Saturday, 30 December 2017

YAR UWA KINASON SHIGA ALJANNA???

*YAR UWA KINASON SHIGA ALJANNA???!!!*

*KI KIYAYE DOKOKIN ALLAH!*

```Hadisi ya tabbata daga Abi Hurairah R.A yace; Manzon Allah s.a.w yace: "Mutane guda biyu yan wutane, ban taba ganinsu ba!(babu irin wadannan mutanen a lokacin manzon Allah s.a.w).
Na farko: Wasu mutane ne wadanda a hannunsu akwai bulala, kamar bindin shanuwa, suna bugun mutane da wannan bulalar,(malamai sunyi fassara biyu, na farko sukace ana nufin azzaluman shuwagabanni, na biyu sukace yan fashi da makami da duk wani mai zalunci). Annabi yace suna daga cikin yan wuta.

Na biyu: sune yan mata wadanda suna sanye da tufafi amma a hakikanin gaskiya tsirara suke! Saboda tufafin bai rufe abunda akeson ya rufe ba(wato suna sanya tufafi Wanda ke bayyanar da tsiraicinsu) kamar hijaba dai gyale na zamani irinsu; show me your back, show me your breast, show me your chest, ustazu baida rabo, baba na balaga da sauransu, wannan duk haramun ne a musulunci!

Annabi ya cigaba da cewa karkatattu ne, kuma suna karkatar da wasu( wato masu ketare abunda shari'ah ta gindaya musu, suna ketare iyakokin Allah, kuma suna koyar da wasu matan irin wadannan dabi'u nasu.
Kawunansu kamar tozon rakumi ne Wanda yake karkatacce(ma'ana suna tara gashi sosai, sai su kulleshi wuri daya, a turashi gefe guda! A yanzu ka iya cewa a cuci maza da sukeyi).
Ba nan matsalar take ba, irin wadancan mutane Annabi Muhammad s.a.w yace ba zasu shiga Aljanna ba sannan baza suji kamshin aljannar ba,  shi kuwa kamshin aljanna ana jinsa daga Nisan wuri kaza zuwa kaza, a wata ruwayar Nisan tafiyar shekara dari biyar.
[Muslim ya ruwaito]

Yar uwa kinason shiga aljanna???

Na roke ki don girman Allah ki ajiye wayewar turawa ki rungumi addininki na musulunci.
Wallahi ina jin zafi a duk lokacin da naga mata suna wata shiga ta fitsara, hankali na na tashi kwarai.

Yar uwa Allah ya gafarta miki, kada ki yarda shaidan ya rinjayeki har ya kaiki ga halaka!
Soyayya da kauna da son mu gudu tare mu tsira tare shine yasa na rubuta wannan takaitacciyar nasiha.

ALLAH YA KARA SHIRYA MANA YAN UWANMU MATA A DUK INDA SUKE A FADIN DUNIYA.


DAN UWANKU A MUSULUNCI.

BABAN_SINAN```
+2348064734911

أقوال العلماء في الرفضة.

أقوال العلماء في الرافضة.

◀ قال ابن تيمية - رحمه الله -:
قال القاضي : ومن قذف عائشة رضي الله عنها بما برأها الله منه كفر بلا خلاف .

【الصارم المسلول【١٠٦٦/٣】
____________________________
◀ قال شيخ الإسلام ابن تيمية - رحمه الله -:
"الرافضة حمير اليهود يركبون عليهم في كل فتنة".

【منهاج السنة【20/ 21-1】
____________________________
◀ قال ابن تيمية - رحمه الله - :
وقال أبو حاتم : حدثنا حرملة قال :
سمعت الشافعي يقول : لم أرَ أحداً أشهد بالزور من الرافضة.

【منهـاج السنـة【٦٠/١】
____________________________
قال ابن تيمية - رحمه الله -:
النصارى الذين قاتلهم المسلمون بالشام كانت الرافضة من أعظم أعوانهم .
【المنهـاج【٣٧٨/٣】
____________________________
◀ قال شيخ الإسلام ابن تيمية - رحمه الله -:
" الرافضة من أجهل الناس وأضلهم كما أن النصارى من أجهل الناس. والرافضة من أخبث الناس كما أن اليهود من أخبث الناس ففيهم نوع من ضلال النصارى ونوع من خبث اليهود ".

【منهـاج السنـة【2/65】
____________________________
◀ قال شيخ الإسلام ابن تيمية - رحمه الله -:
" الرافضة ...أعظم عباداتهم عندهم: لعن المسلمين من أولياء الله مستقدمهم ومستأخرهم ".

【مجموع الفتاوى【٢٨/ ٤٨٨】
____________________________
◀ قال ابن القيم - رحمه الله -:
"ولقد أصبح هؤلاء الشيعة عاراً على بني آدم يسخر منهم كل عاقل".

【المنار المنيف【صـ152】
____________________________
◀ قال الإمام أحمد بن حنبل -رحمه الله -:
ليست الرافضة من الإسلام في شيء.

【طبقات الحنابلة【جـ١صـ٣٢】
____________________________
◀ قال الإمام أحمد بن حنبل - رحمه الله -:
من شتم أصحاب النبي ﷺ لا نأمن أن يكون قد مرق عن الدين.

【السنـة للخـلال【٧٧٩】
____________________________
◀ قال الامام مالك - رحمه الله -:
" الذي يشتم أصحاب رسول الله ليس له سهم -أو قال نصيب - في الإسلام ".

【الإبانـة الصغـرى【ص123】
____________________________
◀ قال أشهب - رحمه الله -:
سئل مالك عن الرافضة فقال : ﻻ تكلمهم ولا ترو عنهم فإنهم يكذبون.

【منهـاج السنـة【60/1】
____________________________
سئل شيخ الإسلام - رحمه الله -:
هل الشيعة من الضالين؟

فأجاب:
"وهل يوجد أضلّ من قوم يعادون السابقين الأولين من المهاجرين والأنصار، ويوالون الكفار والمنافقين".

وقال - رحمه الله -:
(الرافضة ليس لهم سعي إلا في هدم الإسلام ونقض عراه وإفساد قواعده)"

وقال عن الرافضة:
"دائماً يوالون الكفار من المشركين واليهود والنصارى ويعاونونهم على قتال المسلمين ومعاداتهم"
المنهاج 3/378.
____________________________
قال شيخ الإسلام ابن تيميّة - رحمه الله -:
"الرافضة هم أصل كل فتنةٍ وبليَّه، وكثير من السيوف التي سُلَّت على المسلمين إنما كانت من جهتهم".
المنهاج6/370.

وقال:
"الذي ابتدع دين الرافضة[ابن سبأ] كان زنديقاً ملحداً عدواً للإسلامِ وأهله".
منهاج السنّة4/362.
_______

🔘🔘🔘🔘🔘🔘🔘
للاشتراك في مجموعة _*على منهاج النبوة*_ واتساب إرسال الإسم الى
+249966945085

للاشتراك بقناة على منهاج النبوة على التلغرام

https://telegram.me/minhaj7

Friday, 29 December 2017

HUDUBAR JUMA'AH MAI TAKEN; MUHIMMANCIN SALLAR DARE

FASSARAR KHUDBAR JUMU'AH DAGA MASJID ABI HURAIRA AREA 2 TSAFE JIHAR ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

Bayan mukaddimah.....

Yan uwa musulmi masu albarka yau khudbar mu zata yi magana ne game da #MUHIMMANCIN_SALLAR_DARE (kiyamul laili)

Yan uwa musulmi a makon da ya gabata munyi khuduba ne game da sallar nafila..

To yau in sha Allah Zamu yi magana ne game da Sallar Dare wato kiyamul laili.

Hakika Allah ya yabi masu yin sallar dare a cikin suratul sajadah, "ALLAH ya kan rokon sa kuma suna ciyar da abunda muka basu,  Suna tashi sallar dare,  suna da makoma ta kwarai"

Hakika saboda kaunar mu da Allah yake yi  ya bamu damar aikata ibadu kala kala har ma yakan bamu lada idan mun aikata.

Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Mafificiyar sallah itace sallar nafila bayan ta sai sallar dare"

Hakama Manzo sallal lahu alaihi wassalam yana cewa "Sallar da Allah yafi so itace sallar dare"

Yan uwa musulmi masu albarka lallai wannan sallar wato sallar dare tana karawa ihlasi.

Hakika tsayuwa cikin dare yana karawa bawa tsoron Allah da natsuwa, Hakama duk ranar da dan Adam yayi sallah to zaiji natsuwa da kwanciyar hankali.

Wata rana Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace ma sahabin sa "In fada maka wata hanyar alkhairi??
Sai sahabin yace eh, Sai Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace 'Ka yawaita azumin nafila, Da sadaqah domin sadaqah tana cinye zunubai kamar yadda ruwa suke kashe wuta sai kuma ka lizimci sallar dare"

Yan uwa musulmi masu albarka muhimmancin sallar dare baya misaltuwa, Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "ALLAH yayi rahama ga wanda ya tashi yayi sallar dare"

Hakika yan uwa musulmi sallar dare tana cikin salloli masu karawa dan Adam ihklas.

Manzo sallal lahu alaihi wassalam shine baban abun koyi garemu baki daya, Hakika Manzo sallal lahu alaihi wassalam ya kasance yana tsayuwar dare har kafasun sa su fara tsagewa har Aisha radiyyallahu anha tace masa miyasa kana Manzo Allah kake Ibadah kamar haka??

Sai Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace Shin bazan zamo bawa mai godiya ba??

Yan uwa musulmi masu albarka hakika yawan yin sallar dare yana kauda bala'oi da musibuh.

Sallar Dare tana gyara halaye kuma tana gyara halaye.

Ibn hajr asqalani yace 'Ita sallar dare tana wanke zukata'

Saboda muhimmancin sallar dare Manzo sallal lahu alaihi wassalam ya hore mu da yin sallar dare inda yake cewa "NA hore Ku da sallar dare domin tana share zukata"

Hakika sallar dare tana kara lafiya da kwarin jiki,

Ina wadanda basu da lafiya likita yace sai sun rika motsa jiki duk safiya???

To ga exercise daga likitan likitoci Manzo sallal lahu alaihi wassalam idan har ka tsarkake niya to hakika Allah zai baka lafiya da yardar sa.

Ibn Salam ya ruwaito daga cewa Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Ku yada sallama a tsakanin ku Ku raba Sadakar abinci Ku sada zumunta kuyi sallar dare"

Duk mai kokarin sallar dare Allah zai haska zuciyar sa....

Wata rana Manzo sallal lahu alaihi wassalam yana baiwa sahabbai labari cewa "A cikin aljannah akwai wasu benaye masu tsawo ana ganin abunda ke ciki saboda tsabar hasken su a wata ruwayar har matan da suke ciki ya kwatanta, Sai wani mutanen karkara yace ya Manzo Allah wake da wadannan benayen??
Sai Manzo Allah yace na wadanda suka iya magana ne (Magana mai kyau Sadaka ce) da wanda ya sada zumunci da wanda ya yawaita azumi da wanda ya lizimci sallar dare "

ALLAH Ya umarci Manzo sallal lahu alaihi wassalam ya tashi yayi sallar dare" KA TASHI KAYI SALLAR DARE KA ROKI UBANGIJIN KA "

Manzo sallal lahu lahu alaihi yayi addu'a ga wanda ya tada iyalinsa suka yi sallar dare.

Idan mata ta tashi zatayi to tana iya tada mijinta Shima idan bai tashi ba tana iya yayyafa masa ruwa amma idan babu matsala 😁

Yan uwa musulmi masu albarka saboda muhimmancin sallar dare Umar bn Khaddab ya kasance yana tada iyalinsa suyi sallah a karshen dare.

Hakika ALLAH yana sauka a sulisin dare a saman duniyar nan yana cewa "INA MASU NEMAN GAFARA INYI MASU INA MASU NEMAN BIYAN BUKATA IN BIYA MASHI??"

Yan uwa musulmi a yanzu mun bar sallar dare sai a lokachin azumin ramadana.

Idan baka iya tashi da dare to kana iya yin sallar ka bayan isha'i.

Yan uwa musulmi lokachin da yakamata muyi sallar shine misalin karfe 2,3,4 domin shine sulisin dare.

A yanzu muna ganin yadda a duniyance kowa yana neman hanyar rayuwa, Kama daga bidar kudi da sauran su.

Ita lahira babu batun kudi ko wani abu hakika yakamata mu maida hankali dan lahirar mu.

Lallai kada mu kuskura shaidan yayi tasiri garemu.

Mai hankali ne wanda keyi lahirar sa tanadi kafin yaje.

ALLAH Ka taimakemu da taimakon ka ya ubangiji ka yafe mana kurakuren mu.
Ya Allah ka biya mana bukatun mu kayi rahama ga mamatan mu ya amintar damu daga abunda muke tsoro.

(Dan Adam ajizi ne Allah ka gafarta mana abunda muka yi kuskure)

©®Ibrahim Rabilu Tsafe  Alzamfari. 07064282182
Jumu'ah 10-Rabi'ul akheer-1439
29 Friday -December-2017 AB

Sunday, 24 December 2017

AN GABATAR DA DAURA KASHI NA FARKO MAI TAKEN; BAYYANA KIRKIRARRUN KARYA DA AKE JINGINAWA IBN TAIMIYYA AKAN HALASCIN MAULUDI.

🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌
*MASJID ABU-HURAIRAH YAR YARA TSAFE*
🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌

```AN GABATAR DA DAURA KASHI NA FARKO MAI TAKEN; BAYYANA KIRKIRARRUN KARAI-RAYI DA AKA JINGINA GA SHEIKHUL ISLAM IBN TAIMIYYA AKAN HALASCIN MAULUDI...

