Wednesday, 26 October 2022

02 NASIHAR BARKA DA SAFIYA

*NASIHAR BARKA DA SAFIYA 002*

*_(Nine Yusuf wannan kuma ɗan uwana ne)_*

Wannan maganar Annabin Allah Yusuf (Alaihissalam) ce, a lokacin da yayi maganar shine shugaban ƙasar Misira kuma taskar arzikin ƙasar na akan ikonsa...

Tare da haka, bai juya baya ya kalli matsayinsa ko muƙamin da yake akai ba, sai ya ambaci sunansa tsurar shi ba tare da wani laƙabi ba, domin wanda yake da zuciya mai girma, da ɗabi'u maɗaukaka baya juyawa ya kalli wani matsayi na mulki ko kuɗi ko yayi alfahari ya riƙa ɗagãwa da hakan a cikin mutane.

Dr. Hussein Al~feefy
_____________________________

Ni(Abu Sinan) nace, naji a cikin wani karatu da Fadhilatush-Sheikh Dr. Swalih bn Abdillah bn Hamd Al-Osaimi (H) aka tambaye shi cewa: meyasa kake ambatar sunan su Ibn Taimiyya da Ibnul Qayyim gãya ba tare da laƙabin Sheikh, ko Al-allama ko Ustaz da sauransu ba?

Sai ya da amsa da cewa: Wanda Allah ya ɗaukaka baya buƙatar wata ɗaukakar mutane, yace Abubakar Siddiq, ko Aliyu ko Abu Huraira (Radiyallahu Anhum) ka taɓa jin za'a kira su an ce Al-allama Abu Huraira? Ko Fadhilatush-Sheikh Aliyu Bn Abi Ɗalib? Yace sun wuce wannan matsayin, don haka ne ma aka samu wasu daga cikin magabata suna kyamatar wannan laƙubban.
___________________________

Amma yau Ɗalibin da bai gama zama a harkar ilimi ba idan zaka kira sunan shi kai tsaye sai yaga ka ƙasƙanta shi saboda rashin ikhlasi a cikin ayyuka.

Allah ya ganar damu ya bamu ikon yin ibada domin shi


© *AbbanSinan Tsamiya*
01 Rabi'u Thani, 1444AH
27 October, 2022

01NASIHAR BARKA DA SAFIYA

*NASIHAR BARKA DA ASUBA*

Idan wani yazo wurin ka domin ka taimake shi akan bukatarsa, toh fa kaine mai amfanuwa da hakan, domin Allah SWT shine yayi maka ni'ima, ya buɗe maka ƙofar Alkhairi.
A wannan lokacin kyautatawar da za kayi mashi kanka ne zaka kyautata ma; Allah Madaukakin Sarki yana cewa: (Idan kun kyautata, toh kanku kuka kyautatamawa) a wani wuri kuma yace: (Ka kyautata kamar yadda Allah ya kyautata maka)

Allah ya bamu abinda zamu taimaki wanda yazo nema a wurin mu🤲

 ©Dr. Hussein Al-feefy

Fassarar:
*AbbanSinan Tsamiya*
30 Rabi'u Awwal 1444AH
26th October, 2022

Tuesday, 13 September 2022

LADUBBAN TAMBAYA

*FA'IDA*

Ya kamata ɗalibi yayi riko da ƙa'idodi huɗu yayin tambayar Malami:

 1. Kayi tunani akan abinda zaka tambaya, duk wanda ya munana manufar tambayarsa, za'a haramta mashi albarkar ilimi, da amfaninsa saboda mummunar manufarsa.

 2. Kula akan abinda kake tambaya akansa, kada kayi tambaya sai abinda zai amfanar.

 3. Kula da halin da Sheikh yake ciki a lokacin tambayar, kada ka tambayi Malami a yanayin da baya cikin natsuwa ko baya cikin jin daɗi.


 4. Mai tambaya ya natsu akan yadda zai gabatar da tambayarsa, ya tabbata ya fitar da ita a hanya mai kyau yadda za'a fahimta.


Na cirato na kuma fassara daga Littafin تعظيم العلم na Masoyina *Fadhilatush-Sheikh Al-allama Dr. Swalih bn Abdillah bn Hamad Al-Osaimi (Hafizahullah)*


© Mai Fassara
*Abban Sinan*
16/02/1444AH
13/09/2022

Thursday, 29 July 2021

002 ‏FARIN JEKADA ANNABI MUHAMMAD ‎ﷺ

FARIN JEKADA, ANNABI MUHAMMAD ﷺ

Fitowa ta biyu 002

Manzon Allah ﷺ yana da wasu haƙƙoƙi masu tarin yawa da ba za'a iya ƙirge su ba, waɗanda suka zama wajibi mu kula dasu kwarai da gaske.
Ga kaɗan daga cikin su:

1. IMANI DA MANZON ALLAH ﷺ

Ma'anar imani da Manzon Allah ﷺ kamar yadda wasu daga cikin Malamai suka faɗa shine: 
a) Gasgata shi a cikin duk abinda ya faɗa ko ya bada labari
b) Yi Mashi biyayya a cikin dukkan komai
c) Bin Shari'ar Manzon Allah ﷺ
Don haka ne ma wasu daga cikin Malamai suka ce gasgata Manzon Allah ﷺ yana ɗaukar abubuwa guda biyu:
NA FARKO: Tabbatar da AnnabtarSa ﷺ da gasgata Shi akan duk abinda ya isar daga Ubangijin Shi SWT, da kuma yadda cewa Wannan ya keɓanci Manzon Allah ﷺ ne kawai (Ma'ana: babu wani Annabi da zai zo da irin wannan a bayan Shi ﷺ

NA BIYU: Gasgata Shi ﷺ a cikin abinda yazo dashi, ka yarda cewa yazo dashi ne daga wurin Allah SWT, sannan kuma wajibi ne a bishi.

Wajibi ne a Gasgata Manzon Allah ﷺ a cikin dukkan abinda ya bada labari daga Allah SWT, Na abubuwan da suke na Gaibu ne, Labarin Wuta da Aljanna, Labarin tanadin Sakamako mai kyau ga wanda ya kyautata aiki, da mummunan sakamako Ga wanda ya ɓata aikinsa, Labarin Azabar ƙabari da kuma Ni'imomin dake cikin shi, da dukkanin wani abu da Manzon Allah ﷺ ya bada labari dole ne a Gasgata Shi ﷺ.
Allah Maɗaukakin sarki yana cewa:
وَمَا يَنطِقُ عَنِ الۡهَوَىٰ، إِنۡ هُوَ إِلاَّ وَحۡيُُ يُوحَىٰ
Ma'ana:
Kuma bã ya yin magana daga son zuciyarsa.
(MaganarSa ﷺ) ba ta zamo ba, fãce wahayi ne da ake aikõwa.

Zamu dakata a nan Saboda kada Rubutun yayi Tsayi, a fitowa ta gaba zamuyi Magana akan: ABUBUWAN DAKE WARWARE IMANI DA MANZON ALLAH ﷺ Allah ya ɗora mu akan Tafarki na gaskiya har ƙarshen Rayuwar mu, Allah ya kare Addinmu na Musulunci daga Makircin yahudu da Nasara🤲 yaa Allah ka rugurguza duk masu taɓa ƙima da mutuncin Manzon Allah ﷺ a duk inda suke, yaa Allah da wanda akayi yaji daɗi, da wanda yayi, da wanda yana da ikon magana amma yayi shiru Saboda kada arna suce mashi mai tsats-tsauran ra'ayin addini, yaa Ubangiji duk ka tozarta su a nan duniya da gobe ƙiyama🤲 yaa Ubangiji ka ƙara mana Son Annabi Muhammad ﷺ🤲 kasa mu mutu muna masu bin shiriyar Annabi Muhammad ﷺ


✍️ Hashim Sirajo Uba Ats-tsamawy Tsafe
atstsamawy@gmail.com
18/12/1442AH
28/07/2021

01 ‏FARIN JEKADA ANNABI MUHAMMAD ‎ﷺ

FARIN JEKADA, ANNABI MUHAMMAD ﷺ 

Fitowa ta Farko 001

KO KASAN MA’NAR MUHAMMADUR RASULULLAHI ﷺ ?

Godiya ta tabbata ga Allah (S.W.T) wanda ya haɗa Sunan shi da sunan Manzon sa a wajen kalmar Shahada.

Tsira da Aminci su tabbata ga Manzonsa wanda ya fayyace mana ma’anar kalmar shahada ga ayyukansa.

Ma’anar ka shaida MUHAMMADU Manzon Allah ne, shine yin furuci a ɓoye da bayanne, cewa lallai Annabi Muhammad ﷺ bawan Allah ne kuma Manzon Allah ne zuwa ga mutane baki daya, da kuma aiki da abun da wannan kalmar ke ɗauke da shi.

Ya kamata kai Ɗan uwa Musulmi kasani cewa kalmar MUHAMMADURRASULULLAH ﷺ 
tana da ma’ana da rukunnai da sharuɗɗa, da kuma abun da ta hukunta. Ga yadda ma’anar take:

Yiwa Manzon Allah ﷺ ɗa’a a cikin abinda yayi umurni, gasgata shi a cikin abinda ya bada labari, nisantar abinda ya hana ko ya tsoratar, ba’a bautar Allah, bautar kuma ta samu karɓuwa face yadda Manzon Allah ﷺ 
ya tsara (ya shar’anta).
Dole ne mai faɗar Muhammadur Rasululahi ﷺ 
 yayi aiki da waɗannan bayanai, domin faɗar hakan da harshe kawai ba zai wadatar ba.

RUKUNAN MUHAMMADUR RASULULLAHI ﷺ 
 GUDA BIYU (2) NE:

RUKUNI NA FARKO: 
SHINE ZAMAN SHI BAWAN ALLAH:
 Zaman shi bawan Allah yana kore zurfafawa gareshi. Kamar yadda hadisin da Bukhari ya ruwaito yana cewa "Kada ku ɗagani kamar yadda nasara suka ɗaga ISA DAN MARYAM (A.S) Ni bawan Allah ne kuma Manzonsa ne.”
Ma’anar bawan Allah shine: mutum ne wanda aka halitta daga cikin halittar Allah yana gudana a gareshi abin da yake gudana ga mutane kamar yadda Allah SWT ke faɗa cewa: - “Kace masu lallai ni mutum ne irinku (Suratul Kahfi 109). Cewa da wasu keyi Manzon Allah ﷺ  ba mutum bane wannan zurfafawa ne, da kuma nakkasa shi. Masu faɗar wannan sun can-can-ci a hukunta su.

RUKUNI NA BIYU: SHINE MANZON ALLAH (S.A.W): - Ma’anar Manzon Allah ﷺ 
shine wanda aka aiko ga wasu ko kuma ga mutane baki ɗaya don kira ga Allah. Shi Mai bushara ne mai gargadi.

