Wednesday, 26 December 2018

HUKUNCIN HADE SALLOLI A LOKACIN TAFIYA

🔸🔸🔸🔸🔸🔸🔸🔸🔸🔸
*HUKUNCIN HADE SALLOLIN AZUHR DA LA'ASAR KO MAGRIB DA ISHAA A LOKACIN TAFIYA*
🔹🔹🔹🔹🔹🔹🔹🔹🔹🔹

Dukkan godiya ta tabbata ga Allah s.w.t, Tsira da Amincin Allah su kara tabbata ga farin jekada Annabi Muhammad s.a.w da iyalan gidansa da sahabbansa da duk Wanda ya biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.

_Bayan haka:_

Maganganu sun yawaita akan wannan matsalar ta inda zaka samu daliban ilimi kullum cikin rigima muke da junanmu akan wannan matsalar, wannan yace GA abunda malaminshi yace shima dayan sai ya kawo maganar shugaban islamiyyarsu, wannan duka yana faruwa ne imma a haduwar mota ce ko a campuses na manyan makarantu, wannan shine dalilin da yasa nabi malamai domin nayi rubutu akan wannan matsalar, nima kuma zan kawo maganganun mai gidana *Manzon Allah s.a.w,* sai dai tunda ance matsala ce da ta shafi daliban ilimi inaga ba dole sai an bude komai ba, za'a Dan haska fitila ne kadan sai mutum yayi dogon hange kafin hasken ya dauke.

Allah yayi mana jagora.

Hadisi ya tabbata daga Manzon Allah s.a.w, hadisin da Abdullahi Dan Abbas R.A ya ruwaito cewa:
كَان
َ رَسُولُ اللَّهِ صلى الله عليه وسلم يَجْمَعُ بَيْنَ صَلاةِ الظُّهْرِ وَالْعَصْرِ , إذَا كَانَ عَلَى ظَهْرِ سَيْرٍ , وَيَجْمَعُ بَيْنَ الْمَغْرِبِ وَالْعِشَاءِ .
Wannan hadisi ne sahihi da karara yake nuna mana cewa Manzon Allah s.a.w yana hade salloli.

Idan baka fahimci wannan hadisin ba, toh ga wani Wanda Anas Dan maliku R.A ya ruwaito yace:

كان رسول الله صلى الله عليه وسلم إذا ارتحل قبل أن تَزيغ الشمس أخّر الظهر إلى وقت العصر ثم نزل فجمع بينهما ، وإذا زاغت قبل أن يَرْتَحِل صَلَّى الظهر ثم ركب . رواه البخاري ومسلم .
Tirkashi kaji hadisi daga littafan da malamai kecewa sune mafi girman littafai bayan Qur'ani wato(SAHIHUL bukhari da Muslim), kunji fa Manzon Allah s.a.w idan ya daura aniyar tafiya kafin rana ta kawo(wato kafin lokacin sallar azuhr) yana jinkirta azuhr zuwa lokacin sallar La'asar, sannan sai ya sauka ya hade sallolin, idan kuma lokacin sallar azuhr yayi kafin ya fara tafiya yana yin azuhr kawai sai ya fara tafiya.

Ga hadisin mu'az bin jabal R.A a gazwati tabuka yake cewa:

أَنَّ رَسُولَ اللَّهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ كَانَ فِي غَزْوَةِ تَبُوكَ إِذَا زَاغَتْ الشَّمْسُ قَبْلَ أَنْ يَرْتَحِلَ جَمَعَ بَيْنَ الظُّهْرِ وَالْعَصْرِ ، وَإِنْ يَرْتَحِلْ قَبْلَ أَنْ تَزِيغَ الشَّمْسُ أَخَّرَ الظُّهْرَ حَتَّى يَنْزِلَ لِلْعَصْرِ ، وَفِي الْمَغْرِبِ مِثْلُ ذَلِكَ ؛ إِنْ غَابَتْ الشَّمْسُ قَبْلَ أَنْ يَرْتَحِلَ جَمَعَ بَيْنَ الْمَغْرِبِ وَالْعِشَاءِ ، وَإِنْ يَرْتَحِلْ قَبْلَ أَنْ تَغِيبَ الشَّمْسُ أَخَّرَ الْمَغْرِبَ حَتَّى يَنْزِلَ لِلْعِشَاءِ ثُمَّ جَمَعَ بَيْنَهُمَا . رواه الإمام أحمد وأبو داود والترمذي .

Kunga shima wannan hadisin yana tabbatar muna da halascin hade salloli biyu a lokacin tafiya.

A wannan hadisin sai imamut tirmidhi yake cewa;

وبهذا الحديث يقول الشافعي ، وأحمد وإسحاق يقولان : لا بأس أن يَجمع بين الصلاتين في السفر في وقت إحداهما .
Kundai ji, a wurin su imamush shafi'i da imamu Ahmad da ISHAQ bin rahwiyya dukkansu sunce babu laifi a hade salloli biyu a lokacin daya, idan ana cikin tafiya.

Wancan hadisin da ya gabata na tabuka, imamu Muslim ya ruwaitoshi da wani lafazi kamar haka;

خَرَجْنَا مَعَ رَسُولِ اللَّهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ عَامَ غَزْوَةِ تَبُوكَ ، فَكَانَ يَجْمَعُ الصَّلاةَ ، فَصَلَّى الظُّهْرَ وَالْعَصْرَ جَمِيعًا ، وَالْمَغْرِبَ وَالْعِشَاءَ جَمِيعًا .
A riwayar Muslim hade sallolin sai ya bayyanar mana da riwayar Imamu Ahmad da tirmidhi da Abi daud da ta gabata.

Abu na gaba shine addinin Allah sauki gareshi, tunda Allah yayiwa matafiyi rangwame akan ya ajiye *azumi* saboda kada ya wahala, ai banga abun rikici ba akan hade salloli, ana zaune gida ma akwai wasu dalilai da suna iya sa a hade salloli.
Hade salloli ga matafiyi ya kasu gida biyu;
1. تقديم
2. أو تأخير

Wato yin sallar azuhr da la'asar a lokacin azuhr ko yin sallar azuhr da la'asar a lokacin la'asar, sai dai dole idan zakayi taqdeem ko ta'akheer sai kayi niyya, ma'ana idan zakayi ta'akheer, dole sai kayi niyya kafin fitar lokacin sallar farko(azuhr)

Abu na gaba shine;

*DAGA KILOMETERS NAWA NE KASARU KE KAMAWA???*

TIRQASHI!!!

Wannan itace matsalar da nafi cin karo da ita a tsakaninmu dalibai yan islamiyya, Wanda kowa na ganin shi malamin kanshi ne, tare da ta'assubanci ga wani malami ko mazhaba, a karkashin wannan zan kawo wata gamsassar magana da Sheikhul Islam ibn Taimiyya ya kawo akan wannan matsalar Wanda ina kyautata zaton zata gamsar da duk wani mai Neman gaskiya akan wannan matsalar, Sheikhul Islam ibn taimiyya yake cewa;
فالفرق بين السفر الطويل والقصير لا أصل له في كتاب الله ولا في سنة رسوله بل الأحكام التي علقها الله بالسفر علقها به مطلقا .

Allahu Akbar, wannan magana ta ibn Taimiyya ta wadatar akan muce sai munyi dogon bayani, abune Wanda yake bude Allah bai kayyade ba kai waye da zaka kayyade?

Toh, rubutun idan akace za'ayi tayi baya karewa, don akwai hujjoji barkatai dake nuna halascin hade salloli a lokacin tafiya, a hakika yanzu nayi rauni a wurin rubutu, amma mu dauka cewa wannan kamar mukaddima ce, idan bukatuwar hakan ta kama zamu kara cewa wani Abu insha Allahu.

ALLAH YA KARA MANA IKHLASI DA KARFIN GWUIWA A WURIN AIKI DA DAI DAI DA FADAR GASKIYA.


✍ *Hashim Siraj Uba Tsamiya ( _ABU~SINAN_ )*

+2348064734911
+2349030201868

atstsamawy@gmail.com

atstsamawy@yahoo.com

Sunday, 25 November 2018

(B) DOMIN MASU HANKALI SUYI TUNANI

⚪⚪⚪⚪⚪⚪⚪⚪⚪⚪
*وليتذكر ألوا الألباب...*

*DOMIN MASU HANKALI SUYI TUNANI...*
⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫

Gabatarwa: *MUKYAUTATA NIYYA*

_PART_ *B*


*KASHI/BAYAN GIDA YAFI MAULIDI A SALI A CIKIN ADDINI...!!!*

*LADUBBAN SHIGA BAYAN GIDA(BIYAN BUKATA)*

Abubuwan da aka so ayi wajen shiga bayan gida don biyan bukata.