   Daurar wadda Sheikh Sani Liman (ABU HURAIRAH) Tsafe ya gabatar,  bayan Malam yayi khudubatul haaja, yayi sallama ga Yan uwa musulmai da suka taru a wajen.

  Sheikh sani Liman ya cigaba da cewa; abunda ya hada mu a wannan waje shine domin mu tattauna abunda ya shafi bukukuwan maulidi, muna yima Yan uwa musulmi maraba da karba wannan kira da sukayi, suka nuna cewa su lallai su mazajen sunnah ne, masu jira ace Sunnah tayi kira domin su amsa kiran.

  Sheikh Sani ya cigaba da cewa; Yan uwa kafin mu shiga cikin wannan littafin akwai wata shimfida da nikeson in gabatar, domin ta zamo mana haske a tafiyarmu ta Sunnah...

   Yan uwa musulmi ahlus-sunnah da muka taru a wannan masallaci bisa wannan muna saba ya kamata mu San cewa shi Ahlus-sunnah duk inda ya samu kansa to wajibi ne gareshi yayi fada da Bidi'ah!

Sheikh yace, shi fada da Bidi'ah ana yinsa ne ta hanyoyi guda biyu.

*HANYA TA FARKO:*
Fadakar da al'umma akan Bidi'ah a kowane lokaci, a kowane zamani, yadda dan Bidi'ah baiji kunyar jajircewa wajen dabbaka bidi'ashi ba, toh ai mu yafi cancanta ace mun jajirce wajen tabbatar da Sunnah, kada mu dauka cewa bidi'ar mauludi ita kadai ce zamu tsaya akanta! A'a Na daga cikin bidi'oin da ya kamata muyi fada dasu; Fadar ''SADAKHALLAHUL-AZEEM" bayan kammala karatun Qur'ani! Wannan Bidi'ah ne!!!   Na gaba shine; Fadar "AMIIN WA'ALAIKUMUS-SALAM" a wajen maida sallama, kara AMIIN Bidi'ah ne!!! da wasu daga cikin bidi'oin da basu da bambanci da bidi'ar mauludi.

Sheikh Liman yace ya kamata mu zauna mu zakulo wadannan bidi'oin domin a bayyanawa al'umma, kamar yadda babban Malami Sheikh Usman bin fodiyo ya rubuta littafi akan irin wadannan bidi'oin.

Sheikh Sani Liman ya cigaba da cewa; ba wai dole sai a irin wannan zaman bane zamu rika yakar Bidi'ah! Muna da masallatai, da makarantun islamiyyu da sauran wurare, idan ya zamana cewa ana yima bidi'ah tsirara a irin wadannan wurare a koda yaushe, babu shakka ma'abota Bidi'ah zasu ji tsoron  bayyana bidi'arsu, kuma zasu rikice.

*HANYA TA BIYU:*
hanya ta biyu da ake yakar bidi'ah shine riko da Sunnah, da dabbaka Sunnah, saboda idan Ahlus-sunnah mukayi rauni wurin riko da Sunnar Manzon Allah s.a.w, bamu koyi dashi a wajen maganganunmu da mu'amalarmu da wajen sutura da kasuwanci da sauransu, toh an samu matsala!  Ashe kenan yana daya daga cikin hanyoyin fada da bidi'ah raya Sunnah, saboda Annabi ya kira raya Sunnah a matsayin raya addini ne, saboda haka ya zama wajibi akan Ahlus-sunnah ya raya Sunnah! Abar jin kunyar aje gemu ko dage wando da sauransu.

Sheikh Liman yace, wannan ita ce wasiyya ta gareku...


   Sai Malam ya shilla akan maganar abunda ya taramu a wajen, Malam ya sukwane akan maganar bidi'ah, har ya kawo hadissai dake nuna cewa wajibi ne mu kyamaci bidi'ah, sannan ya kawo mana ayoyi dake nuna wajabcin biyayya ga manzon Allah s.a.w, ya kuma kawo mana manyan malaman musulunci da sukayi suka akan mauludi suka ce ba addini bane.

Bayan Malam ya gama wannan jawabin sai yace kai tsaye sunan littafin da zamu karanta;
تبيين كذب المفتري بما نسب إلى شيخ الإسلام ابن تيمية من استحسان الاحتفال بالمولد النبوي صلى الله عليه وسلم.
Wanda babban malaminmu na jahar zamfara Sheikh Muhammad kabir ibn umar Al-marwy(ABU SUMAYYA) ya rubuta.

Daga nan sai sheikh Sani Liman yayi mana bayanin irin kokarin da marubucin littafin yakeyi wajen baiwa sunnar Annabi kariya, da wasu ayyukan da yake yima Sunnah, malam yayi mana bayanin marubucin littafin sosai, inda har ya fada mana wasu daga cikin littafan da ya rubuta.  Na daga cikin littafan da malamin ya rubuta wanda sheikh sani ya ambata akwai;

√ TUHUFATUL AKHYAAR, BIMA'ARIFATI MALA ASLA LAHU MINAL-AKHBAR.

√ MASHAYIKHIS-SUFIYYA YAKULUNA ALLAHU FISSAMÃ(malaman sufaye sun tabbatar da cewa Allah yana sama)

√ ITTIHAFIL MU'UMININA BIT-TAKHRIJI AHADISI BUGYATUL MUSLIMEENA.

√ AHSANUL-AQAWEEL FI ISBATIS- SUNNIYATI LUBSIS-SARAWEEL, WAR-RADDU ALA MAN ZA'AMA ANNAHU BIDI'AH(wannan raddi ne ga katon dan Bidi'ah Abduljabbar akan littafin da ya rubuta ya nuna cewa sa wando Bidi'ah ne).

√ KASHFUZ-ZUNUN FI TAFSIRI QAULIHI TA'ALA;  ﻗُﻞْ ﺑِﻔَﻀْﻞِ ﺍﻟﻠَّﻪِ ﻭَﺑِﺮَﺣْﻤَﺘِﻪِ ﻓَﺒِﺬَٰﻟِﻚَ ﻓَﻠْﻴَﻔْﺮَﺣُﻮﺍ ﻫُﻮَ ﺧَﻴْﺮٌ
ﻣِّﻤَّﺎ ﻳَﺠْﻤَﻌُﻮﻥ

Da wasu littafai kusan sha uku da Malam ya ambata kuma ya ba daliban ilimi shawarar su nemesu domin amfanuwa.
Daga nan ne Sheikh yaja burki saboda lokaci da yayi halinsa, malam yace a kashi na biyu zamu shiga cikin littafin ne kai tsaye.```

Ga masu bukatar audio Na wannan Daura suna iya garzayawa a dandalin sunnah Na darulfikr.com a folder Malam zasu sameshi a cikin muhadara insha Allahu.

Allah ya sakawa marubucin wannan littafi da Alkhairi dashi da Sheikh Sani Liman da ya zakulo littafin domin fadakar da al'umma.

Sai mun hadu a fitowa Na gaba insha Allahu.



*MASJID ABU HURAIRAH TSAFE SOCIAL MEDIA COMMITTEE*
+2348064734911

05-04-1439AH
24-12-2017AC

Friday, 22 December 2017

HUDUBAR JUMU'AH MAI TAKEN, HUKUNCIN BIKIN KIRSIMETI DA SABUWAR SHEKARA A MUSULUNCI.

FASSARAR KHUDBAR JUMU'AH DAGA MASJID ABI HURAIRA AREA 2 TSAFE JIHAR ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

Bayan mukaddimah........

Yan uwa musulmi masu albarka a yau khudbar mu zata yi magana ne game da hukuncin #BIKIN_KIRISMETI_DA_SABUWAR_SHEKARA_GA_MUSULMI

Yan uwa musulmi masu albarka mu girmama ubangiji Allah kuma mu gode masa game da ni'imar shi garemu ta musulunci, Kuma mu gode masa bisa ga alkawarin sa na kare addinin musulunci daga duk wani sharri!

Yan uwa musulmi masu albarka hakika riko da addini dole kuma wajibi haka ma dole rokon ALLAH mutun ya zama musulunci shine addinin shi har zuwa karshen rayuwar shi.

Hakika Allah madaukakin sarki ya zaba mana musulunci ya zama addinin mu kamar yadda yake fada cewa "NA ZABA MASU MUSULUNCI YA ZAMA ADDININ KU"

Hakika shi addinin musulunci ya cika kuma ya kammalo kuma ta tanadi dokoki da ka'idodi, Babu wani bangaren rayuwar mu da musulunci ya kyale, Kama daga

- mu'amula 'Musulunci ya tsara yadda za' a yi mu'amula.

-Siyasa hatta ita ma musulunci ya tsara yadda za'a yi ta a cikin tsafta.

-Ibadah tabbas musulunci ya tsara yadda za'a Ibadah baki daya.

Da sauransu.

Shi musulunci addini ne wayyaye wamda yake dai dai da kowane irin zamani, Kamar yadda Allah madaukakin sarki ke cewa "MUN SAUKAR MAKA DA LITTAFI NE DAN BAYANI GAME DA KOMAI"

Yan uwa musulmi masu albarka kada mu yadda muyi wani abu da zai kaskantar da addinin mu, Ko yaya abun yake komai yadda muke kallo shi karami!!

Yan uwa musulmi a yanzu wani abun takaici da ban tsoro dake faruwa tsakanin musulmi shine yadda zaka ga wai musulmi na bikin kirismeti, Har yana zuwa wuraren su yana taya su murna yana nishadi da annashuwa.

Har takai ga wasu jahilai daga cikin musulmi na cewa 'Ai babu banbanci tsakanin musulmi da kirista !!!

Har suna cewa ai duniya yanzu ta waye, Kai har masu cewa wai ai duk Allah ne ya saukar da musulunci da kiristanci  Subhannallah!!!

To fadin wannan maganar fa kafirci ne, Allah ne yace "ALLAH YA KAFIRTA MASU CEWA ALLAH UKU NE"

A wani Wuri kuma yace "WALLAHI ALLAH YA KAFIRTA MASU CEWA ISAH (ALAIHIS SALAM) DAN ALLAH NE!!"

ALLAH madaukakin sarki ya gargade mu da so da kaunar kafurai tun daga yahudawa na nasarawa wato kirista...

Yana cewa "YAKU WADANDA SUKAYI IMANI KADA KU RIKI  YAHUDU DA NASARA A MATSAYIN MAJIBINTA DUK WANDA YA RIKE SU (MAJIBINTA)  TO YANA TARE DASU LALLAI ALLAH BAYA SHIRYAR DA AZZALUMAI"

Hakama Allah madaukakin sarki yana kara cewa "KAI MUSULMI YAHUDU KO NASARA BASU TABA YARDA DA DA KAI HAR SAI KA ZAMO DAGA CIKIN SU (wato ka koyi dabi'unsu)"

Yan uwa musulmi ana samun wasu musulmi na zuwa wajen kafurai har suna cewa murnar haihuwar Annabi Isah Alaihis salam, Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Duk wanda yayi kama da kiristoci to yana cikin su"

Zama da kiristoci a lalura babu laifi sai dai dole ne a kiyaye duk wata alaka wadda data danganci addinin ka.

Yan uwa musulmi Ibn taimiyah yana cewa 'Abunda kiristoci keyi a addinin Annabi Isah Alaihis salam haramun ne!!!

Yan uwa musulmi masu albarka ma' abota ilmi sunyi gargadi game da taya kafurai murna.

Umar bn Khaddab khalifan Manzo sallal lahu alaihi wassalam na biyu yana cewa 'Kada musulmi su kuskura yaje wajen da kiristoci ke bukukuwan su domin Allah yana saukar da fushin sa a nan to idan musulmi yaje wurin abun na iya faruwa dashi "

Kada ka kuskura wani ya jaka ko ya rude ka cewa wai ai duk ana tare ko kuma kasa daya jama'a daya wallahi kada ko sau daya kaje wajen da kafurai ke yin bukukuwan su!

