. idan ranar JUMU'AT Ta hadu da
ranar Eid to kana da zabi, Ba sai kayi jumu'a ba,
Amma Abu hurairah yace mu muna yi dan samun
lada mai yawa, Anyi haka dan falala garemu,
Saboda hidimar sallah wani na'iya mantawa da
sallar jumu'ar mah,
MIYAGUN DABI'U RANAR SALLAH
Ranar sallah rana ce ta farin ciki da murna,
Wadda musulunci ya ware muna a shekaru sai
biyu wato sallar azumi wato karamar sallar sai
kuma sallar layya ko kuma babbar sallah,
A lokachin sallah ana ado sosai kuma ana
ziyartar yan uwa da abokan arziki, Ko kiran waya
da dai sauran hanyoyin sada zumunta, Sai da
kash!
Ana samun masu amfani da wannan damar suna
wuce wuri har suna afkawa cikin haramun, Kusan
yazama al'adar wasu iyaye ta kyale yayan su
suyi abunda suka ga dama a ranar sallah ba tare
da taka masu burki ba,
A ranar sallah zakaga matasa musamman yan
mata sun chaba ado sun fito, Kirjin su a waje,
Bayan su a zahiri, Duk suna murnar sallah!
Wasu kuma a ranar suke fara iya shaye shaye
musamman samari, Wasu ma matasan a ranar
suke iya zina, Anan arewa cin Najeriya musan
yadda yayan mu suka tarbiyan tu da rufe jikin su
ta hanyar hijabi, Amma abun takaici zakaga wasu
ko gyale ma basu sawa,
Suwa keda laifi??
Manyan manyan masu laifi sune iyaye, Idan aka
ce iyaye ana nufin iyaye maza da iyaye mata,
Laifin uba anan shine shine ke sawo kayan to
dole kai zaka saka ido kan yadda za'a dunka
kayan dama yadda za'a sanya su, Zakaga uba
yasawo kaya kawai ya baiwa yayan, Haka bai
dace ba sam!
Ita kuma uwa ita ce ake kai dinkin agabanta,
Wajen sanya kayan ma agabanta, Amma bata iya
tsawatarwa akan abunda ke yi na kuskure, Iyaye
ku tuna Manzo Allah s.a.w yace mana "Dukkan
ku masu kiwo ne kuma za'a tambaye ku game da
abunda aka baku kiwo"
Masu laifi na biyu sune shuwagabani, Dole ne
shugabanin ku dauki matakan gyara tarbiyar
al"ummar su ta hanyar sanya idanu aka harkokin
su, mai makon haka sun bar al'umma kara zube
Na ukku sune malamai, Malamai sune suka san
hukuncin addini, Kuma sune masu wayar da kai
ta hanyar nasihohi da khudbobi da sauransu, Dole
ne malamai su zage damtse ka'in da na'in wajen
tabbatar da tarbiyar al'umma dan samun manya
gobe na kirki,
Manzo s.a.w yana cewa '"Mata ku zauna cikin
gida jen ku kada hali inyi na jahiliyah (fita
barkata)"
Sannan manzo s.a.w yakawo hadisi mai
tsoratarwa da yake cewa "Mata 2 yan wuta ne,
Ni ban gansu ba, Idan kun gansu ku tsine masu,
Sune masu sanya tufa amma basu sanya ba, Na
biyu sune masu fitar da gashi waje basu shiga
aljannah ko kan shinta bazasu ji ba, Duk da
akwai nisa daga kaza zuwa kaza"
Abun takaici wasu yan mata har dakunan samari
suke shiga da sunan yawon sallah,
Wasu kuma baso da murnar sallah basu yin
sallah suna ji ana kira amma basu zuwa, Dukka
dai muna fatar za'a gyara.