SHARUDDAN MUHAMMAD RASULULLAH ﷺ 
 GUDA SHIDA (6) NE:

1. Furuci da ManzancinSa da kudiri a cikin zuciya.

2. Bin Manzon Allah ﷺ da aiki da abunda yazo da shi na gaskiya, da barin abun daya hana na ɓarna.
3. Gasgata abin da ya bada labari na gaibu daya wuce da kuma mai zuwa.

4. Son Manzon Allah ﷺ fiye da kanka da dukiyarka da uwayenka da sauran mutane baki daya.

5. Gabatar da zancen shi akan zancen ko wane mutum da kuma aiki da sunnar Shi ﷺ 

6. Bashi kariya daga kowace nakasa da kuma kare sunnar shi iya karfinka.

ABINDA KALMAR TAKE HUKUNTAWA SHINE:

Yi mashi Ɗa’a, gasgatashi, barin abin da ba sunnar Shi bane, (kamar bidi’o’i da ƙage-ƙage)ﷺ 

FADAKARWA

A karshe muna kira ga ‘yan uwa Musulmi su sani cewa Allah bai karɓar duk wani aiki face sai ya cika sharuɗɗa guda biyu (2).

IKHLASI: - Shine yin aiki don Allah

MUTABA’A: - Bin Manzon Allah ﷺ 
sau da kafa a cikin duk abinda zaka gabatar, kamar yadda bayanai suka gabata.

Daga karshe muna roƙon Allah (S.W.T) ya aza mu kan bin Sunnar Manzon Allah ﷺ  kuma ya kashemu a kanta Amin.

Rubutawa
Abu Sinan, Hashim Sirajo Uba Ats-tsamawy Tsafe
17/12/1442AH
27/07/2021

Tuesday, 30 March 2021

05 HUKUNCE HUKUNCEN TA'AZIYYA

HUKUNCE-HUKUNCEN TA'AZIYYA A MUSULUNCI.

DARASI NA BIYAR (005) DA NA SHIDDA (006)

📒ABU NA BIYAR: SUNNAH NE DANGIN MAMACI DA MAKWABTAN SA SUYI ABINCIN DA KOSAR DA IYALAN MAMACI SU AIKA MASU📒

📌1.Yana daga cikin karantarwar Annabi Muhammad SALLAL LAHU ALAIHI WASALLAM domin tausaya ga iyalan mamaci, dangin sa da makwabtan sa su aika masu abincin da zai Kosar da su. Saboda Hadithin Abdullahi bin Ja'afar da yake cewa: lokacin da labarin mutuwar mahaifin mu (Ja'afar) ya zo, sai Annabi SALLAL LAHU ALAIHI WASALLAM yace: "KUYI ABINCI DON IYALAN GIDAN JA'AFAR (ku aika masu) HAKIKA ABIN DAKE SHAGALTAR DA SU YA ZO MASU". [Abu Dawud da Tirmiziy da bin Majah suka ruwaito sa kuma Hadithi ne ingantacce].

🖋️Haka kuma Imam As-Shafi'iy a cikin littafin sa AL-UMM yana cewa: "INA SO GA DANGI DA MAKWABTAN MAMACI SUYIWA IYALAN MAMACI ABINCI DA ZAI KOSAR DASU A YINI DA DAREN DA YA RASSU, DOMIN SUNNAH NE KUMA YANA DAGA CIKIN AYUKKAN MUTANEN KIRKI A GABANIN MU (Sahabbai da Tabi'ai) DA MA NA BAYAN MU (sauran mabiyan Sunnar Annabi). A karshe sai ya kawo Hadithin Abdullahi bin ja'afar da ya gabata.

📒ABU NA SHIDDA:MUSTAHABBANCIN SHAFA KAN MARAYA DA TAUSAYA MASA📒

📌1. Mustahabbi ne shafa kan maraya da girmama sa, saboda Hadithin Abdullahi bin Ja'afar da yake cewa:.....Manzon Allah ya wuce mu yana kan dabba ni da Qathm da Ubaidullah bin Abbas, sai yace ku miko man shi (wannan yaro) sai aka mika ni ya dora ni a gabansa, sai yacewa Qathm ku miko man shi, sai aka mika masa shi, sai ya dora sa a bayan sa...... a duk lokacin da ya shafi kaina sai yace: "YA ALLAH KA MAYEWA JA'AFAR A CIKIN IYALAN SA". [Ahmad da Baihaqiy suka ruwaito sa kuma Hadithi ne ingantacce].

Wannan shine abinda Sunnar Annabi Muhammad SALLAL LAHU ALAIHI WASALLAM ta tabbatar dangane da ta'aziyya.

Wallahu a'alamu bissawab.

✍️ Nasiru Bala Bungudu
(Chief Imam Salih bin Abdil Aziz Juma'at Mosque Bungudu)

04 HUKUNCE HUKUNCEN TA'AZIYYA

HUKUNCE-HUKUNCEN TA'AZIYYA A MUSULUNCI.

DARASI NA HUDU (004)

📒ABU NA HUDU: ABUBUWA UKU DA YA KAMATA A NISANTA A LOKACIN MUTUWA📒

Ya kamata a nisanci al'amurra uku da matane ke yawan yi lokacin da aka yi mutuwa.

📌1. Tururuwar mutane wurin shiga gidan da akayi mutuwa, bai dace ba mutane su dinga shiga gidajen da aka yi mutuwa alhali basu da hurumin shiga gidan da sunan yiwa mata ta'aziyya.

📌2. Taruwa a wani kebantaccen wuri domin karbar gaisuwa (ta'aziyya), kamar Masallaci ko gida ko Makabarta. Musamman yanzu wuraren karbar gaisuwa ya dauki wani sabon salo, wani lokaci kaga kamar buki ake yi an kawo rumfuna da kujeri sai abinci ake kawowa kala-kala, wani lokaci kuma ya zama wurin sharholiya da shaci fadi da giba da aibanta shugabanni da Yan siyasa da masu kudi harma da malaman addini. Kai abin bai tsaya nan ba wasu sun mayar da wurin karbar gaisuwa wani dandalin siyasa da rabawa matasa zauna gari banza kudade.

📌3. Abinci da iyalan mamaci ke tanada domin tarbon masu zuwa ta'aziyya, dalili akan haka shine: Hadithin Abdullahi Albajaliy yace: mu (Sahabbai) "MUN DAUKI TARUWA DON KARBAR GAISUWA (ta'aziyya) DA TANADIN ABINCI DON MASU TA'AZIYYA A MATSAYIN NIYAHAH (wato kururuwa ko kukan mutuwa). [Ahmad da bin Majah suka ruwaito sa, Imam An-Nawawiy ya inganta shi]

🖋️Haka kuma Imam An-Nawawiy a cikin littafin sa AL-MAJMU' sharhin MUHAZZAB na Shayhin Malami Shayraziy cewa yayi: " AMMA ZAMA DOMIN TA'AZIYYA IMAM AS-SAFI'IY DA SHAYRAZIY SUN NASSANTA KARHANCIN SA(kyamar sa)" abinda yake nufi sun karhanta taruwar iyalan mamaci a gida domin mai son yayi masu ta'aziyya ya same su yayi masu ta'aziyya, dai dai abin da ya kamata su tafi wajen bukatun su (na yau da kullum), duk wanda ya ya hadu dasu yayi masu ta'aziyya. Kuma babu bambanci wajen karhanta wannan zama tsakanin maza da mata.

🖋️Abinda Imam An-Nawawiy ya fada yana cikin littafin Imam As-shafi'iy: AL-UMM 1/248, ga kuma abinda yake cewa a cikin littafin: "INA KYAMAR TARON KARBAR TA'AZIYYA KODA BABU KUKA DOMIN YANA SABANTA BAKIN CIKI DA KALLAFA WAHALHALU NA KASHIN DUKIYA".

🖋️Shi kuma bin Humam ya nassanta karhancin a cikin littafin sa SHARHUL HIDAYAH 1/473, kuma yace: BIDI'AH CE MAI MUNI" kuma wannan shine mazhabar Hanabila kamar yadda yake cikin AL-INSWAF 2/565.

Kuma abinda kowa ya sani ne kamar yadda bayani ya gabata wurin karbar gaisuwa ya zama wurin fira, giba, kallon mata, labarin Yan siyasa, Yan kwallo, shugabanni, masu kudi da dai sauran su. Wanda hankali lafiyayye ba zai yarda da wannan ba balantana Shari'ah.

Wallahu a'alamu bissawab

Mu hadu a darasi na biyar (005)insha'allah

✍️ Nasiru Bala Bungudu
(Chief Imam Salih bin Abdil Aziz Juma'at Mosque Bungudu)

03 HUKUNCE HUKUNCEN TA'AZIYYA

HUKUNCE-HUKUNCEN TA'AZIYYA A MUSULUNCI.

DARASI NA UKU (003)

📒ABU NA UKU: BA'A IYAKANCE TA'AZIYYA DA KWANA UKU BA KAMAR YADDA WASU SUKE RIYAWA 📒

Ita Ta'aziyya ba'a iyakance lokacin yin ta da kwana uku ba, a'a, ana yin ta duk lokacin da aka ga fa'idar yin ta ko kuma lokacin da aka samu haduwa da wanda aka yiwa rassuwa, saboda Hadithin Abdullahi bin ja'afar da ya gabata a darasi na biyu kamar yadda yake cewa: bayan shi ja'afar yayi shahada sai Annabi SALLAL LAHU ALAIHI WASALLAM yayi jinkiri na kwana uku bai je gidan Ja'afar ba, sannan yazo yace: "KADA KU SAKE KUKA GA DAN UWANA DAGA YAU".
Abdullahi yace: sai Annabi yasa aka zo damu, sai muka zama kamar 'ya'yan tsuntsaye (saboda maraici) kuma yasa aka aske muna kawunan mu sannan ya mike hannu na a sama yace: YA ALLAH KA MAYEWA JA'AFAR A CIKIN IYALAN SA, KA SANYA ALBARKA GA ABDULLAHI (dansa) KUMA KA SANYA ALBARKA GA KASUWANCIN SA". ya fadi haka har dau uku. Daga nan dai mahaifiyar mu ta zo tana ambata masa maraicin mu kuma tana cike da damuwa, sai Annabi ya ce mata: "KINA JI MASU TSORON TALAUCI NE? ALHALI NINE MAJIBINCIN SU DUNIYA DA LAHIRA?".

Wallahu a'alamu bissawab.

Mu hadu a darasi na hudu(004) insha'allah.