Su kafurai basu son Allah basu son Manzo sallal lahu alaihi wassalam duk abunda zasu fada maka karya ne kuma adawar ka tana cikin jinin su da rayuwar su

SABUWAR SHEKARA  (NEW YEAR)

Bayan kwana ki kuma kiristoci na bikin sabuwar shekara, Kuma abun takaici kaga musulmi na murna da annashuwa cewa sabuwar shekara ta kama!!

Har zakaga musulmi na turawa a yanar gizo cewa happy new year

Wannan abun takaici ne matuka!!

Shin musulmi sun manta da ainihin shekarar su??

Wai har ana samun musulmi wanda zaka tambaya yau naga ga watan musulunci ya kasa fada??

Wannan abun takaici ne!!!

Lallai wajibi mu fifita amfani da kwanan watan musulunci fiye da nasu, Watanni musulunci a bayyane suke kuma akwai dalilin saukar dasu Allah madaukakin sarki yana cewa "SUNA TAMBAYAR KA GAME DA JINJIRIN WATA MUN SANYA WANNAN NE DAN SANIN LOKACHIN IBADAH DA AIKIN HAJJI"

hakama madaukakin sarki na cewa "ADADIN WATANNI A WURIN ALLAH SUNE GUDA GOMA SHA BIYU AKWAI HUDU MAFI FALALA A CIKIN SU"

kenan ga manu Zamu dauki na wasu??

Amfani da watan ni kafurai sai lalura da kuma dole!!

Kada mu dauka cewa amfani da watan musulunci al'ada ne...... A'a addini ne.

Muna tawasuli da sunayen Allah dari ba daya ya shiryar damu hanya madaidaiciya ya biya bukatun mu na alkhairi.

Allah ka taimaki yan uwa musulmi dake zirin gaza ka kaskantar da yahudawa da masu goya masu Baya.

Allah ka amintar damu Kabamu lafiya d zama lafiya ya ubangiji kayi rahama ga mamatan mu.

Ya ubangiji kayi albarka da bunkasa kasashen mu da jahar mu da garin mu baki daya.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe  Alzamfari. 07064282182
Jumu'ah 2-Rabi'ul thani-1439
Friday 22-December - 2017 AB

Monday, 18 December 2017

TARIHIN RASUWAR MANYAN MUTANE, MASU DARAJA A CIKIN MUSULUNCI, WADANDA AKE YAWAN TAMBAYA A KANSU.

🗓 *TARIHIN RASUWAR MANYAN MUTANE, MASU DARAJA A CIKIN MUSULUNCI, WADANDA AKE YAWAN TAMBAYA A KANSU*




📒 ```Annabi Muhammad (salallahu alaihi wasallam) ya rasu a shekara ta 11AH

📕 Abubakar sideeq R.A shekara ta 13AH


📔 Umar bin khaddab R.A shekara ta 23AH

📙 Usman bin Affan R.A shekara ta 23AH

📘 Aliyu bn Abi dalib R.A shekara ta 40AH

📗 Aisha bintu Abubakar R.Anha  shekara ta 57AH


📕 Abdullahi bn Abbas R.A shekara ta 68AH

📔 Abdullahi bn umar R.A shekara ta  73AH

📘 Sa'eed Ibnul musayyib R.H shekara ta 94AH

📙 Umar ibn Abdulaziz R.H shekara ta 101AH

📗 Hasanul busri R.H shekara ta 110AH

📕 Abu Hanifa R.H shekara ta 150AH

📗 Malik ibn Anas R.H shekara ta 79AH

📘 Shafi'i R.H shekara ta 204AH

📕 Ibn Rahawiya R.H shekara ta 238AH

📙 Ahmad ibn Hambal R.H shekara ta 241AH

📗 Ahmad Ibn sa'eed AD-DARUMY R.H shekara ta 253AH

📘 Abdullahi Ibn Abdulrahman AD-DARUMY R.H shekara ta 255AH


📔 imamul Bukhary R.H shekara ta 256AH



📕 Imam Muslim R.H shekara ta 261AH


📗 Ibn majah R.H shekara ta 273AH



📘 Abu daud R.H shekara ta 275AH



📙 Tirmidhi R.H shekara ta 279AH

📗 Usman bin sa'eed AD-DARUMY R.H shekara ta 280AH



📗 imamun nasa'i R.H shekara ta 303AH



📔 Ibn jareer AD-DABARY R.H shekara ta 310AH

📘 Ibn khuzaimah R.H shekara ta 311AH


📕 Ibn Hibban R.H shekara ta 354AH


📙 Imamu DARAQUDUNY R.H shekara ta 385AH


📔 imam Hakim R.H shekara ta 405AH


📗 Ibn hazam R.H shekara ta 456AH


📘 BaihaQy R.H shekara ta 458AH


📕 Ibn Abdulbarr R.H shekara ta 463AH


📔 khadeebul baghadady R.H shekara ta 463AH


📗 Ibnul Araby R.H shekara ta 543AH


📘 Ibn rushid R.H shekara ta 595AH

📙 Ibnul jauzy R.H shekara ta 597AH

📔 Alkurduby(mai littafin الجامع لأحكام القرآن) R.H shekara ta 671AH


📕 Imamun-Nawawy R.H shekara ta 676AH

📗 Ibn Taimiyya R.H shekara ta 728AH

📔 Imamuz-Zahaby R.H shekara ta 748AH

📘 Ibnul kayyim R.H shekara ta 751AH


📙 Ibn Katheer R.H shekara ta 774AH


📗 Ibn Rajab R.H shekara ta 795AH


📔 Ibn Hajar AL-ASQALANY R.H shekara ta 852AH


📗 Imamus - suyudy R.H shekara ta 911AH


📘 Ameerus - san'any R.H shekara ta 1182AH



📕 Muhammad Ibn Abdulwahab R.H shekara ta 1206AH



📗 Imamush -shaukany R.H shekara ta 1250AH


📔 AL-ALUSY R.H shekara ta 1342AH


📙 Ibn Sa'ady R.H shekara ta 1376AH


📕 SHANQIDY R.H shekara ta 1393AH


📘 Ibn baz R.H shekara ta 1419AH


📗 Albany R.H shekara ta 1420AH


📔 Ibn uthaimin R.H shekara ta 1421AH

📕 Abdullahi bn Abdulrahman bn jibreen R.H shekara ta 1430AH


⭕ Ku tura ta zuwa ga daliban ilimi

⭕ Ku tura ta zuwa ga wadanda Luke kusa dasu domin mu hadu wurin amfanuwa.


FASSARAWA:
_HASHIM IBN SURAJ IBN UBA (ABU~SINAN)_```
+2348064734911

http://hashimtsamiya.blogspot.com/

atstsamawy@gmail.com

MUHADARAMUHADARA

📀📀📀📀📀📀📀📀📀
*MUSLIM UMMAH WELFARE AND DA'AWAH ASSOCIATION TSAFE*
💿💿💿💿💿💿💿💿💿


*WA'AZIN DA AKA  GUDANAR A RANAR  ASABAR  27/RABIU AUWAL/1439)*

*DAGA BAKIN SHUGABAN KWAMITIN: (MALAM IBRAHIM MUHAMMAD FILO) TSAFE*

*MAUDU'IN KARATUN SHINE:--- WAJABCIN NEMAN ILMI DA AIKI DA SHI*

Shiga Link dake kasa domin saukewa

💽💽💽💽💽💽💽💽💽💽
http://darulfikr.com/s/37564

*AYI SAURARO LAFIYA CIKIN SAUTI MAI KYAU*

Kasance da darulfikr.com a koda yaushe, domin samun KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH.

#ABBAN_SINAN
+2348064734911

Friday, 15 December 2017

HUDUBAR JUMA'AH MAI TAKEN; MUHIMMANCIN NAFILA

FASSARAR KHUDBAR JUMU'AH   DAGA MASJID ABI HURAIRAH DAKE TSAFE ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A wannan makon  limam Sani Abi hurairah Tsafe ya gabatar da khudbar ne akan #MUHIMMANCIN_NAFILAH

Bayan mukaddimah......

Yan uwa musulmi masu albarka hakika gaskiyar zance shine Alqur'ani Mai tsarki, Mafi kyawun shiriya itace shiriya ta Annabi Muhammadu sallal lahu alaihi wassalam, Mafi sharrin ayyuka shine kirkirar abu ga addini.

Yan uwa musulmi masu albarka ina maku Nasiha tare da ni kaina da muji tsoron ALLAH domin jin tsoron ALLAH shine jagora ga rayuwar mu, ALLAH yana fada cikin suratul kasas cewa "WANNAN GIDAN NA LAHIRA MU SANYA SHINE GA MASU TSORON ALLAH HAKIKA AQIBA MAI KYAU ITA KUWA AQIBA MAI KYAU TANA GA MASU TSORON ALLAH"

Saboda kaunar da ALLAH keyi mana ya sanya mana abubuwa da Zamu amfana dasu, kamar nafilfili da sauransu,  Nafila ta sallah tana Matukar muhimmancin ga ibada,

Yan uwa musulmi masu albarka sallah itace abunda za'a fara bincike a gobe Kiyama, Manzo sallal lahu alaihi wassalam na cewa "Farkon abunda za'a yiwa dan Adam hisabi akanshi shine sallah idan tayi kyau to dan Adam ya dace idan kuma an samu matsala sai ALLAH ya umarci mala'iku su binciki shin akwai nafila?
Idan akwai to sai ayi amfani da ita wajen cike sallar farilla"

Haka ma a azumi da zakkah sai a diba idan akwai wakafi da sauran ibadu!!

Kenan koda a wannan hadisin muka tsaya lallai zamu fahimci cewa nafila nada matukar muhimmanci.

A wajen yin ibadar sallah ana bukatar natsuwa sosai Ibn Abbas ya ruwaito yace" Sai kana da natsuwa sannan sallahr ka zata karbu "

Yan uwa musulmi masu albarka yawan yin nafila yana sa mutun yazama abokin Manzo sallal lahu alaihi wassalam a gidan aljannah

Akwai wani sahabin Manzo sallal Sallal lahu alaihi wassalam idan Annabi zai yi alwala sai sahabin ya dauki talkaman Annabi ya rike a hannunsa hakama idan Manzo sallal lahu alaihi wassalam zai yi sallah yakan tsaya har sai Annabi ya fito, Wata rana sai Manzo sallal lahu alaihi wassalam ya tambaye shi mi kake bukata inyi maka??

Sai yace ina so in zama abokin ka a gidan aljannah.....

Sai Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace to ka taimake ni da yin nafila a koda yaushe. "

Yan uwa musulmi masu albarka yawaita nafila na kara kusan tar da dan Adam ga ubangiji, ALLAH madaukakin sarki na cewa" BAWA BAZAI GUSHE YANA SUJJADAH HAR SAI NA SOSHI "

Yan uwa musulmi masu albarka yawaita yin nafila kara maka kusanci da ubangiji ALLAH

Abdullahi bn Umar ya ruwaito cewa" Kafin sallar azahar kayi raka'a 2 bayan sallar kuma kayi 2 la'asar kayi 2 bayan ta kayi 2 hakama a magrib da isha'i hakama a sallar asuba kafin ta wato sallar fajir "

Haka ma Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace" Duk wanda yake yawaita yin nafila raka'a 12 a rana ALLAH zai gina mashi gida a aljannah "

Haka ma Manzo sallal lahu alaihi wassalam yana cewa" Kuyi raka'a 2 kafin magrib ya fadi haka har sau uku amma ga wanda yake sa hali "

Haka ma Aisha radiyyallahu anha ta ruwaito cewa" Manzo sallal lahu alaihi wassalam bai taba barin nafila ba a lokachin sallar asuba ba "

Yan uwa musulmi masu albarka hadisin dake magana game da ba'a sallah bayan la'asar na nufin idan an dade da gama sallar ne.