*Gasu kamar haka:-*

1. A lokacin shiga, zaka fadi ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺇﻧﻲ ﺃﻋﻮﺫ ﺑﻚ ﻣﻦ ﺍﻟﺨﺒﺚ ﻭﺍﻟﺨﺒﺎﺋﺚ . ```ALLAHUMMA INNI A'UZU BIKA MINAL KHUBSI WAL KHABA ISI```
watau [ALLAH INA NEMAN TSARI DAGA GAREKA, KA KARENI DAGA SHARRIN ALJANNU (SHAIDANU MAZA DA MATA)

2. Shiga bayan gida da kafar hagu.

3.sanya gajeren wando lokacin wanka, domin ka kare tsiraicinka idan a fili ne a wajen wankan

4. Fara yin bisimillah

5. Sanya ruwan wanka a gefen hannun dama

6. Amfani da takaitaccen lokaci a bayan gida(kashi)

7. Fitowa da kafar dama

8. Kebewa daga idanun mutane

9. Tsugunnawa lokacin da ake bayan gida

10. Mayar da nauyin jiki zuwa bangaren hagu

Bai kamata ba a shiga bayan gida da abin da ya ke dauke da sunan Allah s.w.t a jikinsa(sai dai domin gudun kada a sace shi), bayan an gama ana son a wanke hannaye da ruwa, ko da sabulu ko kuma tur6aya ko yashi.

Musulmai ya kamata lokacin da za suyi bayan gida ko wanka, su kebe kansu daga inda mutane zasu iya ganinsu.

An kar6o daga jabir yace; "idan muna tafiya tare da manzon Allah s.a.w, ya kanyi bayan gida idan ya kebe daga mutane (wato ya kan sakaya kansa inda ba mai ganinsa.

*ABUBUWAN DA BA'A SON A AIWATAR DANGANE DA BAYAN GIDA...!!*

1. Fuskantar/juya wa Alkibla baya idan a fili ne.

2. Magana ko kuma wa'ka yayin da ake bayan gida

3. Yin wanka a gaban jama'a

4. Karanta ayoyin alkur'ani a ban daki

5. Yin amfani da ruwa mai yawa.

6. Yin wanka, fitsari, ko bayan gida a wajen da ake ibada, misali;
*MASALLACI, COCI,* ko wani majalisi na al'umma.

7. Wanke can cikin dubura

8. Barin wasu mutane su ga tsiraicin dan uwansu.

9. Yin fitsari a cikin rami.

10. Ta6a azzakari ko dubura da hannun dama.

Yan uwa munji kadan daga cikin ladubban bayan gida(KASHI)
Domin karin bayani, ka duba ﺑﻠﻮﻍ ﺍﻟﻤﺮﺍﻡ -ﻛﺘﺎﺏ ﺍﻟﻄﻬﺎﺭﺓ - ﺑﺎﺏ ﺁﺩﺍﺏ ﻗﻀﺎﺀ ﺍﻟﺤﺎﺟﺔ

*YAN TA MAULIDE MUNA JIRAN NAKU LADUBBAN NA CASHEWA, DAGA HADISSAI INGANTATTU, DA INDA AKA CIROSU.*

*HAATU BURHAANAKUM INKUNTUM SADIQEEN*

HUJJA MUKE BUKATA BA ZAGI BA


✍ *Hashim Siraj Uba ats-tsamawy ( _ABBAN-SINAN_ )*
+2348064734911

018 MUKOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUPS DIN; *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na sha takwas 018_


Gabatarwa: *UMMU SINAN*

*MUSTAHABBAN ALWALA:*
Wannan shi ke biye da mataki na sunnoni, kenan sunnoni sun fi mustahabbai karfi,
wadanda suke dukansu biyun farillai na gabansu, babu daya daga cikin sunnoni ko
mustahabbai da mutum zai yi sakaci da su, domin kowannen mu so yake ya yi ibada
cikakkiya kammalalla, to kuwa tunda hakane bai kamata kace ai wannan mustahabbi ne ka daukeshi kamar wani karamin abu. Su mustahabban alwala suna da yawa, amma yanzu ga kadan daga cikinsu:

1⃣ Ambaton Allah kace *Bismillah* a daidai lokacin da zaka fara alwala, amma idan mutum
ya manta saida yake tsakiyar alwalar ya tuna
ba komai sai kayi a lokacin.

2⃣ Addu'a bayan kammala alwala, itace kuma kamar haka:

*ﺃَﺷْﻬَﺪُ ﺃَﻥْ ﻻَ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺍَﻟﻠﻪُ ﻭَﺣْﺪَﻩُ ﻻَ ﺷَﺮِﻳﻚَ ﻟَﻪُ، ﻭَﺃَﺷْﻬَﺪُ ﺃَﻥَّ ﻣُﺤَﻤَّﺪًﺍ ﻋَﺒْﺪُﻩُ ﻭَﺭَﺳُﻮﻟُﻪُ، ﺍَﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﺍَﺟْﻌَﻠْﻨِﻲ ﻣِﻦَ ﺍَﻟﺘَّﻮَّﺍﺑِﻴﻦَ، ﻭَﺍﺟْﻌَﻠْﻨِﻲ ﻣِﻦَ ﺍَﻟْﻤُﺘَﻄَﻬِّﺮِﻳﻦَ.*

_Ma'ana:_ ```Ina shaidawa da babu abun bauta da
cancanta sai Allah, kuma shi kadai yake bashi da
abokin tarayya, kuma ina shaidawa lalle (Annabi)
Muhammad bawan Allah ne kuma manzonsa ne,
Ya Allah ! ka sanya ni daga cikin masu yawan tuba, kuma ka sanya ni daga masu neman
tsarkaka.```

3⃣ 'Karanta Ruwa;
   Bawai ana nufin mai alwala ya shashshafa gabbansa bane, a'a, ana bukatar yayi amfani da ruwa amma kada ya malalar dasu, domin yana daga cikin tsarin musulunci
tattali da tsimi da tanadi.

4⃣ Gabatar Da Asuwaki:
Bayani kuma dama ya gabata akan asuwaki, ana yi da danye ko da
busasshe, idan bai samu ba sai ayi da yatsa, amma mu sani asuwaki daban kuskurar baki ma
daban. Hakanan kuma ko da mutum lokacin sallah yayi amma yana da alwala to abinda ake so shine ya yi asuwaki.

5⃣ Wuri Mai Tsarki:
  An so inda zaka yi alwala ya zama wurine mai tsarki.

6⃣ Dama Kafin Hagu:
  Abun nufi shine ka fara wanke hannun dama kafin hannun hagu, hakanan ka fara wanke kafar hagu kafin ta
dama.

7⃣ Jerantawa:
  Wato jeranta kowacce sunnah
tare da 'yar-uwarta, kamar fara gabatar da kuskurar baki kafin shaka ruwa.

8⃣ Wankewa Sau Uku:
  Ma'ana wanke wuraren da ake wankewa sau uku, mu sani wankewa sau uku zai zama mustahabbine idan wankewar farko ta game ko ina, amma idan ta farko bata
game ba to ta biyu tananan amatsayin wajibi, haka idan ta biyun bata game ba
to ta uku tana nan a matsayin wajibi. Ya zama wajibi mai alwala mace ko namiji ya kula sosai
ya cuccuda inda ya kamata ya sa ruwa ba tare da barna ba.
Amma shi kai sau daya ake shafarsa, ba'a shafar kai sau biyu ko uku. Sannan kuma mutum ya tabbata a wadannan wankewa da akace yayi sau uku bai kara akan hakan ba, yayi iya kokarinsa ya ga guda ukun sun kammala.

Wadannan kadan kenan daga cikin
mustahabban alwala, kuma wadannan bayanai
sun shafi mata kamar yadda suka shafi maza, sai dai
mata su sani gashin kansu al'aurane, saboda haka bai
halatta su bayyanar dasu ga maza ba, kenan idan zaki yi alwala sai ki sami wuri ki kebance
kanki.

Wadannan bayanai da suka gabata zasu haskaka mana yadda alwala take, amma hanya mafi sauki shi ne a yi maka ita a aikace ka gani domin haka sahabban ma'aikin Allah suka yi, an
tambayi Usman dan Affan dan gane da alwala sai yasa aka kawo mishi butar alawala yayi musu ita a aikace, yace kuma irinta manzon Allah s.a.w yayi.

A nan nake kira ga dukkanin limamai na juma'a dana sauran masallatai da kuma malamai a
jami'oi da kwalejin ilimi da kuma malamai a sakandare da firamare da malaman islamiyyu da malamai masu karantarwa a masallatai da
masu wa'azi da sauran wadanda abin ya shafa kamar kungiyoyin addini
dasu karantar da mutane alwala a
aikace, yadda kowa zai gani ya kuma yi tambaya, kada kaga kamar kowa ya gane da zarar ka yi ta a aikace zaka ga abin mamaki, ni na taba gwada
hakan a *Federal university birnin kebbi,* ita ibada sai an koyawa mutum ba wai daka akeyi ba, kai da ganin
alwalar wani kasan bai je makaranta ba, Allah ya karba mana ibadummu.

A NAN MUKA KAWO KARSHE DANGANE DA BAYANI AKAN ABUNDA YA SHAFI ALWALA, A GABA ZAMU BAYANIN ABUBUWAN DAKE KARYA ALWALA INSHA ALLAHU.