ALLAH Madaukakin sarki ya gafarta mana ya
rahama, Ya biya mana bukatun mu, Yayi rahama
ga mamatan mu.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe Alzamfari. 07064282182

Jumu'a 3-Zhul-Hijjah 1438 AH
Friday 25-August-2017

HUDUBAH MAI TAKEN RAMADANA DA ABUNDA YA KUNSA

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA


DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #FALALAR WATAN
RAMADAN DA ABUNDA YA KUNSA
Godiya ta tabbata ga ALLAH Wanda ya sanyawa
bayin sa alamomi da zasu zama alama garesu da
yin bauta a lokachin,
Tsira da aminci su tabbata ga wanda ALLAH Ya
aiko da gaskiya da iyalansa da sahabbansa da
dukkan wadanda suka biyo bayansa da
kyautatawa sallallahu alaihi wassalam,
Yan uwa musulmi muna fuskantar wani yanayi
mai matukar alfanu, Wanda yana kyau muci ribar
wadannan kwanuka mu yawaita taimakon kanmu,
Mu yiwa kawunan mu hisabi, Yakamata muyi
amfani da wannan dama wajen neman gafara da
yafiya daga ubangiji ALLAH,
Watan ramadana wata ne mai alfarma wanda
ALLAH Yasanya shi daga cikin rukunan
musulunci, Ramadana wata ne na tausayi da
rahama da taimakon juna.
A cikin watan ramadan akwai wata rana wadda
tafi dare dubu,
Yan uwa musulmi mu karrama wannan watan da
abubuwa guda biyu (2), Na daya ALLAH Ya ara
mana rayuwa ta kawuwa wannan watan, Sai
kuma zuwan watan na ramadan mai albarka,
Yan uwa musulmi akwai abubuwan da yakamata
mu aikata a cikin wannan watan mai kamawa,
Daga cikin su akwai;
-Mu roki ALLAH Ya yarda damu, Ya karbi dukkan
ibadun da mukayi, Duk wanda aka karbi ibadun
su a cikin watan ramadan to yayi murna yayi
farin ciki,
Lallai kololowar murna ita ce kayi murna da
zuwansa, Da kuma ni'imar halartar sa, Akwai
wanda yafara jin kanshin sa Amma ALLAH Bai
nuna masa ba, Baya daga cikin addini yin murna
walau ta samun matsayi ko dukiya kamar yadda
aya take cewa "GASUNAN SUNA FARIN CIKIN
DAN SAMUN DUNIYA ALHALI BA KOMAI BACE
IDAN KA KWATANTA DA LAHIRA"
-Kiyaye salloli na farilla a cikin lokachi, Idan har
baka sallah cikin jam'i to yakamata kayi amfani
da watan ramadan dan koya da yin sallah cikin
jam'i
-Kaucewa yin sabo, Kaucewa aikata sabo kowane
irin, Ba kauracewa ci da sha ne kurum azumi ba,
A'a harda kiyaye gabobi baki daya daga aikata
zunubai,
-Mai hankali baligi ya sanya a ransa zaiyi azumi
dan ALLAH, Dan kwadayin lada, Da kuma
kaucewa fadawa azabar ALLAH.
Muddin aka samu mutun kawai zai yi azumi dan
yazama dole, Dan kada ace wane baiyi to akwai
matsala, Yakamata a gyara dan samun ladar da
ake nema.
Azumin watan ramadan yana farawa ne da zarar
wata sha'aban yakai ashirin da tara idan ba'a ga
wata ba kuma yakai talatin, kamar yadda hadisi
daga manzo rahama na cewa "KUYI AZUMI IDAN
KUNGA WATA KU AJE IDAN KUNGA WATA"
Idan har mai alfarma sarkin Musulmi yabada
umarnin daukar azumi, To kada ayi wata wata
wajen dauka,
Idan aka bada umarni to akwai abubuwan da
yakamata ayi kamar;
-Kulla niyyah a zuciya, Ba ambatawa da baki ba,
-Sallar tarawihi, Ko a daren yau za'a iya fara
tarawihi dama ana bukatar a tari wannan watan
da aiyuka na alheri dan su zame ma jiki, Idan
watan yazo zaka iya,
>Yan uwa musulmi abunda ake cewa azumi shine
barin chi da sha da kame gabobi, ALLAH
Madaukakin sarki na cewa "KUCI KUSHA HAR
SAI BAKIN ZARE YA FITO DAGA ALFIJIR"
=Hakama yakamata ladanai kuji tsoron ALLAH
kada ladanai su kuskura su kira sallah kafin
lokachi yayi ko bayan lokachi, A yanzu muna
cikin yanayi na damina wanda gari ke laulayewa,
Jiya anan Tsafe anyi ruwa, Wasu ladanai sunyi
kiran sallah tun karfe 6:30pm, Maimakon
6:55pm.