Daga cikin nafilolin da ake bukatar yawaita aikatawa akwai sallar duha wato ita anayi ta ne da safe, Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Dan Adam yana da gabobi guda 360 ana bukatar a kullum kabada Sadaka kwatan kwacin haka sai sahabbai suka ce to idan baka da kudin bada Sadakar??  Sai Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace to ka tsaftace massallaci (kamar shara ko kuma dauke wani tsinke) koda ma ace ka gaza haka to kayi sallar duha "

Yan uwa musulmi masu albarka hakika addinin musulunci yana da Matukar dadi da kuma garabasa ga wani hadisi daga Manzo sallal lahu alaihi wassalam cewa

" Duk wanda ya fito daga gida yayi aikatawa zaije massallaci to ana rubuta mashi ladar aikin hajji da umrah "

Hakika yan uwa musulmi idan muka yawaita yin nafila za'a rubuta sunayen mu cikin illiyun

Yan uwa musulmi bayan sallar asuba yana da kyau mu rika zaunawa koda awa guda ko biyu ne Muna yin tasbih domin falalar dake ciki, Hadisi daga Manzo sallal lahu alaihi wassalam na cewa "Bayan kammala sallar asuba ka zauna har rana ta fito kana da ladar aikin hajji cikakke cikakke cikakke!!

Yan uwa musulmi dole ne mu rage yawan zama ana hira ana surutu fiye da awa guda alhali zaman baida wani amfani garemu,

Imam Muslim ya ruwaito daga Manzo sallal lahu alaihi wassalam cewa "Dayanku bazai yi alwala yana jiran sallah ba face wuta ta haramta gareshi!!"

Yan uwa musulmi kunji falala mai kyau kenan masu zuwa massallaci da Wuri suna jiran limam sun samu shiga a wannan.

Sannan kuma yan uwa musulmi yana da kyau mu yawaita yin nafila a gidajen mu domin Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace "Kada mu maida gidajen mu kamar makabartu (Domin ba'a sallah a makabarta)

Manzo sallal lahu alaihi wassalam yace" Mafificin nafila itace nafillar da akayi a gida "

Yan uwa musulmi kada mu rangwantar da kawunan mu mu kashe jikin mu da hira da surutai marar sa amfani domin wallahi akwai ranar da Zamu nemi ina ma ace Zamu yi aiki koda na kwayar zarra ne!!

Akwai falala mai yawa a cikin sallar nafila, Manzo sallal lahu alaihi wassalam "SALLAR fajir (Kafin asuba) tafi duniya da abunda ke cikin ta"


To yan uwa musulmi kunji fa......

Tabi'ai da sahabbai sun kasance idan wani yayi laifi yana zuwa yayi nafila ya roki Allah ya gafarta masa.

*Sallar nafila tana daga Darajar dan Adam a wurin ALLAH

Hakika sahabbai da Tabi'ai suna yawaita yin nafila domin tsannanin koyi da Annabi, Saboda Annabi ya karantar dasu kuma yayi a gaban su har ma ya kwadaitar da wannan ibadar.

Yawaita nafila yana kawo abubuwa kamar haka :

*Gidan mutun yana albarka

*Darajar dan Adam tana karuwa

*Yana sanya mutun yazama abokin Manzo sallal lahu alaihi wassalam a gidan aljannah.

*Nafila na zama abokiyar hira ga dan Adam a cikin kabari.

*Zai kara maka son ALLAH

*Tana maida dan Adam yazama mutanen kirki.

*Samun ladar aikin hajji da umrah

*Kankarewar Zunubai.!!

Yan uwa musulmi masu albarka a yadda duniya ta chanza a yanzu dole ne mu rungumi koyar wa Manzo sallal lahu alaihi wassalam da duk abubuwan da ya karantar damu.

ALLAH ka gafarta mana kayi mana rahama kabamu lafiya da zaman lafiya, Ya ubangiji ALLAH kayi rahama garemu ka biya mana bukatun mu ka haskaka rayuwar mu, Ameen

©®Ibrahim Rabilu Tsafe  Alzamfari. 07064282182
Jumu'ah 20-Rabi'ul auwal-1439
Friday 15-December-2017 AB

Friday, 8 December 2017

HUDUBAH MAI TAKEN LOKACIN SANYI

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A DAGA MASJID ABI HURAIRAH DAKE TSAFE ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A wannan makon limamin  Massallacin Jumu'a na Abi Hurairah dake unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na Liman'

Yayi Hudubar Sane Akan #LOKACHIN_HUNTURU

Bayan mukkaddimah........

Yan uwa musulmi masu albarka a yau Khudbar mu zatayi magana ne game da halin da muke ciki, Watau yanayi na hunturu da sanyi da kadawar iska.

Idan muka diba lokachin da muka fito na baya zamu ga cewa lallai yanayi yayi matukar chanzawa, Hakika yan uwa musulmi chanzawar lokachi wani sababi ne ga mai imani da zai kara masa imani, Da kara maida kai ga ALLAH Da jajircewa ga biyar sa!

ALLAH Madaukakin sarki cikin hikimar sa da yarda sa yana shata mana zuwan wannan lokachin duk shekara.

Ibn kaiyumul jauzi yana cewa 'Idan aka lura da yadda ALLAH juya lokutta zamu fahimci cewa akwai wata maslaha dake cikin yin hakan'

Idan da yaso sai ya barmu da lokachi daya ko zafi kawai ko sanyi kawai ko kuma ruwan sama kawai!

Yan uwa musulmi masu albarka ina maku wasiya dani da ku da muji tsoron ALLAH, Hakika da tsoron ALLAH Ne zukata ke kamuwa da natsuwa kuma ake fahimta ayoyi da manufofin ubangiji.

ALLAH Madaukakin sarki na cewa "SUNE (Masu imani) MASU DIBA YADDA MUKE JUYA AKAN LAMURA HAKIKA SUN SAMU IMANI KUMA SUNE MASU AMBATON ALLAH BA DARE BA RANA "

Hakama ALLAH S.W.T Na cewa "LALLAH JUYAWAR DARE DA YINI AYAH CE GA MASU IMANI"

Shi wannan lokachin na sanyi ALLAH Madaukakin sarki ne ya kaddaro shi da haka, Domin wuta ce keyin lumfashi!!

Ga hadisi daga Manzo s.a.w "Wata rana wuta takai kara ga ALLAH S.W.T Cewa wani sashen ta yana cin sashen ta sai ALLAH Yabata dama cewa ta rika numfashi wato taja iska (shine muke samun lokachin sanyi) sannan ta saki numfashi (shine lokachin zahi)"

Iman hasanul busariy na cewa 'ALLAH Ya tanadar da wannan lokutta ne dan tunatar damu game da kiyama, Domin idan nukaji sanyi yayi yawa sai mu tuna cewa sanyin azaba da kiyama yafi na duniya, Hakama zafi na duniya bai kai zahin kiyama ba"

Abdullahi dan Mas'ud r.a ya kasance idan sanyi yazo yana cewa 'Maraba da zuwan sanyi maraba da zuwan sanyi idan aka tambaye shi miye dalilin shi na fadar haka sai yace 'Lokachin sanyi lokachi ne da dare keda tsawo (Ana samun damar yin ibadah da kusantar ALLAH) Rana kuma batada tsawo ana yawaita azumi'

Yan uwa musulmi masu albarka lokachin hunturu yana da HUKUNCE HUKUNCEN sa..

*Yin alwala da kyau-Yazama wajibi mu kiyaye yadda muke alwala a lokachin sanyi, Domin muna sanya manya kaya kuma wajen alwala zakaga wasu saboda kaya masu nauyi basu yin alwala da kyau.

Manzo s.a.w "Yaga wasu na alwala amma basu shafawa yadda yakama sai Manzo s.a.w yace 'Boni ya tabbata ga masu alwala basu cikawa ' "

Babu laifi saboda sanyi ayi alwala da ruwan zafi wajen yin alwala.

*Ana son tuna saukin da shari'ah ta kawo mana, Ya halatta shafa sama safa ko takalma ko huffi, Idan har anyi alwala kafin a sanya safar ko takalman.

Mugira ya ruwaito hadisi kuma an ruwaito shi a sunnanin dauda cewa "Manzo s.a.w yana shafa saman khuffi amma idan yayi alwala,

Hakama wata rana Manzo s.a.w zai yi alwala sai Mugira yazo zai cire masa takalma sai Manzo s.a.w yace kabarshi domin nayi alwala kafin insa!

Larabawa na cewa lokachin sanyi namiji zahi kuma macce, Saboda yanayin karfin su ba daya ba.

A zamanin khalifan Manzo s.a.w na biyu wato Umar bn Khattab r.a yana kewa yawa cikin gari yana cewa 'Sanyi yazo sanyi makiyin mu ne dan haka mu tanadi kayan kariya kamar manya barguna da sauran kayan kariya daga sanyi'

Yaku yan uwa musulmi masu albarka, Hakika Umar r.a ya kasance yana taimakon marar sa galihu da kayan rufe jiki dan kariya daga sanyi.

Anan muna kira ga yan uwa musulmi da mu taimaki yan uwa marayu da makwabta da sauran mara sa galihu, Da kuma kula da iyali da kananan yara a tanadar masu kayan sanya kada mu barsu kamar  dabbobi domin zai iya yin illah garesu.

*Yawaita bautar ALLAH, Hunturu lokachi da dan Adam ke samun lafiya da walwala da kebantuwa daga mutane, Domin ko doguwar hirar da ake yi ragewa ake yi, Zaka fito karfe goma ka tarar babu kowa,

Dan haka sai muyi amfani da wanoan lokachin wajen bautar ALLAH ba yawan bacci ba.

*Mu rika cika alwala, Manzo s.a.w na cewa "Cika alwala ne mafi so a yanzu (Lokachin hunturu).

*Dumama jiki dan samun sauki, Sai dai yana da kyau musulmi ayi hattara sosai, Domin kada mu ajiye wuta ta rika kwana a dakunan mu.

Abul musa al'ashry ya ruwaito cewa "Wata rana ayi gobara a Madinah sai aka fadawa Manzo s.a.w sai yace 'Wannan wutar makiyar muce mu daina aje ta a dakunan mu'!!

Dan haka da zarar zamu kwanta sai mu kashe wuta a fito da ita waje,

Yan uwa musulmi mu taimaki yan uwa marar sa galihu, Mu taimaki marar kayan sanyawa.

Lallai ALLAH Na taimakon bawa, Matukar yana taimakon yan uwansa.

ALLAH Ka taimakemu da taimaka, Ka karemu da kariyar ka.

Ya ALLAH Ka biya mana bukatun mu na alkahri ka kiyaye mu kuma ka tsare mu.

Ya ubangiji kayi rahama garemu da iyayen mu.

Ya ubangiji ka zaunar damu lafiya, Ka albarka ci garin mu.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe  Alzamfari. 07064282182