WANDA YAYI BITAR RUBUTUN;
✍ *Hashim Siraj Uba atstsamawy ( _ABU-SINAN_ )*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

(A) DOMIN MASU HANKALI SUYI TUNANI

*وليتذكر ألوا الألباب...*

*DOMIN MASU HANKALI SUYI TUNANI...*

_Gabatarwa:_ *MUKYAUTATA NIYYA GROUPS*

PART *A*

📌 *WANNAN ITACE HUJJAR MU AKAN CEWA MAULIDI BIDI'AH NE...!!!*

*==============*

▫ Abubakar siddiq(RA) yayi khalifanci tsawon shekara biyu amma baiyi maulidi ba, tare da cewa shi mai gaskiyar wannan al'ummar ne, kuma abokin manzon Allah s.a.w a cikin kogo lokacin hijira..!!
*▪▪▪▪▪▪▪*

🔸 Umar bn khaddab(RA) yayi khalifanci shekaru goma(10), amma ba'a ruwaito cewa yayi maulidi ba, tare da cewa shine FARUQ na wannan al'umma..!

*▪▪▪▪▪▪▪*

🔹Usman bn affan(RA) yayi khalifanci shekaru 13, amma baiyi maulidi ba, kuma baice ayi ba, tare da cewa ya auri yayan annabi guda biyu, kuma yayi hijira guda biyu, Wanda yafi kowa kunya a cikin wannan al'umma..!
*▪▪▪▪▪▪▪*

🔸 Aliyu bn Abi dalib(RA) yayi khalifanci shekaru 4 amma bai aikata maulidi ba, baiyi umurni da ayi ba, kuma shi Dan baffan manzon Allah s.a.w ne, kuma shine ya auri shugabar matan yan aljanna...!
▪▪▪▪▪▪▪

▫Hassan bn Aliyu bn Abi dalib yayi khalifanci wata shida(6) amma baiyi maulidi ba, gashi jikan Manzon Allah s.a.w, kuma shine shugaban samarin aljanna...!
▪▪▪▪▪▪▪

◼ Mu'awiya bn Abu sufyan yayi mulki na adalci a cikin kabilun larabawa, amma baiyi maulidi ba, bai kuma ce ayi ba
▪▪▪▪▪▪▪
◻Daular umawiyya tazo, a cikinta akwai irinsu Umar bn Abdulaziz, daular Abbasiyya tazo, a cikinta akwai misalin Harun Ar-rasheed, amma dukansu basuyi maulidi ba, basu kuma yi umurni da ayi ba..!
▪▪▪▪▪▪▪

🔹 Yanzu ma malaman gaskiya, masoya manzon Allah s.a.w gaskiyar so, basuyi maulidi ba tun daga karnukan nan guda uku, tare da tsananin sanin su akan abunda Allah ya saukar, da kuma girman fahimtarsu ga Qur'ani, ya akayi basuyi ba? Tare da cewa sune suka iso da Qur'ani da hadissai zuwa garemu..?

▪▪▪▪▪▪▪
  Mu dai yanzu zamu ce;  Da maulidi alkhairi ne da sun rigamu aikatashi..!
▪▪▪▪▪▪▪
Zamu fadi Abunda Imamu Malik(RH) ya Fada; ```Duk abunda bai zama addini a lokacin manzon Allah s.a.w da sahabbai ba, ba zai taba zama addini ba har tashin Al-kiyama..!```
▪▪▪▪▪▪▪
➡ Abu sananne kawai shine; Manzon Allah s.a.w bai bar duniya ba sai da ya kammala Isar da sakon da Allah ya aikoshi dashi..!
▪▪▪▪▪▪▪
   ▪ ya tsoratar da sahabbanshi akan kirkirar wani abu a cikin addini, da aikata abunda bai aikata ba..!
▪▪▪▪▪▪▪

▫ Ya kamata kusan cewa; wadancan karnukan masu girma basu San wani biki mai suna Maulidi ba! Shifa Maulidi wata bidi'ah ce da yan shi'ah *(FADIMIYYUNA)* suka kirkira, a karkashin wani shugabansu da suke kira Mai daukaka addinin Allah, sai dai karya suke, shi mai cutar da addini ne..!
▪▪▪▪▪▪▪
🔸 yayi mulki a bisa kafirci, da fasikanci, ta inda ya halasta shangiya, ya halasta kowane  farji na mace, ya tsinewa sahabbai kuma yayi umurni da hakan a saman mimbarorin juma'ah, wannan Dan ta'addan shine ya kirkiri maulidi fa! Ya kasa maulidin gida shida, Na farko; Maulidin Manzon Allah s.a.w, sai na Fadima, Aliyu, Hassan, Hussaini(ALLAH YA YARDA DASU) sai Maulidin kanshi..!
▪▪▪▪▪▪▪

Daga nan sai yan fadimiyyuna suka jahiltar da musulmai akan wannan bidi'ar, ya kamata kusan cewa babu wani dalili a wurin yan tamaulide akan halascin maulidi, kawai hujjarsu wasu nassosi ne suke yim a gurguwar fahimta, ko kuma hadissai na karya koda sun inganta sai ka samu basu nuni akan maulidi amma sai su juyar da ma'anarsu.
▪▪▪▪▪▪▪

◼ *YANZU GA WASU YAN TAMBAYOYI GUDA UKU DA MUKESON MU JEFAWA YAN TAMAULIDE, MUNA NEMAN AMSARSU:*
▪▪▪▪▪▪▪

1⃣ Shin bikin maulidi biyayya ne ga Allah da Manzon Allah s.a.w ko sabon Allah ne??

Idan sunce biyayya ne! Ko kuma sunce Sabo ne, duka akwai tuhuma garesu..!

2⃣ Yawwa, idan sukace biyayya ne ga Allah kuma zasu samu lada akai!
Sai muce Ko Manzon Allah s.a.w yasan da wannan biyayyar?
Ko bai sani ba?

➡ Da zasu ce bai sani ba, da sai muce kaiconku! Yanzu kuna tuhumar Babban malami(Manzon Allah s.a.w) da jahilci, wannan kafurci ne, kuma zindikanci ne..!
▪▪▪▪▪▪▪

🔸 Da zasu ce ya sani, toh sai muje a tambaya ta uku.

3⃣ Kunce biyayya ne, kuma Manzon Allah s. a.w ya sani, shin ya bayyanar dashi ga mutane ko kuwa ya boye???

Idan sunce bai Isar ba, wannan tozarci ne ga Manzon Allah s.a.w, da kuma tuhumar Manzon Allah s.a.w da boye wani Abu na manzanci, bayan a Qur'ani Allah s.w.t ya Fada cewa; ```Yaa kai Manzon Allah ka Isar da abunda ya sauka gareka daga ubangijinka, idan bakayi haka ba, baka Isar da Manzancin ba.```

Idan kuma sunce ya Isar, sai muce; Toh kuzo mana da dalili, ina aikin magabata akai?
Yanzu muna bukatar amsoshi daga gareku.

ALLAH YA NUNA MANA GASKIYA YA BAMU IKON BINTA, YA NUNA MANA BIDI'AH YA BAMU IKON KAUCE MATA

KU WATSA WANNAN A TSAKANIN MUTANE DOMIN AL'UMMA SU GANE GASKIYAR BIDI'AR MAULIDI...

WANDA YAYI BITAR RUBUTUN;
✍ *Hashim Siraj Uba Tsamiya ( _ABBAN-SINAN_ )*
+2348064734911

Thursday, 15 November 2018

002 DOMIN MASU HANKALI SUYI TUNANI

🔘🔘🔘🔘🔘🔘🔘🔘🔘🔘
*وليتذكر ألوا الألباب...*

*DOMIN MASU HANKALI SUYI TUNANI...*
🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶

_Fitowa Na biyu 002_

Gabatarwa: *MUKYAUTATA NIYYA GROUPS*

*ASALIN MAULIDI A MUSULUNCI DA WADANDA SUKA KIRKIRESHI!! KASHI NA BIYU(002)*

HAK’IK’A RAFIDA UBAIDIYYUNA, SUN TILASTA WA DUKKAN MA’AIKATANSU ‘YAN MISRA, DA SU RUNGUMI ADDININSU NA RAFIDANCIN BA’DINIYYA, KAMAR YADDA SUKA WAJABTA WA ALK’ALAI SU ZARTAR DA HUKUNCE – HUKUNCE A BISA DOKOKIN WANNAN ADDINI NASU. KAI, HAR YA KAI GA CEWA; SHARA’DI NE NA SAMUN MATSAYI A DAULAR, SAI MUTUM YA JUYA YA KOMA ADDININ RAFIDANCIN BA’DINIYYA. WANDA HAKAN YA SA DA YAWA DAGA CIKIN KAFIRAN AMANA SUN NUNA SHIGA MUSLUNCI TARE DA RUNGUMAR RAFIDANCI.

*DUBA AL- DAULAR FA’DIMIYYA SHAFI NA 218*.

WA’DANNAN MUTANE ‘YAN SHI’A BA’DINIYYA, WA’DANDA SUKA K’IRK’IRI MAULIDI, YANA DAGA CIKIN GABARSU DA SUNNAR ANNABI (SAW), DA AHLINTA; AZEEZ SARKIN LOKACIN YA YI UMURNI DA A DENA SALLAR TARAWIHI A DUKKAN K’ASAR MASAR. WATO A SHEKARA TA *372.* SA’ANNAN A SHEKARA *393* AN KAMA WASU MUTANE *13,* AKA YI MUSU DUKA, SA’ANNAN AKA YI YAWO DA SU AKAN RAK’UMA A CIKIN GARI, AKA TSARESU TSAWON KWANA *3,* DUK WANNAN SABODA KAWAI SUN YI SALLAR *WALAHA.* A SHEKARA *381,* AN BUGI WANI MUTUM AKA ZAGAYA A CIKIN GARI DA SHI SABODA KAWAI AN SAMU LITTAFIN *”MUWA’D’DA’A”* TA IMAMU MALIK (R) A WAJENSA.