✍️ Nasiru Bala Bungudu
(Chief Imam Salih bin Abdil Aziz juma'at Mosque, Bungudu)

Thursday, 25 March 2021

02 HUKUNCE HUKUNCEN TA'AZIYYA A MUSULUNCI

HUKUNCE-HUKUNCEN TA'AZIYYA A MUSULUNCI

DARASI NA BIYU (002)

📒ABU NA BIYU: YIWA IYALAN MAMACI TA'AZIYYA DA KUMA LAFUZZAN DA AKE AMFANI DASU📒

Ana yiwa iyalan mamaci ta'aziyya da duk wadansu kalamai da ake sa ran zasu lallashe su, su rage masu radadi da damuwar wannan rashi tare da sanya su yarda da hukuncin Allah da kuma hakuri, musamman ma lafuzzan da Annabi Muhammad SALAL LAHU ALAIHI WA SALLAM yayi amfani da su, idan mutum ya san su, idan kuwa mutum bai san su ba, to, sai yayi amfani da kyakkyawar kalma domin cimma wannan manufa, kuma kada su sabawa Shari'ah. Dangane da wannan akwai hadithai kamar haka:

📌1. Hadithin Usama bin Zayd (R.A) yace:..... Wata diyar Manzon Allah SALLAL ALAIHI WA SALLAM ta aika masa cewa danta na dab da mutuwa sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata gare sa ya aika mata cewa: Yana yi mata sallama kuma yace: "DUK ABINDA ALLAH YA KARBA NASA NE KUMA ABINDA YA BAYAR NASA NE, KO WANE ABU A WURIN SA YANA DA IYAKANTACCEN LOKACI, TAYI HAKURI TA NEMI LADA (a wurin Allah)."  [Bukhariy da Muslim suka ruwaito sa] .

📌2. Hadithin Buraidah bin Husaib (R.A) inda ya nuna cewa:....... Manzon Allah SALLAL ALAIHI WA SALLAM ya je yiwa wata mata daga cikin matan Madina ta'aziyya sai ya ce mata:" BABU WANI MUTUM KO MACE MUSULMA DAKE DA 'YA' YA UKU (da suka rassu) FACE ALLAH YA SHIGAR DA SU ALJANNA SANADIYAR 'YA' YAN" Sayyidina Umar (R.A) yana gafen dama da Annabi SALLAL LAHU ALAIHI WA SALLAM, sai yace koda 'ya' ya biyu?, sai Annabi yace: "KODA BIYU" [Bazzar da Hakim suka ruwaito sa, kuma Hadithi ne ingantcce] 

📌3. Ta'aziyyar da Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata gare sa ya yiwa Ummu Salamah a lokacin da mijin ta abu-Salamah ya rassu, sai Annabi SALLAL LAHU ALAIHI WA SALLAM ya ce: "YA ALLAH KA GAFARTAWA ABU SALAMAH KA DAUKAKA DARAJAR SA A CIKIN SHIRYAYYU, KA MAYE BAYAN SA, KA GAFARTA MUNA TARE DA SHI, YA UBANGIJIN HALITTU, KA YILWATA MASA KABARIN SA KA HASKAKA MASA". [Muslim ne ya ruwaito sa] 

📌4. Ta'aziyyar da Manzon Allah SALLAL ALAIHI WA SALLAM yayiwa Abdullahi bin Ja'afar sai Manzon Allah ya ce:.... "YA ALLAH KA MAYEWA JA'AFAR A CIKIN IYALAN SA, KA SANYA ALBARKA GA DANSA ABDULLAHI (dansa) KUMA KA (Sanya Albarka ga) KASUWANCI" ya fadi haka sau uku. [Ahmad ya ruwaito sa, kuma hadithi ne ingantcce] 

💡Wasu kenan daga cikin lafuzzan da Annabi Muhammad SALAL LAHU ALAIHI WA SALLAM yayi amfani dasu wurin yiwa Sahabban sa ta'aziyya. 

Wallahu a'alamu bissawab. 

Mu hadu a darasi na uku (003)

✍️Nasiru Bala Bungudu. 
(Chief Imam Salih bin Abdul Aziz Juma'at Mosque Bungudu)

001 HUKUNCE HUKUNCEN TA'AZIYYA A MUSULUNCI

HUKUNCE-HUKUNCEN TA'AZIYYA A MUSULUNCI.

DARASI NA FARKO (001)

Da Sunan Allah Mai Rahama Mai jinkai, Tsira da Amincin Allah su tabbata ga Manzon Allah. 

Bisa ga la'akari da muhimmancin ta'aziyya da kuma bukatuwar musulmi ga sanin yadda take a Sunnar Manzon Allah SALLAL ALAIHI WA SALLAM, domin kaucewa bidi'o'i naga ya dace in tunatar da kaina game da takaitaccen bayani akan ta'aziyya wanda ya kunshi abubuwa guda shidda (6) kamar haka:
👉1. Shar'antuwar Ta'aziyya a Musulunci
👉2. Yiwa iyalan mamaci ta'aziyya da kuma lafuzzan da ake amfani dasu.
👉3. Ba'a iyakance ta'aziyya da kwana uku ba kamar yadda wasu suke riyawa.
👉4. Abubuwa biyu (2) da ya kamata a nisanta a lokacin mutuwa.
👉5. Sunnah ne dangin mamaci da makwabtan sa suyi abincin da zai kosar da iyalan mamacin su aika masu.
👉6. Mustahabbancin shafa kan maraya da tausaya masa.

📒NA FARKO: SHAR'ANTUWAR TA'AZIYYA A MUSULUNCI:📒

An Shar'anta yin ta'aziyya ga iyalai da dangin mamaci, saboda hadithai da suka yi bayanin haka:

📌 1. Hadithin Qurra Al-Muzanniy (R.A), cewa: a lokacin da Manzon Allah SALLAL ALAIHI WA SALLAM ya samu labarin rassuwar dandan wani daga cikin Sahabban sa, ya je yayi masa ta'aziyya har ma yace masa "MINENE YAFI SOYUWA A GAREKA? SHIN KAJI DADIN RAYUWAR KA TARE DA WANNAN YARO? KO (kafi son) KA ISKO SHI BAKIN KOFAR ALJANNA YANA JIRAN KA, YA BUDE MAKA (don ka shiga)?" sai yace: ya Annabin Allah!, nafi son ya riga ni ya bude mani. Wannan Hadithi [[Nasa'iy ya ruwaito shi da wannan siyaqi, haka kuma ibn Hibban da Hakim da Ahmad duka sun ruwaito sa. Kuma hadithin Sahihi ne.]]

📌 2. Hadithin Anas dan Malik (R.A), yace: Manzon Allah SALLAL ALAIHI WA SALLAM yace: "DUK WANDA YAYIWA DAN UWAN SA MUMINI TA'AZIYYA AKAN WATA MUSIBA, (da ta same sa) ALLAH ZAI TUFATAR DA SHI CIKAKKUN TUFAFI A RANAR ALKIYAMA WADANDA MUTANE ZASU YI FATAR SAMUN IRINSU" [Khadeeb Al-Baghdadiy ya fitar da shi da bin Asakir da kuma bin Adiy. Hadithi ne ingantcce] 

Wallahu a'alamu bissawab. 

Mu hadu a darasi na biyu (002) insha'allah. 

✍️ Nasiru Bala Bungudu. 
(Chief Imam Salih bin Abdul Aziz Juma'at Mosque Bungudu)

Wednesday, 13 January 2021

MUSAN MALAMANMU NA SUNNAH - ALOSAIMI

MUSAN MALAMANMU NA SUNNAH...


Waye Sheikh Salih  Al-Osaimi?

Shine Sheikh Dr. Swalih Bn Abdullahi bn Hamad Al-Osaimi, Al-Otaibi

An haifeshi ne a Birnin Riyadh dake Saudiyya, a watan Safar shekara ta 1391AH kuma yana zaune a garin Riyadh har yanzu.
Malam ya himmatu da neman karatu tun yana ɗan ƙarami, yayi tafiye tafiye zuwa ƙasashe masu yawa domin neman ilimi.
Malam ma'aboci sunnah ne
Yayi karatu a wurin malamai masu tarin yawa daga cikin malaman dake Saudiyya, yana da alaƙar ilimi mai ƙarfi da Sheikh Bukar Abu Zaid (R)
Malaman da yayi karatu a wurin su suna da yawa, daga ci akwai:
1. Sheikh Abdulaziz bn Baaz
2. Sheikh Muhammad bn Salihul Usaimin
3. Sheikh Abdullahi bn Aƙeel
4. Sheikh Abdullahi bn Abdulrahman jibrin
5. Sheikh Bukar Abu Zaid
6. Sheikh Salih bn Fauzan Al-fauzan
7. Sheikh Abdulmuhsin Al'abbad

@ Dr. Osaimi yayi karatu a jami'atu Ummul Ƙura, sannan yayi karatun shi tun daga matakin digiri na farko har digirin digir gir a fannin Ulumul Hadith.

@ Dr. Osaimi Mai Fatawa ne kuma limami ne mai hudubar juma'ah a Masallacin Abubakar Assiddiq dake birnin Riyadh

@ An zaɓi Dr. Osaimi a a matsayin member a majalisar manya manyan malamai dake Saudiyya a ranar 3, Rabi'ul Awwal, 1438H

@ Sheikh Swalihul Osaimi yana da halƙoƙi da yake karantawa a wurare kamar haka:
1. Yana karantarwa a Masallacin Manzon Allah S.A.W, darasin da ake kira:
برنامج مهمات العلم

2. Yana karantawa a birnin Riyadh, yana karantar da:
برنامج أصول العلم
3. Yana karantar da mahajjata kafin fara aikin hajji a Masallacin Harami, darasin da ake kira:
برنامج تعليم الحجاج 
4. Yana karantarwa a lokacin azumi a Masallacin Manzon Allah S.A.W, tun daga 1 har zuwa 20 ga Ramadan, sunan darasin
برنامج السرد المجود

Wannan kaɗan kenan daga cikin wurare da kuma Karatuttukan da yake gabatarwa, wanda adadin su zai kusan kai 18-20

Rubuce rubucen da yayi

@ Dr. Osaimi yayi wallafe-wallafe masu yawan gaske, tsakanin waɗanda ya rubuta da kanshi, da kuma waɗanda yayi ma sharhi da Takhriji suna da yawa, amma ga wasu daga cikin su:

١. ﺗﻌﻈﻴﻢ ﺍﻟﻌﻠﻢ
٢. ﺍﻟﺒﻴِّﻨﺔ ﻓﻲ ﺍﻗﺘﺒﺎﺱ ﺍﻟﻌﻠﻢ ﻭﺍﻟﺤﺬﻕ ﻓﻴﻪ
٣. ﺍﻟﻤﺴﺎﺋﻞ ﺍﻷﺭﺑﻌﻴﻦَ ﻋﻦِ ﺍﻷﺋﻤﺔ ﺍﻷﺭﺑﻌﺔ ﺍﻟﻤُﺘَّﺒﻌﻴﻦ
٤. ﺍﻟﻤُﻌﺠَﻢ ﺍﻟﻤُﺨﺘﺎﺭ ﻣﻦ ﺍﻷﺣﺎﺩﻳﺚ ﺍﻟﻨَّﺒﻮﻳَّﺔ ﺍﻟﻘِﺼﺎﺭ
٥. ﺍﻟﻘَﺮﻳﺾ ﺍﻟﻤُﺒﺪَﻉ ﻧﻈﻢ ﺍﻟﻘﻮﺍﻋﺪ ﺍﻷﺭﺑﻊ
٦. ﻣﻌﺎﻧﻲ ﺍﻟﻔﺎﺗﺤﺔ ﻭﻗِﺼَﺎﺭ ﺍﻟﻤﻔﺼَّﻞ
٧. ﺍﻟﻄُّﺮْﻓﺔ ﺍﻟﺴَّﻨﻴَّﺔ ﻓﻲ ﺍﻟﻘﻮﺍﻋﺪ ﺍﻟﻔﻘﻬﻴَّﺔ
٨. ﺧﻼﺻﺔ ﻣﻘﺪِّﻣﺔ ﺃُﺻﻮﻝ ﺍﻟﺘَّﻔﺴﻴﺮ
٩. ﺇﻣﺘﺎﻉ ﺍﻟﻤﺸﻴﺨﺔ ﺍﻷﺣﻤﺪﻳﺔ ﺑﻄﺮﻕ ﺣﺪﻳﺚ ﻓﻀﻞ ﺍﻟﻤﺮﻭﻳﺎﺕ ﺍﻻﺭﺑﻴﻌﻴﺔ - ﻃﺒﻌﺔ ﺩﺍﺭ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺤﺪﻳﺚ ﺍﻟﻄﺒﻌﺔ ﺍﻷﻭﻟﻰ 1413 ﻫـ
١٠. ﺭﻓﻊ ﺍﻟﻤﻨﺎﺭ ﻟﻄﺮﻕ ﺣﺪﻳﺚ ﻣﻦ ﺳﺌﻞ ﻋﻦ ﻋﻠﻢ ﻓﻜﺘﻤﻪ ﺍﻟﺠﻢ ﺑﻠﺠﺎﻡ ﻣﻦ ﻧﺎﺭ - ﻃﺒﻌﺔ ﺩﺍﺭ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺤﺪﻳﺚ ﺍﻟﻄﺒﻌﺔ ﺍﻷﻭﻟﻰ 1413 ﻫـ
١١. ﺍﻟﻔﺼﻞ ﺑﻴﻦ ﺍﻟﻤﺘﻨﺎﺯﻋﻴﻦ ﻓﻲ ﺣﺪﻳﺚ ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺇﻧﻲ ﺃﺳﺄﻟﻚ ﺑﺤﻖ ﺍﻟﺴﺎﺋﻠﻴﻦ - ﻃﺒﻌﺔ ﺩﺍﺭ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺤﺪﻳﺚ ﺍﻟﻄﺒﻌﺔ ﺍﻷﻭﻟﻰ 1413 ﻫـ
١٢. ﺍﻟﺪﺭﺀ ﻟﺘﺼﺤﻴﺢ ﺣﺪﻳﺚ ﻣﻦ ﺣﺴﻦ ﺇﺳﻼﻡ ﺍﻟﻤﺮﺀ - ﻃﺒﻌﺔ ﺩﺍﺭ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺤﺪﻳﺚ ﺍﻟﻄﺒﻌﺔ ﺍﻷﻭﻟﻰ 1413 ﻫـ
١٣. ﻓﻘﻪ ﺍﻟﻮﺍﻗﻊ ﻋﻨﺪ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺴﻨﺔ ﻭﺍﻟﺠﻤﺎﻋﺔ .
١٤. ﺍﻟﺪﺭﺀ ﺍﻟﻨﻀﻴﺪ ﻓﻲ ﺗﺨﺮﻳﺞ ﻛﺘﺎﺏ ﺍﻟﺘﻮﺣﻴﺪ .
١٥. ﻭﺍﻗﻌﻨﺎ ﺍﻟﻤﻌﺎﺻﺮ ﻋﻠﻰ ﺿﻮﺀ ﻣﻨﻬﺞ ﺍﻟﺴﻠﻒ .
١٦. ﻫﺬﻱ ﻫﻲ ﺍﻟﺴﻠﻔﻴﺔ : ﻣﻨﻬﺞ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺴﻨﺔ ﻭﺍﻟﺠﻤﺎﻋﺔ .
١٧. ﺍﻟﻮﻓﺎﺀ ﺑﺼﺤﻴﺢ ﺍﺫﻛﺎﺭ ﺍﻟﺼﺒﺎﺡ ﻭﺍﻟﻤﺴﺎﺀ .
١٩. ﺍﻟﺸﻜﺎﻳﺔ ﻭﺍﻟﻨﻜﺎﻳﺔ : ﺑﺮﻗﻴﺎﺕ ﻣﻮﺟﻬﺔ ﺇﻟﻰ ﻃﻠﺒﺔ ﺍﻟﻌﻠﻢ ﻭﺍﻟﺪﻋﺎﺓ .
ﺍﻻﻧﺒﺎﻩ ﺇﻟﻰ ﻣﺎ ﻟﻴﺲ ﻣﻦ ﺃﺳﻤﺎﺀ ﺍﻟﻠﻪ .
٢٠. ﺁﺩﺍﺏ ﺍﻟﺼﺤﺒﺔ ﻭﺣﻘﻮﻕ ﺍﻟﻌﺸﺮﺓ ﺑﻴﻦ ﺍﻻﺧﻮﺍﻥ .
٢١. ﺗﺬﻛﺮﺓ ﺍﻟﺤﺪﻳﺜﻲ ﻭﺍﻟﻤﺘﻔﻘﻪ .
ﺍﻻﻧﺘﻤﺎﺀ ﺍﻟﺤﻖ .
٢٢. ﻛﺸﻒ ﺍﻟﻨﻘﺎﺏ ﻋﻦ ﺿﻌﻒ ﺣﺪﻳﺚ ﻋﺎﺋﺸﺔ ﻓﻲ ﺍﻟﺤﺠﺎﺏ .
٢٣. ﺭﺳﺎﺋﻞ ﺇﻟﻰ ﺷﺒﻞ ﺍﻹﺳﻼﻡ
٢٤. ﺍﻟﻤﻔﺘﺎﺡ ﻓﻲ ﺍﻟﻔﻘﻪ
٢٥. ﺍﻟﻤﻘﺪﻣﺔ ﺍﻟﻔﻘﻬﻴﺔ ﺍﻟﺼﻐﺮﻯ
٢٦. ﺍﻟﻤﻘﺪﻣﺔ ﺍﻟﻔﻘﻬﻴﺔ ﺍﻟﻜﺒﺮﻯ
٢٧. ﺍﻟﻌﺮﻭﺓ ﺍﻟﻮﺛﻘﻰ
٢٨. ﺍﻟﻐﺎﻳﺔ ﺇﻟﻰ ﺍﻟﺴﻤﺎﻉ ﻭﺍﻟﺮﻭﺍﻳﺔ
٢٩. ﻧﻌﺖ ﺍﻟﺪﺭﺟﺎﺕ ﻟﺘﻠﻘﻲ ﺍﻟﻘﺮﺁﻥ ﻭﺍﻟﻘﺮﺍﺀﺍﺕ
٣٠. ﺗﻔﺴﻴﺮ ﺍﻟﻔﺎﺗﺤﺔ ﻭﻗﺼﺎﺭ ﺍﻟﻤﻔﺼﻞ
٣١. ﻧﺠﻢ ﺍﻟﻤﻨﺒﻬﺎﺕ ﻓﻲ ﻧﺼﺢ ﻃﻼﺏ ﺍﻟﻤﻬﻤﺎﺕ
٣٢. ﺍﻟﺤﻠﺔ ﺍﻟﺴﻴﺮﺍﺀ
٣٣. ﺭﺳﺎﻟﺔ ﺍﻟﻤﺎﺟﺴﺘﻴﺮ : ﺍﻟﻤﺘﺎﺑﻌﺎﺕ ﻭﺍﻟﺸﻮﺍﻫﺪ ﺩﺭﺍﺳﺔ ﻧﻈﺮﻳﺔ ﺗﻄﺒﻴﻘﻴﺔ ﻋﻠﻰ ﺻﺤﻴﺢ ﻣﺴﻠﻢ ﺇﺷﺮﺍﻑ ﺃ . ﺩ . ﻣﻮﻓﻖ ﻋﺒﺪ ﺍﻟﻘﺎﺩﺭ

@ Dr. Osaimi yana da usulubi mai kyau na karantarwa, yana yawan maimaita duk wata jumla mai fa'ida domin ɗalibbai su fahimci inda karatun ya nufa, kamar dai yadda Sheikh Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum (H) yake da irin wannan usulubi mai kyau a nan gida Nigeria

@Na bibiyi wasu daga cikin Karatuttukan da malam ya gabatar kuma ina fa'idantuwa kwarai da gaske, daga Karatuttukan da na bibiya akwai:
١. تفسير سورة الفاتحة وقصار المفصل
٢. الباقيات الصالحات من الأذكار بعد الصلوات لصالح بن عبد الله العصيمي
٣. شرح آداب العشرة
٤. شرح خلاصة الحسناء
٥. شرح خلاصة مقدمة أصول التفسير
٦. شرح الأرجوزة الميئية في ذكر حال أشرف البرية
Waɗannan duk na saurare su daga farko har ƙarshe kuma na fa'idantu sosai.
Haka nan na bibiyi wasu Muhadarori da malam ya gabatar kamar haka:
١. واجب طلاب العلم في النوازل والحوادث المدلهمة

٢. واجب المرأة عند الفتن

٣. الأمر باتباع السنة والتحذير من ردها
Wannan na ƙarshen na saurari muhadarar kuma na sauke littafin saboda muhimmancisa, musamman a wannan lokaci da matsiyata masu ƙaryata hadisan Annabi da sukar maruwaita.

Malam yana nan a raye har yanzu a birnin Riyadh


Allah ya ƙara mashi lafiya da tabbatuwa akan sunnar Annabi Muhammad S.A.W


✍️ Hashim Siraj Uba Ats~tsamawy
29/05/1442AH
13/01/2021AC

Monday, 20 July 2020

WASU DAGA CIKIN AYYUKAN DA AKE SON MUSULMI YA AIKATA A GOMAN FARKO NA ZUL-HIJJAH

*WASU DAGA CIKIN AYYUKAN DA AKE SO MUTUM YA AIKATA A GOMAN FARKO NA WATAN ZUL-HIJJAH*


1. *AIKIN HAJJI:* yazo a cikin bukhari da Muslim, Annabi Muhammad S.A.W yana cewa: (Aikin hajji karbabbe ba yada sakamako sai aljannah).
Abun nufi shine: idan bawa yayi aikin hajji wacce Allah S.W.T ya karba mashi, hajjin da mutum ya tattara ayukan alkhairi, lallai irin wannan baida sakamako, da falala daga wurin Allah sai shigar shi aljannah.

2. *AZUMIN RANAR ARFA:*
 Manzon Allah S.A.W yace: (Azumin ranar arfa yana kankare zunubin shekarar da ta gabata, da wacce zata zo bayanshi.