Jumu'ah 19-Rabi'ul auwal-1439
Friday 18-December-2017 AB

HUDUBA MAI TAKEN TSORATARWA GAME DA RASHIN BADA ZAKKAH

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A DAGA MASJID
ABI HURAIRAH DAKE TSAFE ZAMFARA


DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE



A wannan makon limamin Massallacin Jumu'a na
Abi Hurairah dake unguwar Area2, Tsafe Sheik
Sani Na Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #TSORATARWA GA
MASU HANA # ZAKKAH
Bayan mukaddima.....
Yan uwa musulmi masu albarka, A wancan
makon daya gaba munyi bayani game da
#ZAKKAH da hukunce hukunce ta.
To a wannan makon da ikon Allah zamu yi
magana akan tsoratarwar ga halayyar ga masu
hana #ZAKKAH
Yan uwan musulmi muji tsoron Allah gaskiyar jin
tsoron sa musani yana kallo duk abubuwan da
muke aikata a kullum.
Muhimancin #ZAKKAH ba karami bane a
musulunce har Allah yahada ta tare da sallah
wurare 32 a cikin alqur'ani mai tsari,
Babban dalilin wajabta #ZAKKAH shine nuna
godiya ga Allah, Da kuma sadar da umarnin
Allah.
#ZAKKAH tana kankare talauci a tsakanin
mutane, Bada #ZAKKAH tsarkakewa ne wato
tsarkake dukiya da kuma rayuwa baki daya.
Saboda matsayin Allah ya umurci Manzon Allah
s.a.w akan ya karbo #ZAKKAH "KA ANSO
#ZAKKAH DAGA GARESU DAN ZAMA
TSARKAKEWA GARESU"
Yan uwa musulmi masu albarka, Hakika fidda
#ZAKKAH wajibi ne a musulunci kuma dole ne,
Rashin fidda #ZAKKAH yana kawo fitononi da
musibu a cikin al'ummah baki daya. Allah ya
umarce mu da fiddawa da yake cewa "KU FIDDA
DAGA ABUNDA MUKA AZURTA KU DASHI"
Rashin bada #ZAKKAH yana jawo masibu da
bala'oi kala kala!!
Nana Aisha r.a ta ruwaito daga Manzo s.a.w
cewa "Babu dukiyar da za'a tara ba'a fitar mata
da #ZAKKAH sai Allah tarwatsa ta"
Yan uwa musulmi masu albarka muna ganin
musibu da ake samu na gobara da masibu kala
kala, Hakika wannan duk daga hana #ZAKKAH
ne!
Rashin bada #ZAKKAH na kawo debe albarka ga
noma da kudi, Idan muka diba zamu ga yadda
anan garin aka noma shinkafa da farko tayi kyau
amma daga karshe wasu sun fadi warwas!
Duk fa wannan daga rashin bada #ZAKKAH da
muke yi, Manzo s.a.w na cewa "Mutane bazasu
hana #ZAKKAH ba face sai Allah ya debe
albarka ga abun su"
Hakika tsoratarwa mai karfi tazo akan masu qin
fidda #ZAKKAH har ma wani wuri a Qur'ani da
mushrikai.
Sau da yawa zakaga wami yasamu kudi da suka
kai nisabi, Ko kuma yayi noma yasamu albarka
amma sai ya rike #ZAKKAH ko kuma yabada ga
wanda yaga dama ko kuma badawa a lokachin da
yaso maimakon lokachin da yasamu.
Duk wanda yabada #ZAKKAH yadda yaga dama
malamai sunce kamar bai bada wato dashi da
wanda bai bada duk daya.
Rashin bada #ZAKKAH yana kawo musibu, Ita
kuma musiba munsan tana shafuwar har wanda
baiji ba bai gani ba, Wata qila ma tana iya wuce
wanda ya hana #ZAKKAHR Ta fada wani shi
kuma a kyale sa sai ranar kiyama!
Yan uwa musulmi masu albarka, Idan akwai
abokin ka ko dan uwanka ko wani makusancin ka
yake hana #ZAKKAH to kayi masa nasiha tare da
gargadi.
ALLAH Fa yayi mana babban gargadi (Serious
warning) game da hana #ZAKKAH
*BANI YA TABBATA MARAR BADA #ZAKKAH SU
(masu hana zakkah) MUSHRIKAI GA KIYAMA"
*MASU TARA DUKIYA #ZAKKAH DA SANMU
ZA'A JEFA SU A WUTAR JAHANNANAMA TANA
SUYA SU"
*"MASU TARA DUKIYA BASU BADA #ZAKKAH
KUMA BABU ABUNDA YASAMI DUKIYAR
WALLAHI YABAR MURNA DOMIN BALA'I CE
GARESA"
Manzo s.a.w ya fassara wannan ayar da cewa
"Allah zah maida dukiyar maciji mai baki biyu
yana saransa a wutar jahanama yana cewa 'Nine
dukiyar ka da ka hana #ZAKKAH' "
Yan uwa musulmi masu albarka Allah shirewa
duk dukiyar da aka hana #ZAKKAH albarka,
Idan muka diba matsalar tsaro da sauran
abubuwan da suka dame mu duk suna da alaqa
da kaucewa umarnin Allah.
Bayan wafatin Manzo s.a.w wasu sunce sunce
'Sun daina bada #ZAKKAH saboda Manzo s.a.w
ya rassu, Khalifan Manzo s.a.w ya yake su har
garuruwan su ya bisu ya karbo #ZAKKAH
Aliyu bn abi Thalib khalifan Manzo s.a.w ya hudu
yace 'ALLAH Baya dauke musiba sai an tuba!
Allah madaukakin sarki na cewa "DUK ABUNDA
YASAME KU TO DAGA ABUNDA KUKE
AIKATAWA NE"
Hakika ALLAH Yabamu labarin mutane da yawa
wadanda yayi wa ni'ima suka kafurce!
ALLAH Yana fada mana cikin suratul nahal cewa
"ALLAH YABUGA MISALI WATA ALKARYA DATA
KAFURCE"
Sai mu diba muga yanzu wace ni'imah ce Allah
baiyi mana ba??
Munsan labarin wani da ake kira Saba'a yadda
suka kafurce daga karshe ALLAH Kwace ni'imar
daga garesu.
Lallai ne kuma dole ne mu sadar da umarnin
ALLAH Dan samun falala da rahama wata bata
yankewa daga garesa.
Tsira da amincin Allah su tabbata ga Manzo
s.a.w da iyalansa da sahabban sa dukkan
wadanda suka biyo bayan su da kyautatawa har
zuwa ranar sakamako.
Ya Allah ka biya mana bukatun mu kayi rahama
garemu ka gafarta mana yaye mana damuwa, Ya
Allah kara albarka ga dukiyar da ake bada
#ZAKKAH ya Allah ka tarwatsa duk dukiyar da
ake hana #ZAKKAH


©®Ibrahim Rabilu Tsafe Alzamfari. 07064282182

Jumu'ah 28-Safar-1439
Friday 17-November-2017

HUDUBAH MAI TAKEN BIDI'AH

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A DAGA MASJID
ABI HURAIRAH DAKE TSAFE ZAMFARA


DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A wannan makon limamin Massallacin Jumu'a na
Abi Hurairah dake unguwar Area2, Tsafe Sheik
Sani Na Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #BIDI 'AH DA
HUKUNCIN TA A MUSLUNCHI
Bayan mukaddimah...
Yan uwa musulmi a yau Khudbar tamu zata yi
magana ne game da #BIDI'AH da kuma hukuncin
ta a musulunce!!
Yan uwa musulmi muji tsoron ALLAH Gaskiyar jin
tsoron sa, Mu sani cewa da tsoron ALLAH
Rayuwa ke gudana .
Babbar ni'imah garemu ita ce musulunci domin
musulunci shine hanya daya rak dake sada dan
Adam da ubangiji ALLAH , ALLAH Yabamu
rayuwa (Musulunci) kamar yadda ya labarta
mana cewa "YANZU WANDA YA KASANCE
MATACCE (JAHILI) ZAI YI DAI DAI DA MAI RAI
(MAI ILMI)"
Hakika akwai abubuwa wadanda ke ruguza addini
da dama,Babba Daga ciki shine bidi'ah!
Ita bakwai ne kawo ita bidi'ar,
1-Son rai, Shi son rai shine babban jagora ga
qago bidi'ah a cikin addini, ALLAH Madaukakin
sarki kuma ya gargadi masu son da yake cewa
"BABU WANDA YAFI KOWA ZAMA BATACCE SAI
WANDA KE BIN SON RAI".
2-JAHILCI, Tabbas jahilci ya taka gagarumar
rawa a wajen qago bidi'ah a cikin musulunci,
ALLAH Madaukakin sarki na cewa "MAFI YAWAN
MUTANEN DUNIYA JAHILAI NE"
3-Kau da kai daga karbar gaskiya, Tabbas kauda
kai daga karbar gaskiya yana matukar kai dan
Adam ga kirkiro bidi'ah, Ita kau gaskiya duk
wanda ya karbe ta baya tabewa kamar yadda
madaukakin sarki ke cewa "DUK WANDA
SHARI'A TA BAYA TABEWA DUK WANDA YABI
SON RANSA ZA'A TABAR DASHI KUMA ZA'A
TADA SHI MAKAHO"
4-Nisantar masu ilmi, Tabbas nisantar masu ilmi
na fadin gaskiya da kuma takama da jahilci na
kawo kago bidi'ah a addini, Duk abunda mutun
bai sani yakamata yayi ya tambaya amma sai ya
kiya, ALLAH Kuma na cewa "KU TAMBAYI
MA'ABOTA ILMI IDAN BAKU SANI BA"
5- Jiji da kah da son ra'ayi, Hakika ji da kai yana
kawo mutun ya fadawa bidi'a ko kuma ya kirkiro
ta,
6-Son duniya, Tabbas masu mugun son duniya
suna kirkirar bidi'ah su kawo ta a musulunci,
ALLAH Kuma na cewa "SUN ZABI DUNIYA A
BISA LAHIRA " Wani wuri kuma yana cewa "SUN
ZABI RAYUWAR DUNIYA BISA GA TA LAHIRA"
Abubuwa biyu ne bidi'ah take...
1-Bidi'ah ta magana wadanda suke magana ta
izgili da sunan addini kamar mu'utazilawa da yan
Shi'ah.
2-Bidi'ah ta aiki, Kamar bautawa ALLAH Da
shari'ar da bai umarta ba, Ko kuma kari a cikin
ibadah, Misali wani yace maka 'Assalamu
Alaikum' to sai kaji wurin ansawa ance 'Ameen
'Wa alaikum salam anan cewa Ameen bidi'ah duk
da kalmar amin kalma ce mai kyau amma dai
sunnah bata karantar da haka ba, Akwai kara
wani abu wajen yin sallah da sauran su.
Manzo s.a.w ya koyar damu yadda ake yin Zikirai
kowane iri ya koyar damu na safe na rana na
yammah na dare dana komai,
Sannan akwai bidi'ar kebance wani lokachi
wanda shari'ah bata kebe ba dan yin ibadah,
Wannan baya cikin tsarin musulunci.
Hukuncin #BIDI'AH shine tana rushe aiki baki
daya.
Manzo s.a.w na cewa "Mafi sharrin ayyuka shine
kirkiro wani abu cikin addini"
Wata rana Umar bn Abdul'aziz r.a ya fito sai yaga
wani tsoho mai gudun duniya mai tsoron ALLAH
Ya yawaita ibadah amma kirista ne!!
Dan haka sai ya koma gida yayi ta kuka da aka
tambaye shi miye dalilin kukansa sai yace ganin
wannan ya tuna mashi da ayar nan dake cewa
"RANAR DA ZA'A
KIFE FUSKAM SU A CIKIN WUTA"
Ita #BIDI'AH tana kawo kasala ga aikata Sunnah!
Imam hasanul busary na cewa 'ALLAH Baya
karbar ibadun mai bidi'ah sai almajiransa suka ce
saboda mi? sai yace yana da hujja daga hadisin
dake cewa "ALLAH Ya tsinewa mai yin bidi'ah"
Muna rokon ALLAH Ya gafarta mana yayi mana
rahama, Ya karemu daga aikata bidi'ah yayi
rahama garemuda iyayen mu, Ya biya bukatun
mu.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe Alzamfari. 07064282182