Anan fa mutane uku ne keda laifi na daya Ladani
shi da ya kira sallah kafin lokachi yayi,
Sai kuma limani wanda shine jagora yaje yabada
sallah,
Sai kuma mamu wanda yakamata ku lura da
jadawali, Kafin sallah!
Anan jahar, Gwamnati tana raba jadawali a duk
wani massallaci komai yadda yake cikin lungu,
Kada kuma sai ladani yaci yakoshi har lokachi ya
wuce sannan yace zai kira sallah,
Idan ladani ya kira sallah lokachi baiyi ba, To
Ladani ne keda alhaki na karewar azumin su,
Alfijir na fitowa ne 04:55/6, Magrib 06:55, duk
yanayi n chanzawa, A kula sosai idan ladanai
sunyi kuskure mafita kurum a dinga diba
jadawalin da gwamnati ke kawo, Kowane lokachi
basai radaman ba.
-Tarawihi babbar sunnah ce dake nuna alamar
tsayawar ramadan, Ana samun falala a ciki.
Limamai aji tsoron ALLAH
Limamai aji tsoron ALLAH
Limamai aji tsoron ALLAH
Sau da yawa zakaga limamai na wulakanta
sallah, Ta hanyar yin qoton kurciya da yin ta
yadda aka ga dama,
Manzo rahama na cewa "KUYI SALLAH KAMAR
YADDA KUKAGA INAYI"
To sai ayita gwargwadon hali,
Wani mutun yazo yana sallah yagama yazo
wajen manzo ALLAH Sai manzo s.a.w yace ka
koma kayi sallah dan bakayi sallah ba, Sai da
akayi sau 3, Daga nan manzo s.a.w ya gwada
masa yadda zaiyi da kyau ta hanyar jeranta
kira'a da yi anatse da cikin ruku'u da sujjada,
=Yana da kyau a rage sautin amsa kuwa (Loud
speaker), Domin kada karatu na chan dana chan
su hade sai kaji duk abu ya rikice.
Wata rana Manzo s.a.w ya shigo massallaci ya
tarar kowa na sallar sa anan yahada su kan
limami daya wato Ubaiy bn Ka'af R.A
Hakama wajen yin tahujjud akiyaye.
Yan uwa musulmi manzo s.a.w ya kai karshe
komai game da ganin wata, Idan an samu rikici
to ko kaine ko wani ne ya rikice, Manzo rahama
s.a.w na cewa "IDAN KUKA DAUKA BA'A GANI
BA KU CIKA TALATIN"
Idan sarki musulmi ya bada sanarwar angani ka
sallama kawai ka dauka,
Kasar Saudiyya Yau watan su talatin yake amma
mu 29, Idan mungani zamu dauka anan Najeriya,
Yan uwa musulmi a cikin watan ramadana ana
bukatar taimakon juna, A taimakawa talakawa da
abinci koda koko da kosai ne, Domin wani ko
abincin buda baki baida shi, "Manzo s.a.w ya
kasance idan watan ramadan yazo yakan yawaita
alheri kai kace iska ne ya taso".
Ka taimaki yan uwa musulmi anan za'a gane
kana taimako.
Kuma taimako bawai sai masu kudi ba kowa
yasan wanda yafi sai ka taimaka masa, ALLAH
Madaukakin sarki na cewa "KU TAIMAKA A KASA
NI DAKE SAMA ZAN TAIMAKA MAKU"
Muna rokon ALLAH Sunayen kyawawa, Tsarkaka
ya biya mana bukatun mu, Yayi mana gafara da
rahama, Ya karbi ibadun mu wadanda mukayi da
wadanda zamuyi,
Ya ALLAH Yabaiwa shugaban kasa da Mai
martab emir na Tsafe lafiya, Yayi jagora ga
shuwagabanni mu, Ya shiryamu hanya madaidai
ciya.
ALHAMDULILLAH

©®IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA
29/Sha'aban/1438
26/05/2017.