3. *YANKA ABUN LAYYA DOMIN NEMAN KUSANCI ZUWA GA ALLAH:* Abun nufi a cikin yin layya ba wai kawai cin nama da sadaka da kyauta ne ba kawai, abun nufi shine zubar da jinin dabbar domin neman kusanci ga Allah S.W.T

A karkashin wannan akwai wasu abubuwa kamar haka:
*NA FARKO:*
 Kayi kokarin ganin ka yanka abun layyarka da kanka

*NA BIYU:* idan baka yanka da kanka ba, ka tabbata kana wurin da za'a yanka, a yanka ta a gaban ka.

*NA UKU:* idan baka samu damar yankawa da kanka ba, baka samu damar da zaka tsaya a yanka a gaban ka ba, toh sai kayi umurni, ya zamana cewa an yanka da umurninka cewa a yanka maka

4. *KABBARA, DA GIRMAMA ALLAH S.W.T:*
Ya tabbata daga sahabban Annabi Muhammad S.A.W, Abi hurairah, da Abdullahi dan umar(Allah ya yarda dasu) sun kasance suna kabbarori a kwanaki goma na zul hijja.

5. *AZUMTAR KWANAKI TARA NA FARKON ZUL-HIJJAH:*
Ana son musulmi ya azumci wadannan kwanaki masu daraja, yin ayyukan alkhairi a cikin wadannan kwanaki Yana da falala da lada sosai.


Allah ya datar damu da aikata aiki na kwarai a wadannan kwanaki masu albarka.


https://t.me/muryarsunnah1



✍️ *Hashim Siraj Uba ats-tsamawy ( _ABU SINAN_ )*
atstsamawy@gmail.com

Tuesday, 14 July 2020

MAKABARTA GIDAN KOWA DA KOWA

*MAKABARTA GIDAN KOWA DA KOWA*

*LADUBBAN ZIYARAR MAKABARTA*


Godiya ta tabbata ga Allah shi kadai Wanda ya halitta rayuwa kamar yanda yaso Kuma yake karbarta a lokacin da yaso, tsira da aminci su tabbata ga Annabi Muhammad S.A.W Wanda aka baiwa zabin zaman duniya ko Kuma komawa zuwa ga Allah, ya zabi ya koma zuwa ga mahaliccinsa.

Bayan haka:

Dalilin wannan rubutun shine, kasantuwar Koda yaushe Allah yana karbar rayukan mutane, wadanda ke raye kuma suna ziyarar makabartu domin binne wadanda Allah ya karbi rayukansu, toh amma Sai naga yanzu al'ummar da muke rayuwa a cikinta mun gafala daga kabari da Kuma Azabar dake tattare dashi, wannan ne yasa naga dacewar in tunatar da yan uwana musulmi akan kabari da Kuma ziyarar shi.

*HAKURI IDAN ANYI MAKA MUTUWA*

Manzon Allah S.A.W ya wuce wasu kaburbura a wata Rana, Sai ya ga wata mata tana kuka😢 a kusa da Wani kabari, Sai Annabi S.A.W yace mata: kiji tsoron Allah, kiyi hakuri, ita wannan matar Bata San cewa Annabi S.A.W bane yake mata magana, Sai tace mashi: tafi ka kyale ni, saboda Kai musibar da ta sameni bata same ka bane don haka.
Sai Manzon Allah S.A.W ya wuce ya kyaleta, Sai ake fada mata cewa: Shifa Wanda yake maki magana Annabi ne! Sai ta tafi da sauri ta sameshi, tace: Ni bansan kai Annabi bane. Sai Annabi S.A.W yace mata:
Hakuri a lokacin mutuwa shi yafi.[Bukhari da Muslim]
Ita musiba tana bukatar hakuri, dole ne musulmi yayi hakuri idan Wani Abu na damuwa ya sameshi, Manzon Allah S.A.W ya ziyarci kabarin mahaifiyarshi, Sai yace: na nemi izinin ubangiji akan a bani dama in nema mata gafara, Amma ba'a bani izini ba, Sai na nemi izini akan ziyartar kabarinta, Sai akayi mani izini. Sai Annabi S.A.W yace: ku ziyarci kaburbura, domin suna tuna mutuwa.
 [مسلم وأبو داود]
Daya daga cikin magabata yake cewa: Idan al'amurra suka tsananta gareka, toh ka ziyarci kaburbura, domin ziyarar kabari tana tausasa zukata, tana tuna maka da lahira.
Uthman bn Affan(R.A) ya kasance idan aka ambaci Aljanna da Wuta a gabanshi baya kuka, Amma da zarar an ambaci kabari Sai ya fashe da kuka. Sai aka tambayeshi akan hakan, Sai yace: Naji Manzon Allah S.A.W yaana cewa:
Kabari shine farkon masaukin lahira, idan ka tsira daga gareshi, abunda zai biyo bayanshi yafi sauki, idan baka tsira daga gareshi ba, abunda zai biyo bayanshi yafi tsanani
  [أحمد]

Ziyarar kaburbura Yana da wasu ladubba da ya kamata musulmi ya ladabtu dasu, daga cikinsu akwai:

1. HALARTO DA NIYYA: Dole ne musulmi ya kudurce zai ziyarci makabarta ne don Allah, sannan Kuma domin ya gyara bannar da zuciyar shi ke aikatawa.

2. YIMA MAMATA ADDU'AH: Ana bukatar Mai ziyarar makabarta yayima mamatan dake kwance a cikin kaburbura addu'ah, kamar yadda Annabi Muhammad S.A.W ya koyar da sahabbanshi, addu'ar itace kamar haka:
السلام عليكم أهل الديار من المؤمنين والمسلمين، ويرحم الله المستقدمين منا والمستأخرين، وإنا إن شاء الله بكم لاحقون.
 [مسلم].

Fassarar addu'ar itace kamar haka: 
Amincin Allah ya tabbata ga ma'abota wadannan gidaje, muminai da musulmai, Allah yayi rahama ga wadannan suka Dade da mutuwa daga cikinmu da Kuma yan baya, Kuma in Allah ya yarda mu ma zamuyi tarayya daku a wannan gida

3. BA'A ZAUNAWA, KO TAFIYA AKAN KABURBURA:
Dole ne musulmi yayi kokarin ganin daina zama ko kishingid'a, ko zirga zirga a saman kaburbura, saboda fadar Annabi Muhammad S.A.W cewa: Mutum ya zauna akan garwashin Wuta, ya Kona tufafinsa, ya taba fatar jikinsa, shi yafi alkhairi gareshi akan ya zauna/ya du'ka akan/a gaban kabari
 [مسلم]

4. KARANTA ALQUR'ANI DA KUMA TAWASSALI AKAN ALLAH YA KAI LADAR GA MAMATA:
Babu laifi mutum ya karanta Wani Abu daga cikin abunda ya sawwaka gareshi na Qur'ani Mai girma, sannan ya roki Allah ya karba mashi abunda ya karanta, sannan ladar Allah ya Kai ga mamacin.

5. BAYA HALASTA TABARRUKI DA KABURBURA:
Baya halasta a nemi tabarruki da kaburbura, kamar yadda baya halasta a sumbaci kabari kamar yadda jahilai daga cikin gama-garin mutane suke aikatawa, dogaro da Hadisin da Annabi Muhammad S.A.W yake cewa: Idan zakayi roko ka roki Allah, idan zaka nemi tsari, ka nemi tsarin Allah
[الترمذي].

6. BA'A DARIYA KO WASA A MAKABARTA:
Dariya da wasa a cikin makabarta dalilai ne na kekashewar zuciya, makabarta wuri ne dake sa musulmi ya nisanci wasan tsalle tsalle da guje guje a cikinta, saboda kaburbura suna tunatar da Mai dauke duk Wani jin dadi(MUTUWA), a cikinta akwai tunani Amma ga Masu hankali daga cikin mutane.

7. YABO GA WADANDA SUKA MUTU, DA AMBATON KYAWAWAN AYYUKANSU:
Baya halasta zagin mamata, ko ambaton kurakuran su, matukar sun mutu akan musulunci,
Annabi Muhammad S.A.W Yana cewa: kada ku zagi mamata, domin su sun Rika sun riski abunda suka gabatar
 [البخاري]

A Wani Hadisin Manzon Allah S.A.W Yana cewa: kada ku ambaci matattunku Sai da alkhairi
 [النسائي]

8. BA'A SALLAH A MAKABARTA:
Annabin Rahama S.A.W yayi hani akan yin sallah a a makabarta, ko fuskantar makabarta a lokacin da mutum yake sallah, an riwaito daga Abdullahi Dan Umar (R.A) yace: Manzon Allah S.A.W yayi hani akan yin sallah a wurare guda bakwai, 1. A cikin bola(juji), 2. Kwata(Mayanka), 3. Makabarta, 4. Magamar hanya, 5. Makewayi(Toilet), 6. Wurin da ake daure rakuma, 7. Da kuma saman dakin ka'aba
[ابن ماجه]

Musulmi Yana da kyau ya Rika ziyarar makabarta, zuciyarshi zata cika da tausayi da imani, Sai kaga kana aikata ayyukan kwarai, Sai kaga Allah ya datar dakai kana yi mashi biyayya, kana lizimtar abubuwan da Allah yace ayi, kana nisantar abubuwan da Allah ya hana. Haka nan Kuma ziyarar musulmi zuwa makabarta tana sanya musulmi ya Rika tsoron wannan rayuwar ta duniya, musamman idan ya tsaya a gaban kabari tsayuwa ta dubo da tunani, kana tunanin halin da wadanda ke cikin kaburburan suke a lokacin da suna duniya, suna Kai da kawo, suna ayyuka mabanbanta, Amma fa yanzu gashi basu iya aikata komai daga cikin abubuwan da suke aikatawa a duniya, abunda zai tseratar dasu kadai ayyukansu na Alkhairi da suka aikata a duniya, sannan Sai Kai kayi tunani a karan kanka, kaima Wani lokaci zaka kasance a cikin irin wannan halin. Wannan Sai ya taimakeka wurin yin aiki na kwarai a nan duniya, domin tseratar da kanka daga azaba a ranar hisabi.


Allah muke roko daya gafartawa mamatanmu, mu Kuma idan tamu tazo Allah yasa mu cika da imani🤲🤲🤲



Dan uwanku a musulunci
✍ *ABU SINAN*
+2349030201868
atstsamawy@gmail.com

Thursday, 20 February 2020

006 ZUMUNTA A MAHANGAR SHARI'AR MUSULUNCI

🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃
*ZUMUNTA A MAHANGAR SHARI'AR MUSULUNCI*
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂

Wallafar: *Ash-Sheikh Muhammad Sani Liman Tsafe(ABU HURAIRAH)*

_006_

*بسم الله الرحمن الرحيم*

✅ *ABUBUWAN DA SUKE TAIMAKAWA WAJAN SADAR DA ZUMUNTA*

   Akwai abubuwa da yawa da suke taimakawa mutum wajan sadar da zumunta.
Ga kadan daga cikinsu kamar haka:

1. Yin tunanin manya-manyan darajoji da suka tabbata ga mai sadar da zumunta: Lallai sanin kyakykyawan sakamakon aiki da kuma hango kyakykyawan karshe dake samun mai sadar da zumunta yana taimaka maka wajen sadar da zumunta.