Jumu'ah 12-Rabi'ul auwal-1439
Friday 01-December-2017

HUDUBA MAI TAKEN HARAMCIN SATA A MUSULUNCI

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A DAGA MASJID
ABI HURAIRAH DAKE TSAFE ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A wannan makon limamin Massallacin Jumu'a na
Abi Hurairah dake unguwar Area2, Tsafe Sheik
Sani Na Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #SATA
Godiya ta tabbata ga ALLAH S.W.T Wanda yayi
halitta ya kuma dai dai ta halittar kamar yadda
yake bukata!
Na shaida Annabi Muhammad s.a.w manzo
ALLAH, ALLAH Kayi salati da taslimi ka kara
aminci garesa, da iyalansa da sahabai da dukkan
wadanda suka biyo bayan shi da kyautatawa har
zuwa ranar sakamako.
Yan uwa musulmi masu albarka yau Khudbar
tamu zatayi magana ne kan wata dabi'a wadda
zamu iya cewa ta zama ruwan dare a rayuwar
mu, Wannan dabi'ar ita ce #SATA
Yan uwa musulmi ina maku wasiya na ni kaina da
muji tsoron ALLAH, Kamar yadda ALLAH Da
kansa ya umarce mu cewa "KUJI TSORON WANI
YINI DA ZA'A MAIDA KU GA ALLAH SANNAN
ZA'A SAKAWA KOWACE RAI DA ABUNDA TA
AIKATA KUMA BAZA'A ZALUNCE TA BA"
Su kudi ALLAH Madaukakin sarki ne ya saukar da
su daga sama dan amfanin mu, Dan mu gudanar
da rayuwar mu ta yau da kullum da kuma
gudanar da addini... ALLAH S.W.T Ya gargade
mu game da cin dukiya wadda ba tamu ba da
yake cewa "KADA KUCI KUDI KAN BARNA SAI
DA YARJEJENIYA (Cinikayya a tsakani)"
ALLAH S.W.T Cikin ikon sa ya hukunta cire
hannu ga duk wanda aka kama da laifin satar
dukiya, Kamar yadda yake cewa "BARAWO
NAMIJI DA BARAUNIYA KU YANKE HANNUWAN
SU"
Hatta wadanda ba musulmi basu aminta da
#SATA ba!!
Ko kudi ko wani abun amfani haramun ne satar
sa...
A farkon musulunci idan anzo yin mubayi'a ga
Manzo s.a.w daga cikin sharuddan yin mubayi'a
har da sai an barranta daga sata! kamar yadda
ALLAH Madaukakin sarki ke shaidawa cewa
"IDAN MUMINAI MATA SUKAZO WURINKA SUNA
SHAIDA MAKA CEWA SUNYI IMANI TO SAI SUN
BAR SHIRKA SUNBAR ZINA KUMA SUN BAR
KASHE YAYAN SU KUMA KADA SU SABA MAKA
GAME DA UMARNIN DAKA BASU"
Tun farko musulunci kenan, Ashe yana gwadama
mana illar #SATA kenan!!
A yanzu #SATA ta zama ba maza ba mata, Ba
yara ba tsoffin da matasa, An maida sata kamar
ibadah!!
A yanzu yan kasuwa na sata!
Ma'aikata na sata!
Kai lamarin ya kai har makabarta ma ba'a kyale
ba ana sata!
Ba makabarta ba kadai, Har massallaci sata, Inda
ake koyon imani, Kamar yadda aka sace mana
batir a nan massallacin!!
Har a asibiti ma ba'a tsira ba.
Ana sata ta hanyar bashi, Wato ka ranci kudin
mutun kuma kaki biya, A lokachi Manzo s.a.w ya
taba yanke hannun wata babbar mata saboda
idan taci bashi sai tace bata ci ba..
Idan muka diba hadisin Manzo s.a.w da yake
cewa "Karshen zamani mutun zai tara dukiya bai
damu da abunda ya tara ba na halal ko na
haram"
ABUBUWAN Dake kawo #SATA nada ta yawa
daga cikin akwai-
*Son dukiya da yawa yana kawo sata!
A yanzu #SATA har a sallar farilla ana sata,
Wata rana Manzo s.a.w ya fadawa sahabbai
cewa 'Barawon da yafi kowane barawo shine
barawo a sallah, Sai suka ce kamar yaya? Sai
Manzo s.a.w yace mai yin qotan kurciya'
*Ma'aikata suna sata, Idan ka saci kudin
Zamfara kamar ka saci kudin duk wani
bazamfare ne.
*Yan kasuwa suna sata, Masu tauye ma'auni
suna sata ne.
*Ma'aikatan lafiya, Gwamnati na biyam su amma
sai suna yan kauye suna karbar kudaden su.
*Wadanda ake ba bashi basu biya.
*Marar cika sallah, kamar yadda bayi ya gabata.
*Matar aure mai satar kudin mijinta ko bincikar
aljihu.
*Na tare da barayi, Wanda ake cewa kunci.
*Mai cin iyaka, Ta gona ko ta gida.
*Satar wutar lantarki.
*Direbobi masu cin amana.
*Satar ansar jarabawa.
Da sauran su...
Wallahi duk kudin da aka sata ALLAH Ya debe
masu albarka, Koda kuwa anyi aikin alkhairi da
kudin.
"SHI ALLAH MAI TSARKI NE BAYA KARBAR AIKI
SAI MAI TSARKI"
"ALLAH BAYA KARBAR SADAKA DA AKAYI DA
HARAM"
ALLAH SWT Ya haramta sata ne dan samar da
zama lafiya al'ummah,
Malamai sunce idan mutun ya saye kayam sata
kuma yasani to shima barawo ne!!
Yana da kyau iyaye su rika kwabawa yayan su
domin lura da tarbiyar su.
Saboda fargabar #SATA a yanzu ko massallaci
kazo kana shakka kada ayi maka sata, Duk da
nan ne fa wajen tsoron ALLAH.
KADAN Daga cikin illolin sata akwai-
>#SATA tana korar imani.
>#SATA tana sanya macewar zuciya.
#SATA aibi ce ga duniya da lahira, Domin tana
tasiri har ga yaya da jikoki.
>#SATA tana sa ALLAH Yabar karbar addu'a.
Yan uwa musulmi masu albarka mu tashi tsaye
mu tuba daga aikata #SATA
Duk abunda ka dauka ka maida shi zuwa ga
maishi, Idan bayanan ka kaiwa magadan sa, Idan
kuma babu su to ka sadakar da niyar ALLAH Ya
kai ladar garesa, Kuma ka yawaita istigfari!!
Yan uwa musulmi masu albarka mu yawaita yin
nafila domin ita nafila tana cika mana ayyuka
marar kyau da muke aikatawa.
Mu tuba tun kafin lokachin mu yakare, Domin
baya mantuwa kuma mai adalci ne ga bayi baki
daya.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe Alzamfari. 07064282182

Jumu'ah 21-Safar-1439
Friday 10-November-2017

HUDUBAH MAI TAKEN ILLOLIN GIBA KASHI NA BIYU

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA

DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #ILLOLIN_GIBA_KA
SHI_NA_BIYU
Godiya ta tabbata ga ALLAH ubangijin halitu, Mai
rahama mai jinkai Mamallakin ranar sakamako,
Muna gode masa muna neman taimakon sa,
Tsira da aminci su kara tabbata ga Manzo tsira,
ALLAH Yayi salati ga manzon rahama da
alayensa da sahabbansa da dukkan wadanda
suka biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar
sakamako.
Yan uwa musulmi a yau zamu chi gaba daga inda
muka tsaya a makwanin da suka gabata, La'akari
da wannan babin (Giba) yana bukatar fadaden
bayani sosai, To hakam tasa muka ci gaba daga
inda muka tsaya.
Hakika addinin musulunci ya wajabta kare harshe
da sauran abubuwan da musulunci ya shar'anta,
Musulunci ya haramta cutar da dan uwa musulmi
ta kowace fuska!
'Wata rana manzo s.a.w yana tare da sahabbai
R.a sai ya tambayesu shin mi kuka sani game da
giba? Sai sukace (Sahabbai) ALLAH Da manzon
sa ne suka sani, Sai Manzo s.a.w yace fadar
wani abu akan wani idan bayanan, Sai sukace
koda abun da kafada gaskiya ne? Sai manzo
s.a.w yace eh koda gaskiya ne, Idan kuwa ba
gaskiya bane to laifin biyu kenan (Laifin karya,
Da kuma na giba)!!
A yanzu Giba ta zama ruwan dare, Ta inda duk
wajen dakaje zakaji ana yinta ana fadar kalamai
kan wani ko wata.
ALLAH Madaukakin yana fada mana cewa "YAKU
MASU IMANI KU NISANCI ZATO DOMIN ZATO
YANKI NE NA ZUNUBI"
Hakama madaukakin sarki na cewa "SHIN
DAYANKU ZAICI NAMAN DAN UWANSA ALHALI
YANA RAYE"
Manzon rahama s.a.w ya fada mana dan
tsoratarwa game da # GIBA yana Cewa "Bani
(Bala'i) ya tabbata ga masu cin naman
dan'umansu"
A koda yaushe muna tare da masu sanya ido
akam mu domin rubuta duk abunda muke aikata
a fili ko a boye, Madaukakin sarki na cewa "KADA
KA FADI ABUNDA BAKA DA ILMI AKANSA
LALLAI DA SAURARE DA GANI DA ABUNDA
ZUCIYA TAYI DUKKAN SU ABUN TAMBAYA NE"
Hakama madaukakin sarki na cewa "DUK
ABUNDA ZAKU AIKATA KUNA TARE DA RAQIB-
ATID"
Tunda har ga masu daukar ayyukan mu tayaya
zamu yin sakaci, Mu rika fada abubuwa kan yan
uwan mu?
Wata rana sahabbai suna zaune da 'Manzo s.a.w
sai wasu sahabbai suka ce ai wane baya cin
abinci sai yaga mutane zasu ci, Kuma baya yin
tafiya sai yaga mutane zasuyi, Sai Manzo s.a.w
yace kunci namansa!!!'
Kudiba girma irin na sahabbai, Kuma abunda aka
fada halin sane, Amma manzo ya fada masu.
Jabir bn Abdullahi ya ruwaito cewa 'Wata rana
muna zaune a wajen Manzo s.a.w sai mukaji
wani wari mai marar dadi, Mai Manzo s.a.w yace
wannan warin wadanda ake konawa ne da juta
saboda sunci naman yan uwansu musulmi, Aka
turo'
Amru bn As wata rana ya tafiya tare da sahabbai
sai suka hadu da wani mushen Jaki a kan hanya,
Sai yace wa sahabbai shin kuna iya chin wannan
naman jakin? Sai suka ce a'a sai yace:Cin
naman sa yafi sauki bisa ga cin naman dan
uwanka musulmi'
Wata rana wani sahabi ya tambayi Manzo s.a.w
cewa 'Shin miye mafita daga Giba? Sai Manzo
s.a.w yace mafita itace ka kare kanka da
iyalanka daga aikata alfasha'
Bayan giba ta baki sai kuma Giba ta zuciya,
Minene giba ta zuciya??
Abunda ake cewa giba ta zuciya itace munana
zato ga musulmi..
Munana zato ga Musulmi ko kuma gibar zuciya,
Shima giba ce da ALLAH Baya yafewa! ALLAH
Madaukakin sarki na cewa "KU NISANCI ZATO
DOMIN YANKI NE NA ZUNUBI"
Hakama Manzo s.a.w yace "Kashedin ku da zato
domin yana daga cikin karyar magana"
Akwai wurare daya halatta kayi maganar mutu,
Wato an lissafa su a cikin Giba to babu laifi...
1-Zalunci-Idan an zalunce ya halatta kaje wajen
wani mai iko kamar sarki, Ko alqali ko iyaye ko
kotu dan a kwato maka hakkinka, Zakayi hakan
ne tare da maimaita duk abunda yafaru dai
dai,Aisha r.a ta ruwaito cewa 'Matar Abu sufyan
ta kawo karar mijinta ga Manzo s.a.w cewa
abincin da yake bata baya isa dan haka tana diba
ta kara dan ya ishesu, Sai Manzo s.a.w yace
mata ba komai dan haka"
Kunga anan akwai halacci mace ta kai kara irin
wannan ta mijinta,
2-Neman fatawa, Ya halarta ka baiyana halin
wani wajen neman fatawa, Misali babana ya
cuce ni, Ko yaya na ko mijina ko matata da niyar
neman fatarwar musulunci akan yadda zaka nemi
hakkin ka.
3-Neman taimako, Neman Taimako zuwa ga wani
shugaba kama ana aikata barna a wani wuri, Ana
shaye shaye ko zina, Zaka iya labartawa
shugaba cewa wane da wane na aikata, Kuma
kafadi hakan ne dan gusar da barnar da ake
aikatawa, To wannan ba'a kiranta Giba, Koda an
kirata to ba laifi akai.
4-Tsoratar da musulmi kan wani sharri, Kafadawa
wani game da wani sharri, Misali yazo neman
bincike game da aure halin wani ko wata, To
anan zaka fadi gaskiyar abunda kasani akai ko
minene babu laifi akan haka nan!
Sai dai idan anfada maka kada kuma ka koma
kafawa ita wada zaka aura ko iyayenta, Cewa
wane ai yace man kaza da kaza akanki, To
wannan kai kayi Gibar!!
Ko kuma kaga dalibin ilmi zaije wajen dan Shi'ah
neman fatawa, To kana iya neman sa kayi masa
bayani akan halinsa.
5-Mai baiyanar da barna qarara, Babu laifi kaga
kafadawa jama'a suyi hattara dashi, Musamman
idan kaga suna kokarin shige masa.
6- Shigiya, Babu laifin idan kaga ana cigiyar wani,
Ka ambaci kamar da dole sai da ita ake ganesa,
Kamar baki, Dogo, Mai qaton kai, Mai idanu da
sauransu, Amma fa da niyar kwatantawa bada
cin zarafi ba!
To a wadannan wuraren 6 kadai ne ake fadar
wani abu game da mutun!
Amma idan shugaba ya zaluncenka bai kamata
duk idan ka zauna kayita fadar saba, Kana
zaginsa alhali wanda kake fadawa baida wani iko
akan ya kwato maka hakkinka.
Hakama wasu sun dauka idan kawai kafadi
magana bayan mutun take giba! A'a Har a gaban
mutun idan kafadi magana wada bata dace kuma
ta bata masa rai to kayi gibar sa!!
Sannan kuma akwai masu gibar karamin yaro,
Suna cewa wancan yaron kaza da kaza suna
aiban tasa, Suna fadar miyagun kalamai kansa,
To duk wannan nau'i ne na giba!!
A wannan yanayin da muke ciki koda ka kare
kanka daga aikata giba, To wani na iya daukowa
yakawo yayi a gabanka, Dan haka sai a kiyaye a
san da suwa za'a zauna.....
Idan kayi gibar wani kuma baka nemi yafiyar sa,
To ranar kiyama za'a debo ladar ka a kara masa,
Idan kuma ta kare za'a debo zunubinka a zuba
masa!!!
Ya ALLAH Ya karemu daga aikata sharruka, Ka
kiyaye mu ka tsare mu, Ya ubangiji ka biya mana
bukatun mu, Kayi rahama garemu ka kyautata
karshe mu Ameen.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe Alzamfari. 07064282182