HUDUBAH MAI TAKEN SABUBBAN DAKE SA A SHIGA ALJANNA

HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan SABUBBAN DAKE
KAIWA ZUWA GA ALJANNAH DA KUMA CIKAWA
MAI KYAU DA KUMA MASU KAIWA ZUWA WUTA
DA CIKAWAR MARAR KYAU
Godiya ta tabbata ga ALLAH Muna gode masa
muna neman taimakon sa, Mune neman yakare
daga sharrin kawu nan mu,
Duk wanda ALLAH Ya shiryar babu mai batar
dashi, Duk wanda ALLAH Yabatar babu mai iya
shiryar dashi,
Tsira da amincin ALLAH Su kara tabbata ga
mafifin halittun manzo tsira, Da iyalan da
sahabban sa, Da dukan wadanda suka biyo
bayansu da kyautatawa.
Yan uwa musulmi muyi gaggawar tuba zuwa ga
ALLAH Dan neman yagafarta mana daga laifukan
da muke aikatawa,
Ibadar da muke aikata duka bata kara ALLAH Da
komai, Hakama Fandare mai bai ragesa da
komai, Kamar yadda yake fada cikin hadisul kudsi
cewa ''YAKU BAYINA IDAN ZAKU KURE WAJEN
BAUTA MANI BAZAKU KARANI DA KOMAI BA
KUMA IDAN KUKA KAFURCE MANI BAZAKU
RAGE NI DA KOMAI BA''
YAN UWA MUSULMI Hakika aikata ayyukan alheri
suke kai mutun ga samun aljannah, Kolololuwar
sune ayyukan zukata,
Sannan aiyukan jiki sune ke taimaka ma zuciya
hadisin sahihi ya tabbata cewa ''DUKAN AYYUKA
TARE DA NIYA SUKE TAFIYA''
Aiyukan marar sa kyau kama daga Cuta, zalunci,
Yaudara munafucci E.t.c suke haddasa halin da
muke ciki kamar yadda ayar Qur'ani take cewa
''BANNA TA BAIYANA A SARARI DA KUMA CIKIN
TEKU SABODA AYYUKAN DA HANNAYE KE
AIKATAWA''
Ya yan uwa musulmi yin bauta dan ALLAH Dayin
wasiyya ta kwarai na jagoranta zuwa ga aljannah
hadisin ingantacce na cewa ''ANA CIKA AYYUKA
DA AIKI NA KWARAI DA KUMA CIKI MUNANA
MUMMUNAN KARSHE''
Yan uwa musulmi muyi dukan mai yiwuwa wajen
ganin mun cika da kyawawan ayyukan da samun
tsira gobe kiyama, ALLAH Yana gargadar mu
cewa a suratu ali imran cewa '' KUJI TSORON
ALLAH KADA KU MUTU FACE KUNA MUSULMI''
Kunga kenan wajibi mu nemi yin ayyukan kirki,
Da neman yafiya dan haduwa dashi da imani!
Yaku yan uwa musulmi shagaltuwa da ayyuka na
alheri sa samun cikawa ta kwarai, Hakama
Annabawa kamar su Ibrahim A.S Da Yunus A.S
Sunyi wasiya ga ''Kada ku bautawa kowa in
banda ALLAH'' Kunga wasiya ce mai kyau,
Ababen dake sanya Cikawa mai kyau nada yawa
ga wasu daga ciki
1-KYAKYAWAR NIYA Niya mai kyau wajen aikata
aiyuka.
2-IHLASI wato yi dan ALLAH Kai tsaye
3-KULA DA TSARE LOKACHIN SALLOLI CIKIN
JAM'I wato yin sallah a lokacinta kuma cikin
mutane.