2. Nazari akan mummunan karshe ga mai yanke zumunta:
kula da abin da yanke zumunci yake janyowa na bakin ciki da damuwa da hasara, da nadama da sauransu, yana taimakawa mutun ya nisanci yanke zumunta ya kuma sadar da ita.

3. Neman taimakon Allah:
Wannan yana tabbata ne ta hanyar rokon Allah ya datar da kai ya kuma taimake ka bisa sadar da zumunta ga yan uwanka.

4. Maida mummuna da kyakykyawa:
  Yana daga cikin abin da yake wanzar da soyayya da kuma kiyaye zumuncin dake tsakin yan'uwa shine musanya mummuna da kyakykyawa. Karbar uzurinsu idan sun yi kuskure da kuma basu uzuri. Yana daga mafi kyawon abin da zan fada acikin wannan shine abin da ya gudana tsakanin Annabi Yusuf da yan'uwan sa, hakika sun aikata abin da suka aikata amma yayin da suka bada uzuri ya karbi uzurinsu ya musu rangwame mai kyau, bama wannan kadai ba, har addu’a yayi musu kuma ya roki Allah ya gafarta musu.

5. Yi musu rangwame da kauda kai daga aibobansu koda basu baka uzuri ba:
Wannan yana daga cikin abin da yake nuna karamcin mutum da kuma girman himmarsa, mai hankali tatacce yana yin rangwame da kau da kai daga ambaton aiboban yan'uwansa, baya ambaton laifukan su ko da kuwa basu bada uziri ba.

6. Kan-kan dakai da saukin ma’amala:
  Wannan yana daya daga cikin abubuwan da suke sanya soyayyar yan uwa ga dan uwansu kuma su kusance shi.

7. Nisantar husuma da yawan jayayya da jidali ko fada da yan uwa.

8. Barin yi masu gori da neman sai sun ran kamaka:
ya zama dole mutun ya bar yima yan'uwansa gori idan ya basu wani abu ko ya ziyarcesu, ko ya basu wata kyauta da dai sauransu.

10. Juriya da daukar duk wani aibantawa daga yan'uwa:
Lallai wannan yana daga cikin abubuwa mafi kyau, shine mutun ya kauda kai yayi hakuri da duk wata suka ko tsegumi da yan’uwansa suke mashi, saboda shedan na shige da fice don ganin ya haifar da matsala a tsakanin yan'wa.

11. Gaugawar aikawa da kyauta idan aka samu sabani a tsakanin yan’uwa:
Kyauta tana janyo Soyayya da kaunar juna, sannan kuma tana hana mummunan zato. Saboda Annabi (SAW) yace; ''KUYI KYAUTA KU SO JUNA''

12. Kwadayin kawo gyara da sulhu a tsakanin yan'uwa idan an samu sabani:
  Yana daga cikin abin da ya kamata ga duk masu hankali da natsuwa shine su yi sauri su kawo gyara da sulhu idan wata matsala ta taso a tsakanin yan'uwa, domin idan ba’ayi haka ba sharrin yana iya game kowa.

13. Gaggauta rabon gado:
Ya kamata idan aka samu rasa rai a gida na uba ko na uwa a gaggauta raba gado domin kowa ya amshi rabonshi, wannan yana kawar da rigima da yawan neman sai anraba kuma wannan yana kara dankon zumunci a tsakain yan’uwa.

14. Shirya taro na wata-wata ko shekara-shekara:
Lallai ire-iren wadannan tarukka suna dauke da alherai masu yawa domin a nan ne za’a san juna a sadar da zumunta ga juna, a yima juna wassiya da dai sauransu.

15. Kaddamar da gidauniya ko kafa asusu:
  Yana daga cikin abin da ke karfafa zumunta, shine samar da gidauniya ko wani asusu da za'a rika tara kudi duk wata ko shekara domin tallafawa yan'uwa. Da wannan gudunmawa da aka bada za'a iya tallafawa yan'uwa idan wasu matsaloli sun tunkaresu.

16. Kwamitin masu bada shawara:
  Yana da kyau a samar da kwamito ta wadanda zasu rika bada shawara a karkashin kwamitin zumunta, kamar kwamitin ilimi, Kwamitin sulhu, da sauransu. Ta haka ne kowa zai san hakkinsa da kuma hakkin yan'uwansa a kansa.
17. Kula da halayensu da ba kowa matsayinsa:
  Akwai daga cikin yan'uwa wanda yake yarda da kadan daga sadarwar da akayi masa, koda a shekara za’a ziyarceshi sau daya, koda ta wayar salula ne, wani ma ko da sakin fuskane da kuma Magana. Akwai wanda bai yarda da komai sai ziyara ako da yaushe. Duka wadannan a kula dasu saboda zumunta ta tabbata.

18. Sadar da zumunta don Allah:
  Zumunta Ibada ce mai girma don haka ana sadar da ita ne don Allah shi kadai bashi da abokin tarayya, kamar yadda Allah (SWT) yake fada: ''KUJI TSORON ALLAH DA KUKE ROQON JUNA DASHI, KUMA KU KIYAYE ZUMUNTA. [Nisa'i aya ta 1]
Hakikanin mai sadar da zumunta don Allah shine mai sadar da zumuntar sa ga yan uwanshi ko sun sadar mashi ko basu sadar mashi ba, kamar yadda Bukhari ya ruwaito cikin sahihin littafinsa, manzon Allah (SAW) yana cewa: ''BAI ZAMA MAI SADAR DA ZUMUNTA BA, WANDA SAI AN SADAR MASHI SANNAN YA SADAR, HAKIKANIN MAI SADAR DA ZUMUNTA SHINE WANDA IDAN AN YANKE MASHI SAI YAYI KOKARIN SADARWA''.  [Bukhari 5991]

A NAN ZAMU DAKATA SAI A LOKACI NA GABA INSHA ALLAHU

DOMIN CIGABA DA SAMUN WANNAN RUBUTU KUNA IYA AIKEWA DA SAQON WHATSAPP ZUWA GA: +2349030201868 DOMIN SHIGA GROUP DIN *MU KYAUTATA NIYYA*

#ABBAN_SINAN

https://fb.me/abbansinan

Sunday, 9 February 2020

SUJADAR SAHU A SALLAH

*LIMAN NE YAKE SALLAH DA MUTANE, SALLAH MAI RAKA'A HUDU, BAYAN YA DAGO DAGA SUJADA TA BIYU A RAKA'A TA UKU SAI YA ZAUNA YANA ZATON A RAKA'A TA HUDU YAKE, SAI MAMU SUKAYI MASHI TASBIHI DA SAURI, SAI YA TASHI ZUWA RAKA'A TA HUDU DA SAURI, BAYAN WANCAN ZAMAN DA YAYI DAN KADAN(KAMAR ZAMAN JALSATIL ISTIRAHAH) ZAIYI SUJUDUS SAHAWY NE KO KUWA?*

*_AMSA_*

Idan liman ya zauna a Raka'a ta uku da mantuwa, zaiyi sujada biyu(kafin sallama). Saboda fadar Manzon Allah S.A.W cewa:
لكل سهو سجدتان
Ko wace mantuwa tana da sujada biyu, *Imamu Ahmad da Abu Daud suka fitar da hadisin*

Ibn Qudama Al-maqadisy(RH) a cikin *AL-MUGNY* yace: _Idan Liman ya zauna ba a wurin da ake tahiya ba kwatankwacin *JALSATIL ISTIRAHAH,* zaiyi sujada (kafin Sallama), duka dayane, koda zamu fadi cewa jalsatil istirahah Sunnah ce a cikin Sallah,(ko bamu ce ba) domin shi Mai sallar baiyi nufin cewa jalsatil istirahah yayi ba, yayi nufin waninta(zaton cewa Yana tahiya ta karshe ne) kenan ta zama mantuwa, koda bai yi sujada biyu kafin Sallama ba, sallar shi tayi, domin wani aiki ne yayi Dan kadan a cikin Sallah, shi Kuma aiki Dan kadan bai bata Sallah...._

Haka idan kuka duba a cikin:
كشاف القناع (1/395)
Ya kawo kwatankwacin wannan maganar, ya Kara da hadisin Abdullahi Dan Masa'ud dake cikin Muslim cewa:
فإذا زاد الرجل أو نقص في صلاته فليسجد سجدتين
Idan mutum yayi Qari ko ragi a cikin Sallah zaiyi sujada guda biyu.

Ash-Sheikh Muhammad bin Salih Almunajjid(Hafizahullah) yake cewa:
لكن إذا لم يسجد الإمام للسهو، ظنا منه أنه لا يلزمه السجود، أو نسيانا منه للسجود، فصلاته صحيحة.
Sai dai, idan Liman baiyi sujadar sahawun ba, ko yayi tunanin cewa ba dole bane sai yayi sujadar, ko Kuma ya manta, sallar shi ingantatta ce.

Wannan shine abin da yake na dai dai.

Allah yayi Mana muwafaqa a cikin Kyawawan ayyukan mu

#ABBAN_SINAN
+2348064734911
+2349030201868

Thursday, 30 January 2020

004 ZUMUNTA A MAHANGAR SHARI'AR MUSULUNCI

🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃
*ZUMUNTA A MAHANGAR SHARI'AR MUSULUNCI*
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂

Wallafar: *Ash-Sheikh Muhammad Sani Liman Tsafe (ABU HURAIRAH)*

_004_

*بسم الله الرحمن الرحيم*

✅ *SABUBBAN DA KE JANYO YANKE ZUMUNTA.*

   Idan kayi nazari akan sabubban dake janyo yanke zumunta zaka samu cewa akwai sabubba masu yawa. Ga kadan daga cikinsu
1. *JAHILCI:* Jahiltar mummunan sakamakon da mai yanke zumunta yake samu anan duniya da lahira, ko kuma rashin yin aiki da abin da mutum ya sani. An karbo daga Umar (R) ya kasance akan mimbari yana cewa: ku nemi sanin dangantakarku, sannan ku sadar da zumuntarku wallahi! Lallai zai kasance tsakanin mutum da dan uwansa wata rigima ta hadasu saboda rashin sanin juna, da yasan akwai zumunta tsakaninsu da wannan dalilin na alakar zumunta ya hanashi cin mutuncinsa *(Bukhari, Adabul mufrad 73)*

2. *KARANCIN TSORON ALLAH;*
  Idan tsoron Allah yayi rauni sannan addini yayi saku-saku ba zai damu ba idan ya yanke abin da Allah yayi umarnin asadar, kuma baya kwadayin ladar da ake samu idan an sadar da zumunta kuma baya tsoran mummunan sakamakon da zai same shi a dalilin yanke zumunta.
An karbo daga sa’id bn sam’an, yace: Naji Abu Hurairah yana neman tsarin Allah daga shugabancin yara da wawaye (jahilai) sai aka ce masa mine ne alamar yin haka? sai yace dan za’a dinga yanke zumunta a kuma dinga yin da’a ga mai halakarwa a saba ma mai shiryarwa *(Adabul-mufad 66)*

3. *GIRMAN KAI;*
  Sashen mutane idan mutum ya samu wani matsayi babba ko ya samu wata daukaka ko kuma ya zama babban dan kasuwa sai yayi girman kai ga yan'uwanshi, ya kyamaci ziyartarsu, kuma ya kyamaci zuwa garesu, yana ganin shi ke kan gaskiya kuma shi ya can-canta a ziyarta.