Jumu'ah 17-Zhul-Hijjah 1438 AH
Friday 8-September-2017

HUDUBA MAI TAKEN TASU'A DA ASHURA

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA


DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #AZUMIN_TASU
'A_DA_ASHURA_DA_BIDI_OIN_DA_AK
A_QAGO_ACIKI
Godiya ta tabbata ga ALLAH Madaukakin sarki
muna gode masa muna neman taimakon muna
neman gafarar sa, Muna neman yakare mu daga
miyagun aiyuka!!
Wanda ALLAH Ya shiryar shine shiryayye babu
mai iya batar dashi, Wanda kuma ALLAH Yabatar
babu mai iya shiryar dashi!
Na shaida babu abun bautawa da gaskiya sai
ALLAH, Kuma na shaida annabi Muhammad
bawan sa ne kuma manzon sa.
Bayan haka, Yan uwa musulmi masu albarka
muna cikin sabuwar shekarar musulunci kuma
watan farko na shekarar, Wata mai albarka mai
falala..
Watan muharram wata ne da ALLAH Ya girmama
ya kuma karrama, kamar yadda yake fada cewa
"LALLAI ADADIN WATANIN 12 NE A WURIN KU
KARRAMA SU KADA KU ZALUNCI KAWUNAN KU
A CIKI"
Ashe kuwa duk abunda ALLAH Ya karrama to
wajibin mu muma mu karrama su,
An karbo daga Aisha r.a tace 'Mutanen jahiliya
sun kasance suna girmama watan Muharram har
suna kiransa da suna Muharram watan ALLAH
Kuma sun kasance suna kauracewa aikata sabo
a cikin '
Yana da kyau mu yawaita azumi a cikin watan
Muharram, Har ma an ruwaito daga Manzo s.a.w
cewa 'Mafificin azumin bayan na watan
ramadana shine azumin watan muharram'
Ibn Rajab yayi sharhi watan Muharram wata ne
falala da ake bukatar yawaita ibadu da
kauracewa zunubi,
Yan uwa musulmi bayan mun azumci kwana
goma a watan Zhul hijja (Watan karshe), Yanzu
kuma sai mu azumci kwana biyu a watan
muharram (Watan farko) za'a rubuta mana ladar
mun fara shekara da ibadah kuma mun kammala
ta da ibadah, Daga hakanan sai a sanyamu cikin
bayi na kirki.
Lallai an mustahabanta muna azumtar wannan
rana domin dinbin falalar dake ciki, An ruwaito
daga Manzo s.a.w cewa 'Azumin 10 ga watan
Muharram ina da yaqinin ALLAH Yagafarta
abunda yagabata'.
Jabir r.a ya ruwaito cewa 'Ban taba ganin manzo
s.a.w na kirdadar zuwan wani azumi ba kamar na
goma ga muharram'
Harma kuraishawa kafin zuwan Manzo s.a.w
suna azumtar wannan rana.
Hakama sadda Manzo yayi hijra zuwa Madina ya
tarar yahudawa nayin wannan azumin, Sai ya
tambaye su miyasa kuke azumtar wannan ranar?
Sai suka ce munayi dan murnar nasarar da
ALLAH Yabaiwa annabi Musa A.s akan fir'auna,
Sai Manzo s.a.w yace 'Ai mune muka fi
chanchanta muyi domin Musa dan uwan mu'
Amma tun yana Makkah yana wannan azumi ya
tambaye su dan yaji hujjar da suka dogara da ita.
Azumtar wannan lokachin nada falala da dama
ga wasu daga cikin.
*Manzo s.a.w yayi, Kenan yasamu falala daga
Manzo s.a.w
A yanzu munyi sa'a kasancewa gobe ne tara ga
wata sai mu tashi da tasu'a jibi muyi ashura.
ABUBUWAN DA AKA KIRKIRO A WANNAN
WATAN
Wasu na shafa kwalli, Wasu na lalle wasu na
dinki da dafe dafen abinci!
Wasu kuma baqin ciki a wannan rana, Har suna
koke koke da saran jikin juna da sauransu!
To a maganar gaskiya wannan baida asali daga
kowane magabaci na kwarai, Wasu kuwa na
cewa awadata gida da abinci wai saboda
shekarar zata kasance ma da kyau.
Wadanda sukeyi wannan kirkiren sune suka
kashe sayyidina Aliyu r.a suka kashe Hassan r.a
kuma suka kashe Hussaini R.a.
Su kuwa nawasib sune suke murna saboda sune
suka kashe ahlul baiti.
Yan shi'ah sune suka kashe sayyidina Hussani
r.a a Karbala kuma sun kashe mahaifinsa Aliyu
R.a, Dukkansu sunyi shahada.
Yan shi'ah sun tanadi ranar ashura a matsayin
ranar baqin ciki, Har suna yanka jikin su da
aikata rashin imani ga yara, Wannan yasabawa
musulunci da kuma lafiyayen hankali, Kuma
babbar alama ce dake nuna yadda addinin Shi'ah
yayi hannu riga da musulunci kuma yana nuna
cewa Shi'ah addini ne mai zaman kansa.
Annabi Zakariya A.s, Da Hassan r.a, Da Umar r.a
da Aliyu r.a duk kashe su akayi amma miyara
basu baqin cikin kashe su??
A musulunci babu wata rana da aka tanada dan
baqin ciki, Idan ma za'a sanya to ranar data fi
chanchanta itace ranar da Manzo s.a.w yabar
duniya. Domin Manzo s.a.w yace 'Duk wanda
wata musiba ta sama ko ta rashi to yayi hakuri
domin rashina shine babbar musiba'' !!!!
Shari'ah ta yarda idan akayi maka rassuwa kayi
jimami har da kuka tsawon kwana 3, Amma
abunda yafaru shekaru dubu daya da wani abu
da ya gabata.
Lallai muyi tsayin daka waje yakar shi'ah a
gidajen mu da yayan mu.
A ranar Ashura yan shi'ah nayi babbar bajakoli
da izgili da zagin sahabbai, Alhali Manzo s.a.w
yace "Kada ku zagi sahabbai na domin wallahi
koda dayanku yaciyar da kwatankwacin dutsen
uhudu na zinare bazai kai muddunsu daya ba, Kai
koda rabinsa!"
Wannan na nuna wallahi koda duk mutanen
duniya zamu bi ALLAH Da ibadah har tsawon
shekara bazamu kai nasu da kwana daya ba!! Ko
da rabi ma..
To mutane masu daraja irin haka kuma sune za'a
zaga??
Yan shi'ah na ziyartar makabartu har suna
ziyartar kabarin Hussaini r.a suna cewa' wai duk
wanda ziyarci kabarin sau daya yafi aiki hajji sau
ashirin' Kunj4 wani cin mutunci!!
A ranar ne suke aikata auren mutu'a!!
Lallai babban dalilin yin azumin shine ranar ne
ALLAH Ya halakar da fir'auna.
Yan uwa musulmi masu albarka an samu sabanin
lissafi inda wasu ke cewa yau tara ga wata, A'a
yau ne takwas ga wata kuma a kasar Saudiyya
yau tara ga wata, Sai dai zamuyi amfani da
abunda ke kasar mu!!
Muna rokon ALLAH Yabamu zaman lafiya, Yayi
jagora ga mai martaba Emir na Tsafe, Da kuma
gafarta margayin daya rassu, Ya ALLAH Yayi
salati ga Manzo rahama da iyalansa da
sahabbansa da wadanda suka biyo bayansu da
kyautata, Ka rahama mana ka biya mana bukatun
mu.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe Alzamfari. 07064282182

Yau Jumu'a 8-Al-Muharram 1439 AH
Friday 29-September-2017

HUDUBA MAI TAKEN HARAMCIN CAMFI

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A DAGA MASJID
ABI HURAIRAH DAKE TSAFE ZAMFARA


DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE


A wannan makon limamin Massallacin Jumu'a na
Abi Hurairah dake unguwar Area2, Tsafe Sheik
Sani Na Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #CHAMFI
Godiya ta tabbata ga ALLAH Wanda ya halicci
duniya da abunda ke cikinta, Godiya ta tabbata
ga ubangiji daya ubangijin rana da wata, Godiya
ga wanda kagemu ya bamu ikon gudanar rayuwa.
Tsira da amincin ALLAH Su tabbata ga mafi
soyuwa wajen ubangiji, Annabi Muhammad s.a.w
da iyalansa da sahabban da duk wadanda suka
biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar
sakamako muna rokon ya shiryar damu hanya
madaidai ciya ameen.
Yan uwa musulmi masu albarka a yau Khudbar
tamu zatayi magana ne game da #CHAMFI!!!
#CHAMFI wato ana nufin danganta faruwa ko
afkuwar wani abu na rayuwa ko mako bayan ta,
Ga lokachi ko zamani ko kwana ko wata ko
shekara ko dan Adam, Ko aure ko mutuwa da
sauransu!!
Bayan Manzo s.a.w yafa mana cewa "Duk wanda
ke #CHAMFI to ya tabbatar yayi shirka"
Shirkar kuwa zata iya kasancewa rakama ko
kuma babbah!!
Jingina faruwar wani abu ga aure ko shugaba
duk wani musulmi mai tauhidi yasan babban
kuskure ne.
Wasu kuma da danganta rashin lafiya da
#CHAMFI da kuma masu danganta duk wani
abunda yasame da #CHAMFI!!
Yan uwa musulmi masu albarka
Babu inda ya halatta ga musulmi yayi #CHAMFI
sai a wuri daya shine kayi #CHAMFI ga kanka
wato duk abunda yasameka a rayuwa ka dauka
cewa daga laifukan da kake aikatawa na rayuwa!
Shi #CHAMFI tsohon abu ne dake da tsohon
tarihi wato ba daga hausawa ne aka fara yin
#CHAMFI ba, Bari muji kadan daga wasu
al'ummah dake aikata #CHAMFI-
Yahudawa sun # CHAMFA Annabi Salihu (a.s)
domin yazo ya isko su cikin bata da shirka,
Yafara yi masu wa'azi ba dare ba rana, Da suka
qi yin imani sai ALLAH Ya jarabce su da musibu!
To sai suka fara yin #CHAMFI cewa Annabi
Salihu (A.S) yakawo masu!
Mushrikai na Makkah suma sun #CHAMFA
Manzo (s.a.w) domin ya isko su cikin kafurci da
bata, Yayi masu wa'azi da suka qi karba sai
ALLAH Ya jarabce su da talauci da rashi!
Suma sai suka #CHAMFA Manzo (s.a.w) cewa
kafin yazo suna cikin arziki, Amma da yazo sun
fara fadawa talauci!
Idan muka diba rayuwar mu ta Najeriya zamu ga
cewa kwatan kwacin rayuwar nan ta same mu, A
baya yan kasa na cikin wadata amma a yanzu
talauci wane hali muke ciki??
To nan yakamata yayi tauhidi yayi amfani,
Garemu.
Yan uwa musulmi masu albarka, Yakamata mu
kara sani talauci da arziki da komai da komai duk
suna hannu ubangiji, Amma sai mu dora laifi kan
shugabanin mu, Shin mu manta cewa akwai yan
Najeriya masu aikata Shirka wanda sune
kolulowar laifi ga ubangiji.
Mun manta fadar ALLAH s.w.t daya fada cewa
"DUK ABUNDA YASAME KU DAGA ALLAH DA
AYYUKAN DA AIKE AIKATAWA"
Hakama madaukakin sarki na cewa "DUK
ABUNDA YASAMU KU MAI KYAU DAGA ALLAH
MARAR KYAU KUMA DAGA ABUNDA KUKE
AIKATAWA NE"
Shi #CHAMFI inkari ne tauhidin rububiya.
Yan uwa musulmi masu albarka, Akwai abunda
jahilai keyi na #CHAMFA Watan safar wato
watan da muke ciki, Ma'ana wata na biyu a
musulunci, Jahilai sun kasance suna kauracewa
aikata ayyuka kamar aure da tafiya da sauransu!!
Sai Manzo s.a.w yace "Babu komai a watan
Safar, Wata ne kamar saura"
Akwai masu alaqanta cuta da #CHAMFI, a yanzu
turawan yamma na farfaganda ta cewa suna
cuta kamar ta sauro da sauransu, Wai sai suce
sun karar da ita, Hakika ita cuta tana samuwane
da iko da iznin ALLAH.
A cikin ayyukan turawa akwai tuka da warwara.
A cikin wannan watan akwai musulmi da suke
cewa wai ALLAH Na saukar da annoba dubu
ashirin da uku (23, 00.000) wai suna cewa ayi
nafila raka'a 4 da fatiha kafa 7 idan kagama za'a
rubuta 'Salamun ala nuhin' a rubuta a sha.
To wannan baida asali a musulunce kuma bidi'ah
ce!
Su duka al'amura da faruwa ne da ikon Allah.
Babban tabi'i imam alhambali yace "Kebance
wani lokachi dan a aiyana cuta garesa kuskure
ne"
Wani fasihin mawaki na cewa 'Muna ta dorawa
zamani laifi mun manta mune ke aikata laifin ba
zamani ba'
Yan uwa musulmi masu albarka, A kowane
lokachi mu zama masu imani domin bamu san
inda ajalin mu yake ba!
A takaice dukan wani abu da ake aikata wato
#CHAMFI shirka ne kuma bata ne!!
ALLAH Yabiya bukatun mu ya gafarta mana yayi
rahama garemu, Yabamu zaman lahiya mai
dorewa.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe Alzamfari. 07064282182