4-GYARA Jawo al'umma zuwa ga hanyar gyara
da zata taimaka masu wajen kara kusanci da
ALLAH Kamar yadda ayar Qur'ani ke cewa ''DUK
WANDA YAYI AIKI NA KWARAI BAI DA TSORON
LOKACHIN MUTUWA''
5-TSORON ALLAH FILI DA BOYE
6-LIZIMTAR SUNNAH DA KOYI DA MAGABATA
NA KIRKI
7-KYAUTAMA AL'UMMA Yi masu fara'a, Da
yawan yi masu kyauta, Da Sadaqah da kuma
yawan yi masu sallama, Duk yana cikin
kyautawa. ALLAH Yana cewa ''WADANNAN
MASU TAIMAKO A FILI DA BOYE TO BABU
TSORON RANAR MUTUWAR SU''
8-KAMEWA CUTAR DA AL'UMMA
9-YIN ADDU'A Kamar yadda ALLAH Ke cewa ''KU
ROKE NI ZAN KARBA MAKU WADANNAN MASU
GIRMAN KAI DA ROKON ALLAH ZASU SHIGA
JAHANNAMA''
10-ADDU'A GA JAMA'A Wato yin jam'in addu'a
ga kamar cewa ALLAH Ka yafe mana, kayi mana
rahama ka gafarta mana, Hadisi ya tabbata cewa
''AKWAI MALA'IKA WANDA DUK KAYI ROKO SAI
YACE KAIMA HAKA'' kunga kenan idan muka roki
ALLAH Da roko mai kyau ko marar kyau duka
zata iya dawowa garemu.
Yaku yan uwa musulmi muyi hattara tare da
kiyaye aikata miyagun aiyuka, Da zarar ka mutu
babu imani to haqira kayi babbar hasara,
Suna da matukar yawa amma ga wasu daga
cikin su.
1-MUNAFURCI Wanda yanzu yazama ruwan dare,
A tsakanin al'umma wanda yake kaiwa ga
mummunar makoma
2-TOZARTAR DA SALLAR FARILLA Tozarta salla
ta farilla yana kaiwa zuwa ga zuwa wuta.
3-JAHILCI Wato rashin karatun addini, Da kin
gaskiya.
4-RASHIN SALLAR JUMU'A Tabbas rashin sallar
jumu'a yana kaiwa kai tsaye zuwa ga wuta.
5-RASHIN JAM'I Sai kaga kawai mutun yaki zuwa
massallaci, Yayi zaune yana sallah a gida.
6-SATA
7-CHIN MUTUNCI
8-KARYA wadda yanzu ta zama kamar ado a
tsakanin mutane musamman matasa.
9-KARKATUWA ZUWA GA DUNIYA DA KIN
LAHIRA.
10-GABATAR DA SON DUNIYA BISA GA TA
LAHIRA.
11-CUTAR ZUCIYA cutar zuciya tana da fadi da
kuma yawa ga misalan ta kamar haka
-GIRMAN KAI Wanda hausawa ke cewa rawanin
tsiya ''DUK MAI GIRMAN KAI DAI DAI DA
KWAYAR ZAIRA BAYA SHIGA ALJANNAH''
-HASSADA Wadda itama kanta yanzu ta zama
ruwan dare, Da zarar wani yaga kafara samun
wani abun hannu to shikenan kyashi da hassada,
Zasu fara biyo baya.
-JI DA KAI
-YAUDARA
-MAKIRCI
-ALGUSSU
-KIN ABUNDA ALLAH KESO
-SON ABUNDA ALLAH BAYASO
Ranar kiyama Kudi da yaya basu da tasiri kamar
yadda Qur'ani ke cewa.
12-SABAMA IYAYE A wannan lokachin
musamman matasa, Suna sabawa iyayen su
wanda iyaye sune suka rene su, Suka bada
kudaden su wajen samar wa yayan su da ilmi,
Amma da zarar sun girma sai su fara wulakanta
su, Har wata rana zakaji iyaye na bidar yayan
alhali suna cikin garin, Matasa yakamata muji
tsoron Hadisi daga manzo tsira na cewa
''ALJANNAR MU NA KARKASHIN KAFAFUN
MAHAIFAN MU''
13-YANKE ZUMUNTA A wannan zamanin yanke
zumunta yana da matuqar yawa a tsakanin
al'umma, Zakaga wa da qane uwa daya uba
daya, Ko kuma uba daya ko uwa daya, Ko kuma
wata dangantaka ta jini suna gaba da juna babu
magana a tsakani, Wanda haka na jagoranta
zuwa ga mummunar makoma, Da kuma zuwa
Jahannama, ALLAH Ya karemu ALLAH
Madaukakin sarki na cewa A cikin aya mai
matukar ban tsoro ''KUJI TSORON YININ DA ZA'A
MAIDA KU WAJEN ALLAH ZA'A CIKAWA WA
KOWA DA ABUNDA YA AIKATA BAZA'A ZALUNCI
KOWA BA''
Daga karshe muna rokon ALLAH Ya gafartamana,
Ya yafe mana, Yayi mana rahama, Ya ALLAH
Muna tuwasulli da wannan aiki daya biya mana
bukatun mu, Ya gafarta ma mamatan mu, Ya
rage mana zafin nan na sama da kasa dana
Aljihu, Ya ALLAH Ka yiwa jagororin linzami ka
daukaka musulunci da musulmai, Ka kara
kasqanta kafurci da kafurai, Ya ALLAH Ka kawo
ma musulman kasar Somalia mafita akan bala'in
yunwar dake damuwar su.