*TSANANIN GABAR UBAIDIYYUNA (RAFIDA BA’DINIYYA) WA’DANDA SUKA K’IRK’IRI MAULIDI GA SAHABBAI DA AHLUS SUNNA:*

A SHEKARA TA *395H* A CIKIN WATAN *SAFAR,* AN RUBUTA ZAGIN MAGABATA (SAHABBAI) DA TSINE MUSU A BABBAN MASALLACIN *MISRA ”JAMI’UL ATIK”’* DA MA SAURAN MASALLATAN, TA CIKI DA WAJENSU, DA TA DUKKAN GEFE – DA – GEFENSU, DA K’OFOFIN SHAGUNA DA MAK’ABARTU. AKA ZANA SHI DA ZINARI. HAKA AKA YI A K’OFOFIN GIDAJE DA NA MANYAN ‘DAKUNAN TARO. KUMA AKA TILASTA MUTANE AKAN YIN HAKAN, TSINE MA AHLUS SUNNA ABU NE DA YA WATSU A BAKUNAN MUTANE, AKAN MINBARORI A DUKKAN FA’DIN MASAR TSAWON MULKIN UBAIDIYYUNA. HAR TA KAI GA SHI *ABHID* – SARKINSU NA K’ARSHE- SABODA TSANANIN SHI’ANCINSA, DA GULUWWINSA WAJEN ZAGIN SAHABBAI (RA) – IDAN YA GA MUTUM AHLUS SUNNA SAI YA HALATTA JININSA.

*DUBA AL- KHI’DA’DA NA MAK’RIZIY,* (2/ 341). DA *TARIKHUD DAULATIL FA’DIMIYYA* SHAFI NA (620). DA *WAFIYYATUL A’AYAN* (3/ 110).

*KAFIRCIN UBAIDIYYUNA (RAFIDA BA’DINIYYA) WA’DANDA SUKA K’IRK’IRI MAULIDI:*

WANI ABU DA YA FI DUKKAN ABIN DA MUKA AMBATA A BAYA SHI NE; *AL- HAKIM* SARKIN DAULAR FA’DIMIYYA, YA YI DA’AWAR CEWA; SHI ALLAH NE. *(SUBHANALLAH)!!*  SAI YA UMURCI MUTANE DA SU TASHI SU TSAYA DA K’AFAFUNSU A CIKIN SAHUN SALLAH A LOKACIN DA MAI HU’DUBA YAKE HU’DUBA IDAN YA KIRA SUNANSA, DON GIRMAMA AMBATONSA DA SUNAN NASA. KUMA HAKA YA SA AYI A DUKKAN MASARAUTAR TASA. HAR A HARAMAINI (MAKKA DA MADINA). AMMA YA WARE MUTANEN MISRA YA UMURCE SU DA SUNA FA’DUWA K’ASA SU YI SUJADA, IDAN AN KIRA SUNAN NASA. HAR YA ZAMA MUTANEN DA SUKE KASUWA MA WA’DANDA BA SA ZUWA JUMA’A SUKAN FA’DIN SU YI SUJADA IN NA CIKIN MASALLACIN SUN FA’DI, IN MAI HU’DUBAN YA AMBACI SUNAN NASA, A RANAR JUMA’A. HAR AN SAMU WASU JAHILAN IDAN SUN GAN SHI SAI SU CE: YA *WAHIDANA,* YA *AHADANA,* YA *MUHYI,* YA *MUMITU.* SA’ANNAN YA UMURCI BAK’AK’E DA SU K’ONA MASAR, SU WAWASHE DUKIYOYINTA, DA KAYAYYAKI, DA MATA. KUMA SUKA BI UMURNIN NASA, SUKA KAMA MATA SUKA YI TA ALFASHA DA MUNANAN AIYUKA DA SU. SUKA K’ONA ‘DAYA BISA 3 NA MISRA SUKA WAWUSHE RABINTA.

DUBA *AL- BIDAYA WAN NIHAYA* (12/ 10 – 11), DA *AL- MUNTAZIM* (7/ 298).

*WANNAN SHINE TARIHIN MAULIDI DA WADANDA SUKA KIRKIRESHI A TAKAICE.*

Note: AKWAI BUKATUWAR DUK WANDA YA KARANTA NA FARKO YAYI KOKARI YA NEMI NA BIYU, IDAN KA KARANTA NA BIYU KADA KAYI HUKUNCI SAI KA NEMI NA DAYA.

*DOMIN MASU HANKALI SUYI TUNANI...*




✍ *ABBAN_SINAN*

001 MUKOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE,
DAGA ZAUREN *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na daya 001_

Gabatarwa: *UMMU-SINAN*

*MUKADDIMA*

Godiya ta tabbata ga Allah madaukakin sarki Wanda ya wajabta mana tsarki, tsira da aminci su tabbata ga fiyayyen halitta Annabi Muhammad s.a.w Wanda ya karantar damu yadda zamuyi tsarki.

_Bayan Haka;_
Insha Allahu kamar yadda muka alkawarta muku cewa zamu fara kawo muku karantarwa akan ibada da sauransu, yanzu zamu fara daga yau har zuwa lokacin da muke iyawa insha Allahu.
Mun tsara Abubuwan daki-daki, zamu fara da magana akan tsarki kafin sauran, zamuyi kokarin ganin kullum munyi sau daya, filin tambaya a bude yake insha Allahu.

*TSARKI DA YADDA AKE YINSA A MUSULUNCI*

*Shimfida:*  Mu sani ya 'yan-uwa masu albarka,
wannan addini na musulunci addinine da yake
cikakken addini ta kowane bangare, bai takaitu
ga alwala da sallah ba kawai, ya shafi kowane bangare na rayuwa, kamar tsafta kiwon lafiya
zamantakewa, kasuwanci taimakon juna, tsare-
tsaren gudanarwa dadai sauransu.
A yanzu zamu kawo bayanai da suka shafi tsarki, dame-dame ake yiwa tsarki? Me rashin tsarkin yake jawowa? Ya ladubban yin tsarkin
suke? Ya ake shiga makewayi? Dadai sauran wadansu batutuwa da suke da alaka da wannan
maudu'i, da fatan Allah ya yi mana jagora ya
kuma fahimtar da mu.

*ABUBUWAN DA AKEWA TSARKI:*

Ana yin tsarki ne
daga dukkan abinda ya fito ta daya daga
mafita guda biyu ko ma ta duka inbanda hutu (tusa). Kenan ana yiwa fitsari, bayan gida maniyyi maziyyi jinin al'ada….tsarki, kawai dai idan mutum yana da alwala sai ya yi tusa to
alwalar kawai zai sake ba sai ya dauki buta ya yi tsarki ba.

Insha Allahu zamu dakata anan sai lokaci Na gaba.

WANDA YAYI BITAR RUBUTUN SHINE: *Hashim siraj uba ats-tsamawy(ABU-SINAN)*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN:

*MUKYAUTATA NIYYA*
wa.me/+2348064734911

*KARATTUTUKAN MALUMAN SUNNAH*
wa.me/+2349031666613

13 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN; *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na sha biyu 013_

Gabatarwa; *UMMU SINAN*


*MENENE JININ BIKI???*
  Jini ne da yake fitowa daga mahaifa ta sanadiyyar haihuwa.
Kenan shi jinin
biki jini ne da yake da alaka da haihuwa, idan mace taga jini kwana daya ko biyu kafin
haihuwa to shima malamai suna lissafashi cikin
jinin haihuwa.

*MAFI YAWAN KWANAKINSA;*

    Mafi yawan kwanakin da macen da ta haihu zata ga jinin haihuwa malamai sun karawa juna sani, wadansu sukace
kwanaki ar'bain ne (40), wadansu kuma sukace kwanaki sittin ne(60) kamar yadda mai Akhdari
ya bayyana.
Sabanin na al'ada shi kwanaki goma sha-biyar ne.

  Idan mace ta haihu sai jinin bai dauke ba to zata jira kwanaki arba'in, ko sittin, idan ya dauke a kwanakin shikenan sai ta yi wankan tsarki na daukewar jinin haihuwa ta ci gaba da sallah da kuma sauran ayyuka na ibada, idan kuma bai dauke ba to sai a nemi magani ya
zama jinin ciwo sai ta yi wankan tsarki ta ci gaba da ibada, idan kuma jinin ya dauke kafin kwanakin kamar ya dauke ranar da aka yi haihuwar to a nan ma zata yi wanka ne ta cigaba da sallah, laifi ne mai girman gaske mace
jinin haihuwarta ya dauke amma taki yin sallah wai sai ta yi arba'in wannan ba tsari bane na addinin musulunci.