4. *YANKEWA MAI TSAWO;*
A nan akwai wanda yake yanke ma yan'uwansa lokaci mai tsawo al’amarin ya dore akan haka har ya kai ga yanke zumuntarshi dasu gaba daya, har ya saba da yankewa sai yayi nesa dasu. An karbo daga Mikdam, lallai yaji manzon Allah (SAW) yana cewa lallai Allah yana maku wasiyya da iyayenku mata sannan yana maku wasiyya da iyayenku maza, sannan yana maku wasiyya da yan'uwanku *(Adabul mufrad 60)*

5. *AIBANTAWA MAI TSANANI;*
Sashen wasu mutane idan dan'uwansu ya ziyarcesu bayan a baya ya yanke zumuntarshi dasu lokaci mai tsawo sai su yawaita zar ginshi har zargin yayi tsanani wanda wannan sai yasa shi kaurace masu saboda tsoron mummunan zargi da suke mashi.

6. *DORA MA RAI NAUYIN DAYA WUCE QA’IDA;*
A nan akwai wanda idan dan'uwansu ya ziyarcesu sai su dora ma kansu yin hidindimu da suka wuce karfinsu domin su ga cewa sun karrama dan'uwan nasu sama da karfinsu ko karancin abun hannunsu, wannan shi ke sanya yan'uwan nasu su dinga takaitawa da ziyartarsu domin tsoron kada su dora masu ire-iren wadannan nauye-nauyen. Saboda Annabi yace mafi karancin sadar da zumunci shine sallama mafi girman zumunta shine  sadarma wanda ya yanke maka.

7. *KARANCIN KULA DA WADANDA SUKA KAWO MAKA ZIYARA;*
  Akwai daga cikin mutane wanda idan yan'uwanshi suka ziyarceshi baya bayyanar da farin cikinsa akan ziyarar, bai tsayawa ya tattauna dasu ko ya sakar masu fuska, sai dai za ka ga yana bata rai yana kyamarsu, wannan yana zama sanadin yan'uwa ba zasu kara ziyartarshi ba dan tsoron irin wannan wulakancin.
Manzon Allah yace, kada ku wulakanta wani abu na alkhairi ko da sakin fuskane idan ka hadu da dan'uwanka.

8. *TSANANIN ROWA;*
  Wasu daga cikin mutane idan Allah ya azurtasu da dukiya mai yawa ko wani matsayi zaka same su suna gudun yan'uwansu, ba wai dan girman kai ba a'ah! Domin jin tsoron kada yan'uwan suyi amfani da wannan damar domin bayyanar da bukatunsu zuwa garesu, ko kuma domin kada ya temakesu. Maimakon ya basu dama idan sun ziyarceshi yakarbi bakuncinsu, ya yalwata masu, yayi masu hidima gwargwadon halinsa,ko kuma ya basu uzuri akan abin da ba ya da ikon yi masu amma sai kaga yana kauda kansa, yana kaurace masu domin kada su rokeshi kamar yadda yake riyawa. Mine ne amfanin dukiya ko matsayi da mutum zai samu idan har zai haramta ma yan'uwansa amfana da ita.
9. *JINKIRIN RABON GADO;*
Hakika zaka samu wasu daga cikin mutane suna jinkirta rabon gado kodai  domin kasala, ko kuma wani daga cikin magadan yana da wani mummunan kuduri game da yan'uwansa ko makamacin haka.
Duk lokacin da aka jinkirta rabon gado to kiyayya da adawa zata watsu tsakaninsu domin idan wannan yana da hali ko yafi karfin gadon wani shi kuma yana bukatar raba gadon domin bashi na shi kason ya samu ya bude kasuwanci ko makamanci haka.

10. *MUTUWAR AUREN ZUMUNCI;*
  Hakika mutuwar auren zumunci yana haifar da matsaloli a tsakanin yan'uwa na bangaren miji dana bangaren mata musamman in akwai 'ya'ya a tsakaninsu ko kuma saboda wasu matsaloli da suka shafi sakin auren.

A NAN ZAMU DAKATA SAI A LOKACI NA GABA INDA ZAKUJI CIGABAN *SABUBBAN DAKE JANYO YANKE ZUMUNTA*

DOMIN CIGABA DA SAMUN WANNAN RUBUTU KUNA IYA AIKEWA DA SAQON WHATSAPP ZUWA GA: +2349030201868 DOMIN SHIGA GROUP DIN *MU KYAUTATA NIYYA*

#ABBAN_SINAN
https://fb.me/abbansinan

003 ZUMUNTA A MAHANGAR SHARI'AR MUSULUNCI

🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃
*ZUMUNTA A MAHANGAR SHARI'AR MUSULUNCI*
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂

Wallafar: *Ash-Sheikh Muhammad Sani Liman Tsafe (ABU HURAIRAH)*

_003_

*بسم الله الرحمن الرحيم*

✅ *HADARIN  DA KE CIKIN YANKE ZUMUNTA*

Hakika Allah (SWT) da manzonsa (SAW) sun tsoratar dangane da hadarin yanke zumunci, suka sanya matsayin yanke zumunci dai dai da Fasadi/barna a bayan kasa.
Allah (SWT) yace to shin kuna fatan idan kun juya daga (umarnin) zakuyi barna a cikin kasa, kuma ku yanke zumuntarku? Wadannan sune wadanda Allah ya la'anesu, kuma ya kurmantar dasu, kuma ya makantar da ganinsu. *(Suratu Muhammad 22-23)*

An karbo hadisi daga Aisha (R) manzon Allah (SAW) yace zumunta tana rataye da al’arshin Allah. Tana cewa wanda ya sadar dani Allah ya sadar dashi, wanda ya yanke ni Allah ya yankeshi *(Muslim 2555)*
An karbo daga MUD’IM (R) manzon Allah (SWA) yace mai yanke zumunta baya shiga Aljanna *(Muslim 2556)*
Haka nan kuma, an karbo  daga Abubakrata, Manzon Allah yace, Babu wani laifi daya can-canta Allah ya gaggauta ma ma'abocin sa uquba tun anan duniya tare da  cewa yayi mashi tanadin uqubar a lahira kamar wanda ya yanke zumunta da kuma azzalimi *(Bukhari adabul mufrad 67)*
An karbo daga Abu Huraira; lallai wani mutum yace ya manzon Allah lallai ni ina da yan'uwa kuma ina sadar da zumuntarsu amman suna yanke mani, ina kyautata masu amma suna munana mani, ina yin hakuri dasu amma suna jahiltata? Sai Annabi yace, idan har ka kasance kamar yadda ka fada to lallai kamar kana zuba masu toka ce mai zafi, Allah ba zai gushe ba yana taimakonka akansu matukar ka dauwwama akan haka *(Muslim 2558)* Ma’ana: kamar kana ciyar dasu toka mai zafi saboda abin da suke haduwa dashi na laifi.
Haka nan kuma an karbo daga Abdullahi ibn Amru binul As, Manzon Allah (SAW) yace, bai zama mai sadar da zumunta ba wanda yake so aranka mashi, sai dai mai sadar da zumunta shine wanda idan an yanke mashi, shi yana sadarwa *(Bukhari 541)*
An karbo daga salmanu ibn Amir, Manzon Allah yace, yin sadaka ga miskinai sadakace kamar sauran sadakoki, amma yin sadaka ga dan'uwa tana da darajoji biyu (2) ladar sadaka da kuma ladar sadar da zumunci *(Abu Dawud 2555 da Tirmidhi 658)*
An karbo daga Abu Hurairah yace, lokacin da wannan ayar ta sauka,,, kayi gargadi ga yan'uwanka makusanta, Annabi (SAW) ya kira Quraishawa, suka hadu gaba dayansu, yayi musu wa’azi gaba dayansu kuma yayi ma dai-dai kunsu yace ya Fatima ki tsamar da kanki daga wuta, lallai ni bani wadatar daku a wurin Allah da komai sai dai lallai kuna da wata zumunta da sannu zan sadar da ita *(Muslim)*

ANAN ZAMU DAKATA SAI A LOKACI NA GABA INDA ZAKUJI *SABUBBAN DAKE JANYO YANKE ZUMUNTA*

DOMIN CIGABA DA SAMUN WANNAN RUBUTU KUNA IYA AIKEWA DA SAQON WHATSAPP ZUWA GA: +2349030201868
DOMIN SHIGA GROUP DIN *MU KYAUTATA NIYYA*

#ABBAN_SINAN
https://fb.me/abbansinan

KARATUTTUKAN MASALLACIN ABU HURAIRAH TSAFE

*MASJID ABU HURAIRAH TSAFE*

Wannan Masallaci karkashin kwamitin social media na masallacin sunyi kokarin tattara karatuttukan da *Ash-Sheikh Muhammad Sani Liman Tsafe (ABU HURAIRAH)* yake gabatarwa a wannan Masallaci har kusan littafai *36* gasu kamar haka:

1. *Aqeedatud dahawiyya*

2. *Ahkamul idaini*

3. *Alfurqan baina auliya'allahi wa'auliya'ish-shaidan*

4. *Ahkamul uduhiyya*

5. *Al'imamu wa'af'alihi*

6. *Al'ilmam, bi'ahkami wadabus siyam*

7. *Aljawabul khafi*

8. *Alwajibatul mutahattimatul ma'arifah.*

9. *Bugyatul mushtak*

10. *Bulugul maram*

11. *Daura- akan Magunguna da ruqya*

12. *Daura- akan Maulidi*

13. *Hisnul Muslim*

14. *Hiqbatun minat-tarikh*

15. *Hudubobi guda 166*

16. *Imani haske*

17. *La'ilaha ilallah*

18. *Manasikul hajji*

19. *Mayatamayyazu bihil muslimu anil mushrik*

20. *Mu'amalatul hukkam*

21. *Muhadarori*

22. *Nabiyur Rahma*

23. *Qa'idatul jalila*

24. *Ru'usul aqlam*

25. *Riyadus saliheen*

26. *Ramadhan Tafseer, 2007,10,13,16,17,18, da 2019*

27. *Salatut Tarawih*

28. *Sahihul bukhari*

29. *Shama'ilul Muhammadiyya*

30. *Sifatu saumun Nabiyy, kala biyu*

31. *Tarbiyatul aulad, kala 3*

32. *Tafseer weekly na ibn Katheer*

33. *Tuhfatul iraqiyya*

34. *Usulul iman*

35. *Usulus salasa*

36. *Wasiyyatul kubrah*

37. *Aqeedatul wasidiyya na (ibn taimiyya).*

38. *Adabuzzifaf na (Albany)*

39. *Fadlul Islam na (Muhammad bn abdulwahab)*

40. *Nawaqidul Islam na(Muhammad bn Abdulwahab)*

41. *kitabuttauhid na (Muhammad bn abdulwahab)*

42. *kitabuttauhid na (sheikh salhul fauzan)*

43. *Albida'ah*

44. *Sharhin sunnah na (Barbahary)*

45. *Kama takunu yuwalla alaikum na (dr. Ramadani)*

46. *Jilbabul m ar'atil Muslima na (Albany)*

47. *Huququn da'at ilaiha fidra waqarrarat'ha shari'a na(sheikh uthaimin)*

48. *Siyamu Ramadan*

49. *Qiyamu Raman.*

50. *Ahkamul jana'iz na (Albany)*

51. *Tafsirul kalimatul shahada.*

52. *Sifatus salatin nabiyy na (Albany)*

53. *Sharhi masa'ilil  jahiliyya na (Muhammad bn Abdul wahab)*

54. *Auradu ahlussunah.*

55. *Tabyini kazibul muftary bima nusiba ila ibn taimiyya na (M Kabir Maru).*

zamu cigaba da kawo wadan da muka tuna  daga baya insha Allahu

Wannan kwamiti na Nan na kokari kafin zuwa Ramadan za'a gabatar maku da 16GB memory card Mai dauke da Wadannan karatuttukan da ma wasu wadanda bamu shigar ba a Nan.