ALHAMDULILLAH

©®IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA
25/Jimada Akhair/1438
24/03/2017.

HUDUBAH MAI TAKEN WATAN SHA'ABAN

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #WATAN SHA'ABAN
Godiya ta tabbata ga ALLAH madaukakin sarki,
Muna gode masa, Muna neman taimakon sa,
Muna kara gode masa da baiwar bamu Haske
(Qur'ani) daga garesa,
Na shaida annabi Muhammadu bawan ALLAH Ne
kuma manzo sane, Da iyalan sa da sahabbansa
da dukan wadanda suka biyo bayansu da
kyautatawa,
Yan uwa musulmi yau Khudbar mu zatayi
magana ne akan Watan sha'aban falalar sa da
kuma ayyukan da'ake bukata a aikata, Da kuma
wadanda yakamata a kaura cewa,
Watan sha'aban daya ne daga cikin watanin
musulunci, Kuma wata ne mai daraja, Wata ne
wanda ALLAH Yahada ya kasance kusa da watan
Ramadana mai alfarma!
Manzo tsira S.A.W Yana cewa ''LALLAI ALLAH
MADAUKAKIN SARKI YANA ZUBA WATA BAIWA
WATA NI'IMA A KOWANE WATA DAN HAKA MU
TASHI MU NEMETA A WATAN''
Yaku yan uwa musulmi Wannan hadisin mai
daraja yana koyar damu abubuwa guda biyu
kamar haka
1-Muyi kokari mu dinga rokon ALLAH Da dagewa
wajen bauta masa, Domin dacewa da lokachin da
ALLAH Ke raba wannan ni'imar,
Manzo S.A.W Yana yawaita azumin nafila a cikin
wannan wata mai daraja na Sha'aban! Har ma
Aisha R.A Tana cewa ''"KAI KACE YANA
AZUMTAR WANNAN WATAN NE BAKI DAYA
"" (Saboda yadda yakasance yana azumtar
wannan watan)!
Yan uwa musulmi yawaita azumtar wannan
watan zai sa dan Adam yaji sauki wajen yin
azumin farilla (Ramadana)!
2-Kowane bawa ya lizimci rokon ALLAH Kowane
lokachi, Dan dacewa da wannan lokachin, Dan
samun ingantuwar rayuwa mai albarka, Muna
Ya ALLAH Ya amintar damu tare da ruhin mu, Ya
kuma yarda damu Ameen!
A wani hadisi wanda Usama ya ruwaito yana
nuna mana muhimmancin dake tattare da azumi
a cikin wannan watan na sha'aban! Hadisin na
cewa "USAMA YANA CEWA YA MANZO ALLAH
S.A.W NAGA KANA YAWAITA AZUMI A WANNAN
WATAN (SHA'ABAN) SAI MANZO S.A.W YACE
EH NAGA MUTANE NA QIN AYYUKA A CIKIN
WATAN GASHI KUMA ANA DAGA AYYUKAN BAYI
A WATAN DAN HAKA NIKEYI DAN A DAGA
AYYUKANA AKWAI AZUMI A CIKI"
Yan uwa musulmi muyi kokari mu gyara zukatan
mu, Mu gyara ayyukan mu, Mu gyara taraiyar mu
ta yau da kullun!