Imam Tirmizi yake cewa: Malamai sun yi ijima'i tun daga Sahabbai da Tabi'ai da wadanda suka zo bayansu (Sun yi ijima'i) akan cewa lalle mace mai haihuwa zata bar salla tsawon kwanaki arba'in sai dai idan ta ga tsarki kafin hakan (kafin kwanaki arba'in din) sai ta yi wanka ta kuma yi sallah.
Idan mace ta yi bari sai ya zama na halittar mutum ta bayyana a barin, kamar ace ga tsarin
halittar ba wai gudan jini bane ya zama na kuma akwai jini daya zuba to anan tana da hukuncin jinin biki(jinin haihuwa), gwargwadon kwanakin da sune  halittar take bayyana a ciki sune
watanni uku galibi amma dai mafi karanci sune kwanaki tamanin (80).
Idan ta yi barin gudan jini ko gudan tsoka ta yadda halittar mutum bata bayyana ba to ba'a
la'akari da wannan jinin da ya zubo, saboda
haka ba zatabar sallah ba kuma ba zatabar
azumi ba saboda jinin domin bata da hukuncin
jinin biki.

Idan jinin haihuwa ya dauke kafin wadancan
kwanakin da aka yi bayaninsu to zata yi
wankane ta kuma yi sallah ko da jinin ya
dauke ne a ranar da aka yi haihuwar.


ZAMU DAKATA A NAN SAI WANI LOKACI NA GABA IDAN ALLAH YA KAIMU INSHA ALLAHU.