Jumu'ah 13-Safar1439 AH
Saturday 03-November-2017

HUDUBA MAI TAKEN LAYYA DA HUKUNCE HUKUNCENTA

FASSARAR HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA


DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE

A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #LAYYA_DA_SALLAR
_IDI_DA_ABUBUWAN_BUKATA_A_WANN
AN_WATAN_DA_KYAWAWAN_HALAYE_A_
WAJEN_BIKIN_SALLAH
Godiya ta tabbata ga ALLAH Madaukakin
sarki,Muna gode masa,Muna neman taimakon
sa,Muna neman ya kare da sharrin kawunan mu
da miyagun ayyukan mu, Tsira da amincin ALLAH
Su kara tabbata ga manzo tsira, Annabin rahama
sallallalahu alaihi wassalam, Da iyalansa da
sahabban sa da dukkan wadanda suka biyo
bayan su da kyautatawa har zuwa ranar
sakamako.
Yan uwa musulmi yau Khudbar zata magana ke
wannan halin da ibadu dake gaban mu,
Yan uwa musulmi muji tsoron ALLAH Gaskiyar jin
tsoron sa, Kamar yadda umarce, Kuma mu kara
gode masa kamar yadda ya umarce mu, Sannan
abu ne mai kyau mu dage da ambaton ALLAH A
Wannan lokachin kamar ya umarce mu da cewa
"YAKU WADANDA KUKA YI IMANI KU AMBASHI
ALLAH AMBATO MAI WAYA KUYI KUMA TASBIHI
GARESHI"
Yan uwa masu albarka muyi tseararre a wannan
lokachin (Anan ana bukatar tsere) domin suna
cikin kwanakin da Allah ya kebance dan rahama
da tausayi ga bayin sa!
Yawaita ambaton ALLAH A cikin wannan lokachi
abu ne mai matukar muhimmanci, Hasalima an
ruwaito Abi Huraira R.a ya kasance yana shiga
ko ina yana yawaita yin kabbori, Har cikin
kasuwa yana shiga dan tunasar da yan kasuwa
da masu sayyayya, Yana daga murya yana cewa
'Allahu akbar Allahu akbbar, Allahu akbar wallahu
Akbar walil lahil hamdu'
>LAYYA
Daga cikin kwanakin goma akwai wata babbar
ibadah da ake aiwatar a wannan watan, Layya
nada sharudda
-Amfani da kudin halal wajen sayen dabbar
zakuyi amfani da ita,
Ita layya Sunnah ce daga sunnar annabawa,
Annabi Ibrahim A.s da kuma Annabi Muhammad
S.a.w , Inda tayo asali shine lokachin da annabi
Ibrahim yayi mafarkin ya yanka dansa wato
Annabi Isma'il A.s, Alqur"ani yabamu labarin
cewa Ya yanka dan nasa"SAI MUKA FANSHI
YARON DA ABUN YANKA MAI GIRMA (Rago)"
Layya abu ce dake kara kusanta bawa da
ubangijin sa, ALLAH Ya umarci Manzo s.a.w da
zuwa sallar idi, Da layya kamar yadda yake fada
cewa "KAYI SALLOLI KUMA KA YANKE LAYYA
KA DAN ALLAH DA KUMA TSARKAKA WAJEN
ALLAH"
Hadisi yazo daga sahabin manzo s.a.w cewa
"Mun kasance da ranar arfa da Manzo s.a.w
yace lallai yazama tillas ga kowane gida suyi
layya"
Ashe yazama wajibi ga kowane gida suyi layya,
Malamai sunce gida guda suna iya hadawa asayi
dabba dan ayi layya!
Hakama wani hadisi da yayo ya tsoratar da masu
tabi'ar matsolanci cewa "Manzo s.a.w yace 'Duk
wanda keda wadatar yin layya baiyi ba to kada
ma yaje massallachin idi' "
Sau da yawa zakaga magidan ci a ranar jajibiri
ya sawo wancan ya sawo wanchan, Dan adafa
abinci amma ya kasa yin layya, Ita wannan sallar
ba sallah bace ta dafe dafen abinci, Sallah ce
yanka layya!
Sheik Muhammad bn fodio yace: 'Idan bakayi
layya ba, Kuma ka dafa abinci ko wannan abincin
bidi'ah ce '!!
*Layya ta hau wajibi ga kowane musulmi, baligi,
Mai hankali, Mai wadata, Mazaunin gida, Amma
kananan yara sunnah ce, Yin layya koyi ne da
Manzon rahama s.a.w.
Ibn taimiyah yace 'A ibaduh na jiki babu kamar
sallah, A ibada ta kudi kuma babu kamar layya'
Layya ana yin tane daga dabbobin ni'imah wato
sune kamar haka-
~Rakumi rakuma
~Sa ko saniya
~Rago ko Tunkiya
~Bunsuru ko akuya.
Wadannan dasu ne kadai ake yin layya!
Sau da yawa zakaga wasu na sakaci wai da
sunam suna jin kunyar yanka bunsuru ko tinkiya
ko akuya, Dan basu da halin sayen Rago, Wannan
bai dace ba, Hausawa ma suna cewa dai dai kurji
dai dai ruwa!!
Yan uwa musulmi masu albarka, Sai dabbar layya
ta cika wadannan sharuddan sannan take layya,
~Rakumi ko rakuma sai sun kai shekara 5
~Sa ko saniya sai sunkai shekara 2 zuwa ta 3
~Bunsuru ko akuya sai sunkai shekara 1 zuwa
cikin ta 2
~Rago ko tunkiya sai sun kai shekara 1 !!
Duk da akwai basu dake cewa ana iya yanka mai
wata 6, Amma wannan bai inganta ba!
Dole ne dabba ta tsarkaka daga aibi, Wato wasu
kuma sharudda kamar haka,
~Ba'a layya da mai ido daya
~Rashin lafiyar da data baiyana
~Dabba mai gurgunta
~Tsohuwar dabba marar mai marar bargo
~Mai yankakke kunne, Ko bindi ko marar hauru
da sauran illoli baiya nan nu, DUK BA'A LAYYA
DA SU!!!
Ana son dabba wadda idan ka kalle ta zakaji
wadata.
Idan ka sawo dabba sai daya daga cikin matsalar
chan ta same ta, Malamai sunce ba ba komai
abunda dai ba'a so shine kaje saye kaganta da
wannan illar kuma ka sawo.
Hikmar dake cikin layya:
1-Kusanta bawa da ALLAH Domin ciki umarni ne
Na ubangiji kamar yadda madaukakin sarki ke
cewa "ALLAH BAYA BUKATAR NAMA KO JINI
YANA BUKATAR TSARKAKE NIYA"
2-Dan samarwa mabukata, Wato rabawa
wadanda basu yi ba, Saboda rashin hali
3-Kara soyyyaya tsakanin musulmi, Duk wanda
ya dauki nama ka bashi zaiji farin ciki da kara
sonka
4-Alamace ta daga addinin Allah, Domin yin layya
daga addini ne,
5-Koyi ce da jagorori wato annabi Ibrahim A.s da
Annabi Isma'il A.s, Mu diba fa annabi Ibrahim a.s
ce masa akayi yayi layya da dansa,Kuma ya
dauki azamar yi,
6-Yin layya ko ne da alhazai, Su suna yin hadaya,
mu kuma dake gida muna yin layya.
SALLAR IDI
Sai kuma bangare na biyu, Manzo s.a.w ya
wajabta mana sallar idi, akwai hadisi daga
manzo s.a.w da yake cewa "Manzo s.a.w yazo
garin yasrib (Madina) ya iske suna yi wassani
biyu a shekara, Sai manzo s.a.w yace ku aje
wadannan ga wasu nan wato ranakun sallah"
Manzo s.a.w yayi umarni a fita a ranar sallah
zuwa idi, Har wata mata tambaye sa to ni ina
son fita amma banda hijabi sai yace kije ki aro.
harda mata masu haila suna iya fita,
IDAN RANAR JUMU'A TA HADU DA RANAR EID
Manzo s.aw. idan ranar JUMU'AT Ta hadu da
ranar Eid to kana da zabi, Ba sai kayi jumu'a ba,
Amma Abu hurairah yace mu muna yi dan samun
lada mai yawa, Anyi haka dan falala garemu,
Saboda hidimar sallah wani na'iya mantawa da
sallar jumu'ar mah,
MIYAGUN DABI'U RANAR SALLAH
Ranar sallah rana ce ta farin ciki da murna,
Wadda musulunci ya ware muna a shekaru sai
biyu wato sallar azumi wato karamar sallar sai
kuma sallar layya ko kuma babbar sallah,
A lokachin sallah ana ado sosai kuma ana
ziyartar yan uwa da abokan arziki, Ko kiran waya
da dai sauran hanyoyin sada zumunta, Sai da
kash!
Ana samun masu amfani da wannan damar suna
wuce wuri har suna afkawa cikin haramun, Kusan
yazama al'adar wasu iyaye ta kyale yayan su
suyi abunda suka ga dama a ranar sallah ba tare
da taka masu burki ba,
A ranar sallah zakaga matasa musamman yan
mata sun chaba ado sun fito, Kirjin su a waje,
Bayan su a zahiri, Duk suna murnar sallah!
Wasu kuma a ranar suke fara iya shaye shaye
musamman samari, Wasu ma matasan a ranar
suke iya zina, Anan arewa cin Najeriya musan
yadda yayan mu suka tarbiyan tu da rufe jikin su
ta hanyar hijabi, Amma abun takaici zakaga wasu
ko gyale ma basu sawa,
Suwa keda laifi??
Manyan manyan masu laifi sune iyaye, Idan aka
ce iyaye ana nufin iyaye maza da iyaye mata,
Laifin uba anan shine shine ke sawo kayan to
dole kai zaka saka ido kan yadda za'a dunka
kayan dama yadda za'a sanya su, Zakaga uba
yasawo kaya kawai ya baiwa yayan, Haka bai
dace ba sam!
Ita kuma uwa ita ce ake kai dinkin agabanta,
Wajen sanya kayan ma agabanta, Amma bata iya
tsawatarwa akan abunda ke yi na kuskure, Iyaye
ku tuna Manzo Allah s.a.w yace mana "Dukkan
ku masu kiwo ne kuma za'a tambaye ku game da
abunda aka baku kiwo"
Masu laifi na biyu sune shuwagabani, Dole ne
shugabanin ku dauki matakan gyara tarbiyar
al"ummar su ta hanyar sanya idanu aka harkokin
su, mai makon haka sun bar al'umma kara zube
Na ukku sune malamai, Malamai sune suka san
hukuncin addini, Kuma sune masu wayar da kai
ta hanyar nasihohi da khudbobi da sauransu, Dole
ne malamai su zage damtse ka'in da na'in wajen
tabbatar da tarbiyar al'umma dan samun manya
gobe na kirki,
Manzo s.a.w yana cewa '"Mata ku zauna cikin
gida jen ku kada hali inyi na jahiliyah (fita
barkata)"
Sannan manzo s.a.w yakawo hadisi mai
tsoratarwa da yake cewa "Mata 2 yan wuta ne,
Ni ban gansu ba, Idan kun gansu ku tsine masu,
Sune masu sanya tufa amma basu sanya ba, Na
biyu sune masu fitar da gashi waje basu shiga
aljannah ko kan shinta bazasu ji ba, Duk da
akwai nisa daga kaza zuwa kaza"
Abun takaici wasu yan mata har dakunan samari
suke shiga da sunan yawon sallah,
Wasu kuma baso da murnar sallah basu yin
sallah suna ji ana kira amma basu zuwa, Dukka
dai muna fatar za'a gyara.
ALLAH Madaukakin sarki ya gafarta mana ya
rahama, Ya biya mana bukatun mu, Yayi rahama
ga mamatan mu.

©®Ibrahim Rabilu Tsafe Alzamfari. 07064282182

Jumu'a 3-Zhul-Hijjah 1438 AH
Friday 25-August-2017