Allah ya sakawa Malam da Alkhairi

#MABUHURAIRAHTSAFE_SOCIAL_MEDIA

005 ZUMUNTA A MAHANGAR SHARI'AR MUSULUNCI

🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃
*ZUMUNTA A MAHANGAR SHARI'AR MUSULUNCI*
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂

Wallafar: *Ash-Sheikh Muhammad Sani Liman Tsafe (ABU HURAIRAH)*

_005_

*بسم الله الرحمن الرحيم*

✅ *CIGABA DA BAYANI AKAN SABUBBAN DA KE JANYO YANKE ZUMUNTA.*

11. *NISAN WURIN ZAMA DA KUMA KASALAR ZUWA ZIYARA*
Akwai daga cikin mutane wadanda idan gidan su ko garin su yana nesa sai a dinga jin kasalar zuwa ziyartarsu, wanda wannan sai ya nisantasu da yan'uwansu.
Nisan wuri bai kamata ba ya zama dalili na yanke zumunta, musamman wannan zamanin da ake da hanyoyin sadarwa daban daban, Allah ya bamu ikon kulawa da zumunta.

12. *MAKWABTAKA A TSAKANIN YAN UWA*
Da yawa Makwabtaka tana gadar da yankewar zumunta a tsakanin yan'uwa. Umar Dan khaddab yace ku umurci yan'uwanku su dinga ziyartar yan'uwansu amma kada suyi makwabtaka da juna a gidajensu, sannan sau dayawa kusanci a tsakanin gidajen yan'uwa yana haifar da sashen wasu matsaloli wadanda suke haifar da fada a tsakanin 'ya'yansu wanda wannan yakan zarce har zuwa ga iyayensu sai wannan ya haifar da gaba da yanke zumunci a tsakaninsu.

13. *KARANCIN KAUDA KAI DA HAKURI A KANSU:*
Sashen wasu mutane suna da karancin kauda kai da kuma hakuri akan abin da yan'uwansu suka yi masu. Wasu yan'uwan da an samu sabani tsakaninsu ko wani kuskure da ya afku sai su yanke zumunta, su kaurace ma yan'uwansu.

14. *HASSADA:*
   Akwai daga cikin yan’uwa wanda Allah yake azirtawa da ilimi ko wani babban matsayi ko dukiya mai yawa sai ka same shi yana yima yan'uwansa hidima yana kyautata ma su, sannan ka samu sashen yan'uwansa suna nuna masa hassada da kiyayya da haifar da rikici tsakanin shi da su, suna cewa duk abin da yake yi masu ba domin Allah yake yi ba.

15. *YAWAN WASA:*
Lallai yawan wasa (da sunan wai abokin wasa) yana haifar da mummunan abu a tsakanin yan'uwa domin wani yana iya fadar kalma mai muni ga dan'uwansa ba tare da ya kula da hadarinta ba agare shi, wannan sai ya gadar da kiyayya da gaba a tsakaninsu a sanadiyyar wannan Kalmar.

16. *ANNAMIMANCI DA KARBAR GULMA:*
Akwai da yawa daga cikin yan'uwa wadanda dabi'arsu shine yawo da annamimanci a tsakanin yan'uwa domin su kawo rabuwar kai da gurbata tsakanin yan’uwa wanda wannan yana gadar da yanke zumunta, sai dai abu mafi muni shine karbar gulma da yadda da ita shi ke haifar da yankewar zumunta.

17. *SHAGALTUWA DA DUNIYA:* Shagaltuwa da duniya da son yawan tara abin duniya yana hana mutun sadar da zumunta, da kuma samun lokacin ziyartar yan'uwansa da nuna soyayyar shi zuwa gare su.

18. *MIYAGUN HALAYE NA MATAR SHI:*
Wasu daga cikin mutane ana jarabtarsu da muguwar mata mai mummunan dabi’a mai yawan sukar yan'uwansa, bata son yayi mu’amala da yan'uwansa ko wasu, tana dogewa wajan ganin ta raba shi da yan'uwansa tana hana shi ziyartarsu, da sadar da zumunta zuwa garesu, idan yan uwan sa suka ziyarceshi sai tayi ta fushi tana murtike fuska. Bugu da kari akwai mazajen da suke mika ragamar zumuncinsu ga matarsu sai wanda ta yarda dashi yake sadarmawa, wanda bata yarda da shi ba sai ya yanke ma sa.

19. *MANTAWA DA WASU YAN'UWA A LOKACIN WALIMA KO WATA HIDIMA:*            Hakika wani daga cikin yan'uwa yakan shirya walima ko wata hidima ya gayyaci yan'uwansa sai ya manta da wani ko wasu, sai su da ba’a gayyata ba su munana masa zato, su nuna kamar an wulakantasu an zabi wasu wadanda suka fisu, wannan  nasa ya kaurace masu da yanke zumunta a tsakaninsu.
Wadannan sune  kadan daga cikin abubuwan dake janyo kauracewa juna da kuma yanke zumunta. Ya kamata a basu kulawa ta musamman da hattara da fadawa cikinsu.

A NAN ZAMU DAKATA SAI A LOKACI NA GABA INDA ZAKUJI *ABUBUWAN DA SUKE TAIMAKAWA WAJAN SADAR DA ZUMUNTA*

DOMIN CIGABA DA SAMUN WANNAN RUBUTU KUNA IYA AIKEWA DA SAQON WHATSAPP ZUWA GA: +2349030201868 DOMIN SHIGA GROUP DIN *MU KYAUTATA NIYYA*

#ABBAN_SINAN

https://fb.me/abbansinan

LADUBBAN NEMAN ILIMI DA BADA ILIMI

*KWAMITIN HARKOKIN ADDINI DA ZAMANTAKEWA NA MASALLACIN ABU HURAIRAH TSAFE*

*LADUBBAN NEMAN ILIMI DA BADA ILIMI*

✅ *IKHLASI:*
yi don Allah, mai neman ilimi da malamin dake bada ilimi ya zama dukan su sunayi don Allah, domin neman yaddar Allah. Rasulullahi (S.A.W) yace "Duk wanda ya nemi ilimi don neman yaddar Allah, daga baya ya canza niyarsa don neman duniya, ba zaiji kanshin Al-Janna ba" *(Abu Dawuud: 3664)*

✅ *NIYYAR DAUKE JAHILCI:*
  Duk wanda zai nemi ilimi ko zai bada ilimi ya zamanto don ya dauke ma kansa jahilci da waninisa. Imam Ahmad Bin Hambali Yace "Shi ilimi babu abun dake dai-dai dashi ga daraja musamman ga wanda ya kyautata niyar sa". Dalibansa sukace kamar yaya? Yace "Wanda yayi da manufa (Niyar) ya dauke makansa jahilci ko waninsa"

✅ *NEMAN ILIMI DA MANUFAR KARE ADDINI:*
  Ya kamata ga mai bada ilimi ko dalibi ya kasance da manufar ba addini kariya ya keyi, Rasulullahi (S.A.W) yace: "Yaku wanda sukayi imani ku kasance masu taimakon addinin Allah, *Q: Suratul Saffi;14".*

✅ *AIKI DA ILIMI:* Na daga cikin ladubban ilimi ga malami da dalibi aiki da  ilimi Rasulullahi (S.A.W) yace Alqur'ani hujjane gareka ko akan ka” *(Muslim: 223)* hujjane gare ka in kayi aiki dashi kashiga Aljanna. Akan ka in bakayi aiki dashi ba ka shiga wuta.

✅ *HAKURI:*
Dole ne malami da mai neman ilimi suyi hakuri: malami yayi hakuri wajen bada ilimi, dalibi yayi hakuri wajen neman ilimi. Hakuri kan neman ilimi ya kasu gida ukku (3):

1. Hakuri da talauci da yinwa

2. Hakuri akan dagewa har sai ka samu

3. Rashin yanke kauna ga abin da kake nema

Imam Ahmad bin Hambali yace Na shekara tara (9) ina karatun *Kitabul Haid* har saida na gane shi

✅ *TAWALIU DA NISANTAR GIRMAN KAI:*
Ana son malami da dalibi su sanya tawali'u da nisantar girman kai ga abin da suke nema. Imam Mujahid yace Mai girman kai ko mai kunya baya samun ilimi.

✅ *TAFIYA DON NEMAN ILIMI:*
Wajibi ne ga malami ko dalibin ilimi da suyi tafiya don neman ilimi musamman ilimin da babu a  inda suke. Rasulullahi (S.A.W) yace Neman ilimi wajibine ga dukkan musulmi” *(Muslim)*

✅ *RASHIN KARBAR ILIMI GA DAN BIDI'AH:*
Bai halitta ga dalibi ya nemi ilimi ga dan bidi'ah, yan bidi'ah sune wadanda suke saba ma gaskiya kuma suka kirkira abubuwan da musulunci bai zo dasu ba, kamar: Yan shi'ah, Khawarij, da sauran darikun Sufaye.
Muhd Bin Sirin yace: Kada ku kuskura ku zauna da yan bidi'ah kada kuyi karatu garesu kar ku sauraresu domin Ahlis-sunnah sunyi ittifaki a kaurace masu da kuma nesa dasu”.

Allah ya bamu ilimi Mai amfani Kuma Mai albarka 🤲🤲🤲

*MASJID ABU HURAIRAH TSAFE SOCIAL MEDIA COMMITTEE*
+2348064734911
https://fb.me/masjidabuhurairahtsafe