DOMIN SHIGA GROUP DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

DOMIN MASU HANKALI SUYI TUNANI

*وليتذكر أولو الألباب...*

*DOMIN MASU HANKALI SUYI TUNANI...*

✍ *KO MAULIDI NA DA ASALI A CIKIN ADDINI???*

🍂 *AL-ALLAMA, IMAMUSH SHAUKANY (RAHIMAHULLAH) YACE;*

```Har yanzu ba'a samu dalili a cikin AL-QUR'ANI da SUNNAH, da IJMA'IN MALAMAN MUSULUNCI ko QIYASI da ya nuna tabbatuwar maulidi ba, bari ma Musulmai sun hadu akan cewa ba'a san maulidi a zamanin sahabbai ba ko tabi'ai ko masu bi musu ba.```

📚 *FATHUR-RABBANY(2/1087)*

_GASKIYA DAYA CE, DAGA QINTA SAI..._

#ABBAN_SINAN
http://wa.me+2348064734911
atstsamawy@gmail.com

01DOMIN MASU HANKALI SUYI TUNANI...

🔘🔘🔘🔘🔘🔘🔘🔘🔘🔘

*وليتذكر أولو الألباب...*

*DOMIN MASU HANKALI SUYI TUNANI...*
🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶🔶

_Fitowa Na Farko 001_

Gabatarwa: *MUKYAUTATA NIYYA GROUPS*

*ASALIN MAULIDI A MUSULUNCI DA WA’DANDA SUKA K’IRK’IRE SHI!!*

MAGABATAN WANNAR AL’UMMA BA SU YI MAULIDI BA KAMAR YADDA KOWA YA SANI, K’ARNUKAN DA MANZON ALLAH (SAW) YA YABESU WATO K’ARNI NA FARKO DA NA BIYU DA NA UKU DUKA SUN GABATA AMMA LITATTAFAN TARIHI BA SU KIYAYE MANA CEWA AN SAMU WANI DAGA CIKIN SAHABBAI KO TABI’AI KO MABIYA TABI’AI, DA MA WA’DANDA SUKA ZO A BAYANSU DA YA YI MAULIDIN ANNABI (SAW) BA, DUK DA TSANANIN SOYAYYARSU GA MANZON ALLAH S.A.W, KUMA DUK DA CEWA SUN FI KOWA ILIMIN SANIN ADDININ MUSULUNCI, KUMA DUK DA CEWA SUN FI KOWA KWA’DAYIN BIN SHARI’AR ANNABI (SAW).

FARKON WA’DANDA SUKA FARA MAULIDIN ANNABI S.A.W  SUNE :
*BANU UBAID AL-K’ADDAH*, WA’DANDA SUKE KIRAN KANSU DA *FA’DIMIYYUNA*
MA’ANA JIKOKIN FATIMA (R A). SABODA SUNA DANGANTA KANSU ZUWA GA ZURIYYAR ALIYU (R A),
ALHALI A HAK’IK’ANIN GASKIYA WA’DANNAN MUTANE SU NE SUKA ASSASA *DA’AWAR BA’DINIYYA,* WATO ‘YAN BA’DINIYYA MASU CEWA ADDINI YANA DA ZAHIRI YANA DA BA’DINI, KUMA WAI SUNE SUKA SAN BA’DININ.

*ASALIN KAKANSU*
SHI NE *IBNU DISAN,* WANDA AKA FI SANI DA *AL- K’ADDAH,* YA KASANCE MAULA NE NA *JA’AFARUS SADIK’* WATO ‘YANTACCEN BAWANSA, KUMA ‘DAN ASALIN GARIN *AHWAZ* NE, ‘DAYA DAGA CIKIN WA’DANDA SUKA ASSASA MAZHABAR *BA’DINIYYA* A IRAK’I, SANNAN SAI  YA BAR GARIN ZUWA MAGRIB, TO A WANCAN YANKIN NE YA DANGANTA KANSA ZUWA GA *AK’ILU ‘DAN ABI ‘DALIB,* YA RIYA CEWA SHI DAGA TSATSONSA YAKE,  TO A LOKACIN DA *RAFIDA* MASU GULUWI SUKA AMSA DA’AWARSA, SAI YAYI DA’AWAR CEWA WAI SHI ZURIYYAN *MUHAMMAD BIN ISMA’IL BIN JA’AFAR AL- SADIK’* NE, KAWAI SAI SUKA YARDA DA HAKAN DUK DA CEWA SHI *MUHAMMAD BIN ISMA’IL*  YA MUTU BAI BAR *‘DA* BA,
DAGA CIKIN WA’DANDA SUKA BI SHI AKWAI *HAMDAN K’URMU’D*, WANDA *K’ARAMI’DA* SUKE DANGATUWA GARE SHI. DA ZAMANI YA YI NISA SAI *SA’ID BIN HUSAINI BIN AHMAD BIN ABDULLAH BIN MAIMUN BIN DISAN* YA BAYYANA, SAI YA CANZA SUNANSA DA NASABARSA, SAI YACE WA MABIYANSA SHINE *UBAIDULLAHI BIN HASAN BIN MUHAMMAD BIN ISMA’IL BIN JA’AFAR AL- SADIK’*, A HAKA SAI FITINARSA TA BAYYANA A MAGRIB.

DON K’ARIN BAYANI AKAN WANNAN BAYANI, DUBA *WAFIYYATUL A’AYAN*( 3/ 118), *ALBIDAYA WAN NIHAYA* (11/ 202), *FABHA’IHUL BA’DINIYYA* SHAFI NA (11), *ALFARK’U BAINAL FIRAK’ NA BAGDADIY* SHAFI NA (266 – 267).

KHALIFOFIN DAULAR RAFIDA ‘YAN BA’DINIYYA/FA’DIMIYYA DAKE *MISRA* SUNE SUKA FARA DUKKANNIN MAULIDI!

DON HAKA FARKON WA’DANDA SUKA FARA MAULIDI SU NE RAFIDA ‘YAN BA’DINIYYA WA’DANDA SUKA YI NUFIN CANZA WA MUSULMAI ADDININSU, TA HANYAR SHIGAR DA ABIN DA BA YA CIKINSA.
UBAIDIYYUNA SUN SHIGA MISRA NE A *SHEKARA TA 362 BAYAN HIJIRA*, A RANAR *5 GA RAMADAN*, WANNAN NE FARKON LOKACIN DA SUKA FARA MULKINSU A MISRA, WASU SUN CE: RANAR *7 NE GA RAMADAN,* TO DUKKANNIN MAULIDI NA ANNABI (SAW) DA NA WANINSA WA’DANNAN MUTANE UBAIDIYYUNA SUNE SUKA FARASHI,
BABU WANDA YA TA’BA YIN MAULIDI KAFINSU.
*AL- MIK’RIZIY* YACE; KWANAKIN DA KHALIFOFIN FA’DIMIYYA SUKA RIK’A A MATSAYIN RANAKUN IDI, DA RANAKUN TARO WA’DANDA AKE YALWATAWA TALAKAWA DA YAWAITA MUSU NI’IMOMI YA KASANCE KHALIFOFIN FA’DIMIYYA SUNA DA RANAKUN IDI DA NA TARO A TSAWON SHEKARA, GA SU KAMAR HAKA:
*BIKIN DAREN FARKON SHEKARA,* DA, *BIKIN RANAR FARKON SHEKARA,* *RANAR ASHURA,* *RANAR HAIHUWAR ANNABI (SAW),* *RANAR HAIHUWAR ALIYU (RA),* *DA RANAR HAHUWAR HASAN (RA),* *DA RANAR HAHUWAR HUSAINI (RA),* DA RANAR HAIHUWAR *FATIMA AL- ZAHARA’U (RA),* DA RANAR HAIHUWAR *KHALIFA MAI CI A LOKACIN,* DA IDIN DAREN *RAJAB,* DA DAREN TSAKIYAR *RAJAB,* DA DAREN FARKON *SHA’ABAN,* DA TSAKIYAR *SHA’ABAN,* DA TARON IDIN *SALLAR AZUMI,* DA NA IDIN *LAYYAH,* DA IDIN *GADEER,* da sauransu...

SA’ANNAN SAI *AL- MAK’RIZIY* YA ‘DAUKESU ‘DAYA BAYAN ‘DAYA YANA BAYANIN YADDA SUKE YINSU. DUBA *AL- KHI’DA’DUL MIK’RIZIYYA* (1/ 490).

*YANAYIN MULKIN KHALIFOFIN RAFIDA ‘YAN BA’DINIYYA TA DAULAR FA’DIMIYYA, WA’DANDA SUKA K’IRK’IRI MAULIDI:*

SARAKUNAN DAULAR FA’DIMIYYA TA RAFIDA ‘YAN BA’DINIYYA SUN FUSKANTAR DA SIYASARSU NE ZUWA GA MANUFA GUDA ‘DAYA, ITA CE: YIN DUKKAN IYA K’OK’ARINSU NA TILASTAWA MUTANE AKAN SU BI ADDININSU NA RAFIDANCIN BA’DINIYYA, DA SANYA SHI YA ZAMA SHI NE AWWALU MAA YAJIBU A DUKKAN GARURUWAN MISRA, DA MA SAURAN GARURUWAN DA SUKE MULKI, DA MAK’OBTANSU.
SARAKUNAN WANNAR DAULA SUN YI MATUK’AR MU’AMALA DA YAHUDAWA DA NASARA, TA YADDA SUN NUNA MUSU SOYAYYA SOSAI, SUN BASU MUK’AMAI MASU GIRMA A CIKIN WANNAR DAULA.
DUBA *ALBIDAYA WAN NIHAYA* (11/ 358), *AL- MUNTAZIM* (7/ 190), *ITTI’AZUL HUNAFA* (1/ 297), *AL- DAULAR FA’DIMIYYA* SHAFI NA (202).

HAK’IK’A AL- UBAIDIYYUNA/RAFIDA/‘YAN BA’DINIYYA DA SARAKUNAN DAULAR FA’DIMIYYA, SUN KAI MATUK’A WAJEN YA’DA TSINUWA GA KHALIFOFIN ANNABI (SAW) GUDA 3; *ABUBAKAR* (RA), DA *UMAR* (RA), DA *USMAN* (RA) DA SAURAN SAHABBAI.
SABODA SUNA K’IRGASU A CIKIN MAK’IYA ALIYU (RA). TARE DA WATSA FALALAR ALIYU (RA) DA ‘YA’YANSA TA HANYAR ZANAWA A JIKIN MANYAN K’ARFUNA DA RUBUTAWA A JIKIN KATANGUN MASALLATAI,
KUMA MASU HU’DUBA SUN KASANCE SUNA TSINE MA SAHABBAI AKAN DUKKANNIN MINBARORIN K’ASAR MISRA GABA ‘DAYA.


KADA RUBUTUN YAYI TSAYI, ZAMU DAKATA A NAN SAI LOKACI NA GABA ZAMU CIGABA INSHA ALLAHU.

*DOMIN MASU HANKALI SUYI TUNANI...*


*ABU-SINAN*

ISTIKHARA

*SALLAR ISTIKHARA(NEMAN ZABIN ALLAH) A MUSULUNCI*
👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇

Wallafar Dalibinku;
✍ *ABBAN SINAN*

http://darulfikr.com/ebook/41913

KU SAUKE KU KARANTA ZAKU KARU MATUKA

http://wa.me+2348064734911

BINCIKE...

*ANALYSIS*

Assalamu Alaikum warahmatullahi wabarakatuhu

Yan uwa na masu albarka dake group din *MUKYAUTATA NIYYA* both, na *Mata* dana *Maza* ina bukatar taimakonku a wannan shekarar domin Isar da sakon Allah.
Wane irin taimako ne???
Nayi shiri na musamman domin fadakar da yan uwa musulmi cewa *Maulidi* bashi da Asali a cikin addinin Islama, a tare da haka sai nayi wani bincike, *Misali:* Ni ina da Abokai masu WhatsApp mutum 500+, ina da groups 100+, a Facebook ina da abokai 5000, da masu bibiya 1000+ a Facebook ina da groups, Wanda idan aka Tara mutanenshi sun kai 100,000+ bari na tsaya a haka, idan nayi posting duka wadannan zasu gani, abokanansu ma zasu gani, toh abunda Nike bukata a yanzu shine, kaima/kema kuna da WhatsApp friends da groups, me kake/kike tsammani idan kikayi copy na post din ka/kika watsa shi ga abokanka/ki???
Muyi tarayya a wurin yada alkhairi shi yafi domin mu rabauta a wurin Allah, kamar yadda sanarwa ta gabata cewa, salon da'awar a wannan karon zai chanja, taken rubututtukan shine;
ﻭَﻟِﻴَﺘَﺬَﻛَّﺮَ ﺃُﻭﻟُﻮ ﺍﻟْﺄَﻟْﺒَﺎﺏِ...
those of understanding would be reminded...
Domin masu hankali suyi tunani...
Suratu sad aya ta 29

Miye shawararku, ko goyon bayanku akan hakan???

Ina saurare domin karba, ina saran fara rubutu a 29 safar 1440AH insha Allahu

#ABBAN_SINAN
#MAULIDI
#SHAWARA
#MUKYAUTATA NIYYA

http://wa.me+2348064734911

17 MUKOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN; *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na sha bakwai 017_

Gabatarwa: *UMMU SINAN*

*SUNNONIN ALWALA:*
1⃣ Wanke Hannaye Kafin A Tsoma Su A Ruwa, ta yadda mai alwala zai karkato butar alwala domin ya wanke hannayen sa zuwa  wuyan hannu.

2⃣ *Kuskurar Baki:*    
  Mai alwala ya tabbata ya sanya ruwa a bakinsa sannan kuma ya kuskure bakinsa da
ruwan.

3⃣ *Sha'ka Ruwa:*
  Shine mai alwala ya shaki ruwa ruwan ya shiga hancin sa sosai, sai dai kawai idan yana azumi ne sai yayi kadan. Amma yadda mutane suke shafar hancinsu wai da sunan shaka ruwa wannan bai dace ba, ya kamata mu gyara.

4⃣ *Facewa:*
  Mai alwala zai shaki ruwa ne da