Yaku yan uwa musulmi akwai wasu abubuwa
dake bijirowa a cikin addinin marar sa asali,
Wadanda shedar ke kawo mana, Daga cikin
akwai, Yana sanya mutane azumi a watan daya
gabata (Rajab), Wanda babu wani nassi
ingantacce dake magana akan haka,
Yan uwa musulmi wannan watan sunansa
Sha'aban larabawa sun kasance suna yawaita
ayyuka a ciki kama daga noma, Fatauci da kuma
komawa cikin yaqi, Saboda basu yaki a cikin
watan daya gabata!
Koda addinin musulunci yazo sai ya maida watan
sha'aban watan aiki, Amma na azumi,
Magabata na kiran wannan watan da suna watan
Qira'a, Ko kuma watan karatu, Saboda tanadi da
shiryawa zuwa watan Ramadan
Idan kai mai Qira'a ne ko tafsis yakamata kaci
gaba da yin gwaji karatun ka dan zuwan
Ramadana,
Yan uwa musulmi mu gyara bitar mu, Da tafsir
idan kai mai tafsir ne!
Ya ALLAH Ya gwada mana zuwan sa lafiya,
Watan sha'aban wata ne mai daraja kamar
manzo s.a.w yake cewa "WATAN SHA'ABAN
IDAN YAYI ALLAH NA GAFATARWA MUTANE
DUKA IN BANDA MAI GABA DA MAI SHIRKA"
Yan uwa musulmi kunji fa illar take tattare da
Shirka da kuma gaba, Dam haka duk mai shirka
ko gaba yakamata yayi gaugwar tuba,
Kada mu bari wannan garaba sar mai tarin yawa,
Mu gyara ayyukan mu ta hanyar bin abunda
musulunci yazo daci sau da qafa, Mu kiyaye
bidi'a kada muyi wa shedan biyyaya,
Akwai wasu karyayyaki da wai akwai wasu
sallalo da zikirai, Da wai akeyi a cikin wannan ,
Wanda wannan baida asali a musulunci!
Hanyoyi qalilan da aka amince a aikata a wannan
watan sune
-Tsayuwa a tauhidi
-Azumin nafila
-Yawaita rokon ALLAH
Yaku yan uwa musulmi mu fadawa iyalan mu, Da
yayan mu su sani cewa su ranka dukan azumi na
ramadana wanda ake bin su,
Dukkan wadanda keda matsala kama daga
matafiya, Mai jego, Mai haila da kuma marar sa
lafiya, Dasu ranka wadannan azumin da ake biyar
su, Domin akwai hadari ALLAH Yasamu bawa ana
binsa bashin azumi ga kuma wani ya taho,
Yaku yan uwa musulmi mu kiyaye daukar azumi
kafin kowa yadauka, Domin akwai masu daukar
azumi kafin kwana daya ko biyu, Wai da gudun
idan an samu matsalar lissafi bata shafe su ba,
To yakamata su sani cewa manzo s.a.w yana
cewa "DUK WANDA YAYI AZUMI YANA SHAKKA
YA SA6AMA BABBAN QASEEM S.A.W" Kunga
dole ne a dauka tare kuma a aje tare,
Hakama wani hadisin na cewa "AZUMIN DA
ALLAH KE KARBA SHINE WANDA AKA DAUKA
TARE KUMA AKA AJE TARE"
Musulmi kada muyi rigima, Ko bijerewa umarnin
shuwagabanin mu, Koda an samu karin bai wuce
kwana daya, Kuma akwai hadisin dake bayani kan
haka manzo s.a.w yana cewa "IDAN KUNGA
WATA KU DAUKI AZUMI IDAN KUKA DIBA BAKU
GANSA BA TO ANRUFE MAKU SHI TO KU CIKA
TALATIN"
Kungani yan uwa musulmi akwai umarni daga
manzo s.a.w! dan haka muyi biyayya ga
shuwagabanin mu dan tsira gobe kiyama,
Ya ALLAH Kabamu lafiya da zama lafiya, Kayiwa
shuwagabanin mu jagoranci, Kayi mana maganin
zafi na sama da kasa dan aljihu, Ka biya mana
bukatun mu.
ALHAMDULILLAH

©®IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA
08/Sha'aban/1438
05/05/2017.