hannun dama sai ya sa hannun hagu akan karan hancin sa, sannan sai ya fyato ruwan da
ya shaka.

5⃣ *Shafar Kunne;*
  Mai alwala ya tabbata ya shafi cikin kunnensa da wajen kunnen, zaka/ki sanya yatsanka manuniya(☝) a cikin kunnen sannan kasa babban yatsa(👍) a wajen kunnen sannan sai ka shafa.

6⃣ *Sake Taba Ruwa:*
A lokacin da zaka shafi kunne shin zaka shafi kunnen ne da ragowar
danshin hannuka da ka yi shafar kai da shi? Ko ko zaka sake taba ruwa na musamman domin
shafar kunne, malamai sun karawa juna sani, ko
wanne ka yi ya yi daidai.

7⃣ *Dawo Da Shafar Kai:*
Ka tsaya ka fahimta, shi shafar kai farilla ne, amma dawo da shafar
kai sunnah ce daga cikin sonnonin alwala.

8⃣ *Jeranto Farillai:*
Ta yadda zaka kawosu daya-bayan-daya kamar yadda aka lissafosu, kada ka dauki na uku ya zama shine na farko
sannan ka biyo shi dana biyar, misali…'.

Wadannan sunnonin matsayinsu bai kai matsayin farillai ba,
amma suna cikin manyan abubuwan da suke cika alwala.


ZAMU DAKATA ANAN SAI LOKACI NA GABA ZAMUYI BAYANIN *MUSTAHABBAN ALWALA* INSHA ALLAHU



WANDA YAYI BITAR RUBUTUN SHINE;
✍ *Hashim Siraj Uba ats-tsamawy( _ABU~SINAN_)*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

16 MUKOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN; *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na sha shida 016_

Gabatarwa: *UMMU SINAN*

*FARILLAN ALWALA*

1⃣ *Niyyah:*
Domin a bambance wanda ya sa ruwa domin sanyaya jiki, ko domin gusar da
datti, duk wannan ba niyya ce ta alwala ba.

2⃣ *Wanke Fuska:*
  Ita kuma fuska ta bangaren tsawo tana farawa ne daga matsirar gashin kai zuwa karkashin haba(gemu), amma
ta fuskar fadi tana farawa ne daga kunnen dama zuwa kunnen hagu, wannan shine abinda yake amsa fuska, kenan dole mai alwala ya tabbatar ko ina ya samu ruwa kamar kasan haba, gefen
ido da gefan kunne da matsa-matsin karan hanci, ayi hattara sosai domin wasu alwalarsu
kamar alwalar yarace.

3⃣ *Wanke Hannaye Zuwa Gwiwar Hannu;*
Mai alwala mace ko namiji ya tabbata ya wanke hannayensa tun daga saman yatsunsa (farce/kaifa) har zuwa gwiwar hannu ya tabbata gwiwar ta shiga inda ya wanke, anan ma akwai manyan mutane masu alwalar yara.

4⃣ *Shafar Kai:*
Ka tabbata ka hada yatsunka sannan kuma ka fara shafar daga goshi (dai-dai
matsirar gashi) sannan ka shafa zuwa keya.

5⃣ *Wanke Kafa:*
Haka nan mai alwala ya tabbata ya wanke kafarsa har zuwa idon sawu,
wato wadannan kasusuwan guda biyu dake
gefen kafafuwa sun shiga cikin inda aka wanke.

6⃣ *Cudanyawa:*
  Mai alwala ya tabbata ya cudanya duk inda ya wanke ya dirza ruwa ya
shiga ko ina.

7⃣ *Jerantawa:*
  Abinda ake nufi shine a lokacin da ka fara alwala to ka dakatar da komai sai ka kammala, amma kana alwala kana kuma wata sabga daban wannan ba dai dai bane.

Mai alwala ya tabbata ya gabatar da wadannan ayyuka a lokacin da yake alwala ta yadda idan aka rasa daya daga cikin su to alwalarka ta shiga chakwakiya.


ZAMU DAKATA ANAN INSHA ALLAHU SAI WANI LOKACI NA GABA ZAMUYI BAYANI AKAN *SUNNONIN ALWALA*


DOMIN SHIGA GROUPS DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

15 MUKOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN; *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na sha biyar 015_

Gabatarwa; *UMMU SINAN*

*FALALAR ALWALA;*
Kasantuwar cewa alwala wajiba ce wannan kadai ya isa ka gane falalar ta a
musulunci domin dukkan abunda akace farillah ne
to wannan matsayi ne mai zaman kanshi, bayan hadisi na 62 a cikin *Muwadda Malik* yana cewa; An karbo daga Abdullahi As-Sunaabihi, lalle ma'aikin Allah –Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi yace:  *''Idan bawa mumini ya yi alwala sai ya yi kuskurar baki dukkanin laifukan dake bakin sun Wanke, idan kuma ya shaqa ruwa sai ya fyace, dukkan laifukan daya shaka sun fice, idan kuma ya wanke fuskarsa laifukan da ke fuskar ta sa sun wanke, har wadanda ke karkashin girar shi, idan ya wanke hannayensa laifukan dake hannayensa sun fice, har wadanda ke karkashin akaifarsa (farce), idan kuma ya shafi kanshi laifukan dake kan nashi sun fice har wadanda ke kunnuwansa, idan kuma ya wanke kafafuwansa duk laifukan dake kafafuwansa sun fice, har wadanda ke karkashin farcen kafafun nashi."*
Sannan kuma
tafiyar da ya yi zuwa masallaci ya zama wani
kari ne da yake da shi na lada''.
Lalle wannan bakamar falala bace da alwala take da shi, domin mai alwala zai kasance yana kammala alwala zunubanshi suna digewa a
kasa, amma wani hanzari ba gudu ba, wannan ladan zai tabbata ne ga wanda ya yi alwala a yadda shari'a ta tabbatar da ita ba wacce ya tsinta a
kan titi ba.

*SHARUDDAN ALWALA*

  Sharuddan alwala sune abubuwan da ake so mai alwala ya cika su kafin ya fara alwalar, sune kamar haka:

1⃣ *Musulunci*
  kenan idan wanda ba musulmi ba ya yi alwala bata yi ba.

2⃣ *Hankali*
Idan mahaukaci ya yi alwala itama bata yi ba.

3⃣ *Wayau*
Idan dan karamin yaro mara dabara
ya yi bata yi ba.

4⃣ *Ruwan ya zama mai tsarki*
Idan ya zama ruwa ne mara tsarki to alwalar bata yi ba, bayanai sun gabata akan hukunce hukuncen ruwa.
5⃣ *Ruwan ya zama na halas*
Idan ruwa ne da
mutum ya sata ko ya same shi bata shar'antacciyar hanya ba to alwalar bata yi ba.

6⃣ *Ya kasance mai tsarki*
  Idan mai alwala ya
kasance ya yi fitsari ko bayan gida misali wato ya kasance mara tsarki kafin alwala to ko ya yi alwalar bata yi ba.

7⃣ *Gusar da duk abinda zai hana ruwa shiga*
Kenan idan mutum ya kasance yana sanye da wani abunda zai hana ruwa ya kai ga fatar jiki to dolene ya cire shi, kamar zobe da sauransu.


ZAMU DAKATA A NAN INSHA ALLAHU SAI WANO LOKACI NA GABA ZAMUYI BAYANI AKAN *FARILLAN ALWALA*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

14 MUKOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN; *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na sha hudu 014_

Gabatarwa; *UMMU SINAN*

   Alwala ibadace mai zaman kanta
wacce Allah madaukakin sarki ya shar'anta ta
kafin gabatar da wadansu ibadu musamman ma
sallah, mutum yana samun cikakken ladan alwala idan ya yi ta cikakkiya, Allah madaukakin
sarki ya saukar da hukunce-hukuncen alwala a cikin littafinsa mai girma alkur'ani:

*''Ya ku dukkanin wadanda suka yi imani, idan kuka ta shi za ku yi sallah to ku wanke fuskokin ku da hannayanku zuwa gwiwar hannu ku kuma shafa kawunanku da kafafanku zuwa idon sawu (idon kafa)…''* [Suratu Ma'ida, aya ta: 6].

Tabbas wannan aya ta yi bayanin wajibcin alwala lokacin da za'a yi sallah, kuma ta
bayyana gabban da ya zama wajibi a wanke ko kuma a shafa, sannan kuma ayar ta iya kance
ko wanne mahalli.
       Ma'aikin Allah
–Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi ya bayyana siffar yadda alwalar take da maganarsa da kuma aikinsa bayanin da yake
gamsasshen bayani.

Ka sani lalle ita wannan alwala tana da falala da kuma sharudda da kuma farillai sannan tana da sunnoni da kuma mustahabbai, sharuddan nan
da farillai tabbas a tabbata mun sansu alokacin gabatar da alwala iya gwargwado domin da sune alwala zata zama karbabbiya, amma su sunnoni da mustahabbai suna cika alwalarne ta inda matsayinsu bai kai matsayin farillai ba.

ZAMU DAKATA A NAN INSHA ALLAHU SAI WANI LOKACI NA GABA ZAMUYI BAYANI AKAN *FALALAR ALWALA*

DOMIN SHIGA GROUP DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

Wednesday, 17 October 2018

012 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN; *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na sha biyu 012_

Gabatarwa; *UMMU SINAN*

*ABUBUWAN DA BASU HALATTA GA MAI AL'ADA;*

A wannan karon zamu lissafa abubuwan da basu halatta mace mai al'ada ta aikatasu ko a aikata mata, abubuwan sune kamar haka;

1⃣ *SALLAH;*
Baya halatta mai al'ada ta yi sallar
farilla ko nafila, idan kuma tayi, ta yi ba'a karba ba, sannan kuma ta yi laifi, sannan bayan ta
kammala al'adar ba zata rama sallolin ba.

2⃣  *SAKI;*
Baya halatta matar da take al'ada a sake ta, wannan ya sabawa karantarwar
musulunci, saboda haka koda yana son ya sake ta to ya bari sai ta kammala al'ada kafin ya sadu da ita sai ya sake ta, amma idan ya sake ta tana jinin al'adar to sakin ya yi amma
za'a tilasta shi ya mayar da ita idan sakin bai kai uku ba.

3⃣ *DAWAFI;*
Bai halatta mai al'ada ta yi dawafin
Ka'abah, amma zata yi sauran dukkan abinda maniyyaci yake yi, kamar tsayuwar Arafah da
kwanan mina dana muzdalifa da jifa da
Labbaika, da daidai sauransu.

4⃣ *ZAMA A MASALLACI;*
  Mai al'adah ba zata zauna a cikin masallaci ba, domin sauraron karatu ko karantarwa ko taro da dai sauransu(SAI DA KWAKWARAN DALILI).

5⃣ *AZUMI;*
Baya halatta mai al'ada ta yi azumi na farilla ko na nafila, idan ta yi kuma bai yi ba, saboda haka zata lissafa azumin da ta sha bayan watan ya wuce sai ta rama su.
  Ba'a ajiye azumi domin tsammanin gobe al'ada zata zo,
amma dazaran ta zo to ba azumi.

6⃣ *TABA ALQUR'ANI;*
Mai al'ada bata taba ALQUR'ANI,
kasantuwar sa littafi mai tsarki sannan kuma ita bata da tsarki, amma wannan baya hana idan ta ganshi zai fadi ta daukeshi ta gyara masa wuri.

7⃣ *KARATUN ALQUR'ANI;*
Mai al'ada bata karanta Alkur'ani, duk da cewa wadansu malamai suna ganin ya halatta ta karanta daga abunda ta haddace domin kada ta manta sabanin dauka.

8⃣ *SADUWA;*
Baya halatta saduwa da mace
a lokacin al'ada, idan ta ki yadda da mijinta ya sadu
da ita domin tana al'ada ba za'ace ta sabawa Allah ba hasali ma ta yi biyayya ne ga reshi, baya halatta a sadu da mace tana al'adaba har sai
al'adar ta dauke kuma ta yi wankan tsarki, kenan koda al'adar ta dauke amma batayi wanka ba to bai halatta a sadu da ita ba. Ya
halatta miji ya taba duk inda yake so a jikin matarsa a lokacin da take al'ada bayan ta yi
*kunzugu* in banda daga *cibiyarta* zuwa *gwiwarta*
wannan kam bai halatta ba har sai jinin ya dauke kuma tayi wanka, hakanan itama ya halatta ta
taba ko ina a jikinsa duk da tana al'ada.

9⃣ *TABBATAR DA RASHIN TSARKI;*  Al'ada tana
tabbatar da wacce take da ita bata da tsarki.

🔟 *WAJABTA WANKA;*
  Al'ada tana wajabta wanka, wato dukkan matar da ta yi al'ada kuma al'adar ta dauke to wankan tsarki ya wajaba akanta.

ZAMU DAKATA A NAN SAI LOKACI NA GABA INDA ZAMUYI BAYANI AKAN JININ BIKI(JININ HAIHUWA) INSHA ALLAHU.

ALLAH YAYI MANA JAGORA.

WANDA YAYI BITAR RUBUTUN SHINE:

✍ *Hashim Siraj Uba ats-tsamawy( _ABU~SINAN_ )*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

Monday, 15 October 2018

011 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN; *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na sha daya 011_

Gabatarwa: *UMMU SINAN*


*ALAMOMIN DAUKEWAR JININ AL'ADA;*

Idan jinin al'ada ya dauke akwai wasu  alamomi da shari'ah ta sanya domin su zama manuniya akan cewar al'adarki ta dauke, wadannan alamu sun kasu gida biyu kuma kowacce tana cin gashin kantane, ga alamomin kamar haka:

1⃣ *BUSHEWAR GABA;*
Abunda ake nufi shine mace ta shigar da kyalle ko auduga cikin gaban ta, sannan ta fito dashi busasshe ba wani jini a tare da shi, to da zarar ta ga haka to ta tabbata
al'adarta ta dauke.

2⃣ *FARAR KUMFA;* 

Wannan wani ruwa ne fari mai laushi da yake zuwa karshan al'ada, idan mace ta ga irin haka karshen al'adar ta, ta sani ta kammala Al'adar ta.

Wadannan alamomi su suke nuna daukewar al'adar mace, idan mace bata taba yin al'ada ba sai a wannan karon sai ta fara ganin bushewar gaba to kai-tsaye ta samu tsarki, ba sai ta jira farar kumfa ba, amma idan wacce ta saba gani ce sai ta ga bushewar gaba to malamai suka ce zata dan saurara kadan domin jiran farar kumfa, amma jinkirin ba zai kai
ga fitar zababbun lokutan sallah ba.

    A dunkule dai kowane daya daga cikin wadannan abubuwa guda biyu yana nuna samuwar tsarki ba lalle sai sun hadu a lokaci
guda ba, da zarar alamar ganin tsarki ta tabbata sai kiyi wankan tsarki domin ki cigaba da
ibada, domin idan ba kiyi wanka ba ko da jinin ya dauke mijin ki ba zai sadu da dake ba kuma baza kiyi  sallah ba, da dai sauransu.

Idan mace ta ga ruwa fatsi-fatsi ko diddiga - diddiga bayan daukewar jinin al'ada to kada ta damu ta ci gaba da harkokinta na ibada, dama matsalar idan ta ganshi a farkon jini ne, amma idan a karshen jini ne to wannan ba komai,
Ummu Adiyyah matar Manzon Allah  (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) tace: *((Mun kasance bama lissafa (Ruwa) fatsi-fatsi da diddiga-diddiga bayan tsarki da cewa wani abune)).* [Abu Daud Hadisi Na: 307, Nasa'i, Hadisi Na: 368 , Ibnu Majah Hadisi Na: 647,
Darimi Hadisi Na: 865].

Mace ta dinga duba samun tsarkinta a lokacin da zata kwanta bacci da kuma lokacin sallar
asuba, amma ba'a ce ta tashi cikin dare ba domin ta duba.!!!

 

ZAMU DAKATA A NAN SAI LOKACI NA GABA INDA ZAMUYI BAYANIN ABUBUWAN DA BASU HALATTA GA MAI AL'ADA INSHA ALLAHU.

ALLAH YAYI MANA JAGORA.

WANDA YAYI BITAR RUBUTUN SHINE:

✍ *Hashim Siraj Uba ats-tsamawy( _ABU~SINAN_ )*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*

http://wa.me/+2349031666613

010 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN; *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na Goma 010_

Gabatarwa: *UMMU SINAN*


*KARKASUWAR MATA GAME DA JININ AL'ADA:*
    Mawallafin littafin Akhadari ya kasa mata zuwa kashi uku dangane da jinin al'ada, kashi na farko; *WACCE TA FARA,* Kashi na biyu kuma; *WACCE TA SABA,* sannan sai kashi na uku; *MAI JUNA BIYU,*
mai juna-biyu (wato mai ciki), ga bayanansu kamar haka;
1⃣ *WACCE TA FARA;*
  Ita wacce ta fara al'ada ya zama shi ne ganin al'adarta na farko a rayuwar ta, to abunda ke kanta zata zuba idone ta ga kwanaki nawa zai  dauka kafin ya yanke, ta yadda ba zai wuce kwanaki sha- biyar ba,(KAMAR YADDA BAYANI YA GABATA A RUBUTUKAN DA SUKA GABATA) idan ko ya wuce sha-biyar to abunda ya
doru akan kwanaki sha-biyar bai zama al'ada ba, kenan mafi yawan kwanakin da zata yi la'akari dasu sune kwanaki sha-biyar, amma zai iya daukewa kafin hakan, abin nufi in ya wuce to ya zama abunda ake kira
*(Isthala)* wato cuta sai a nemi magani, a karkashin wannan nake cewa iyaye su kara sa ido akan 'ya'yayansu mata su rika tuntubar su suna fahimtar da su
tun kafin lokacin ya yi domin kada lokaci yayi yarinya ta ga jini ta fashe da kuka,ko makaman tan hakan Wanda wannan Na faruwa kwarai da gaske, wata babbar mace ce amma bata san menene jinin al'ada ba ita dai kawai tace tana ganin jini a wani lokaci bayan wasu kwanaki kuma sai ta daina ganin shi,  kunga akwai hadari kwarai da gaske.

2⃣ *WACCE TA SABA:*
Abunda ake nufi da wacce ta saba itace wacce ta gabatar da al'ada sau uku, a adadin kwanaki guda, misali wacce ta yi al'adar farko a kwanaki biyar, da ta sake yi sai yayi mata kwanaki biyar da ta yi na uku shima kwanaki biyar, to wannan sai a kira ta da sunan
wacce ta saba, domin ta saba akan kwanaki sanannu.
  Amma idan ta yi al'adar karo na farko
kwanaki uku karo na biyu kuma kwanaki biyar
karo na uku kwanaki shida to ba za'a kira wannan wacce ta saba ba, domin ba ta da
tsayayyun kwanaki.
  Ita wacce ta saba wato wacce take da
sanannun kwanakin al'ada to wadannan
kwanakin sune kwanakin al'adarta, idan kwanakin suka cika al'adar kuma ta dauke sai ta yi wanka ta ci gaba da gudanar da ibada,
amma idan kwana kin suka cika al'adar kuma bata dauke ba sai ta kara kwanaki uku,haka zata dinga kara kwanaki uku har kwanaki sha biyar su cika, misali idan al'adar ta kwanaki biyar ne sai kuma jinin bai dauke ba a kwanaki biyar din sai ta kara kwanaki uku na sauraron daukewar sun zama takwas kenan, idan ya dauke shikenan sai wanka, idan kuma bai dauke ba sai ta kara uku akan wadancan kwanaki takwas din sun zama sha-daya idan bai dauke ba sai ta kara uku sun zama sha-hudu idan bai dauke ba sai ta
kara kwana daya, ya zama goma sha-biyar kenan, sai ta yi wankan kammala al'ada ko ya dauke ko bai dauke ba domin kwanakin al'ada makurarsu shine kwana goma sha-biyar kuma
sun cika, abunda ya cigaba da zuwa ba sunan shi jinin al'ada ba,sunanshi jinincuta *(Istihala)*
  sai a nemi magani.  A dukkan wadancan kare-karen kwanaki da aka yi inda ace bayan ta kara kwana uku na
saurare sai ya dauke a kwana na daya cikin ukun shikenen sai ta yi wankan tsarki.
Mu sani kamar yadda bayani ya gabata shi jinin al'ada bai wuce kwanaki goma sha-biyar ga wacce ta fara da wacce ta saba.

3⃣ *MAI JUNA BIYU(mai ciki);*  Galibin mata masu
juna biyu basa al'ada, sabo da haka da zarar mace tana da juna biyu (ciki) sai kuma ta ga
al'ada to kada ta yi sakaci wurin tuntubar likita.
  Idan al'ada ta zowa mace mai juna-biyu, to idan cikin ya kai watanni uku zuwa biyar zata iya yin
al'ada ta kwanaki sha-biyar zuwa ashirin, idan kuma cikin ya kai watanni shida to al'adar zata
iya daukar kwanaki ashirin zuwa ashirin da biyar, kada a sha'afa wurin tuntubar likita idan
Kina da juna biyu kuma kika ga jini.

   *TANBIHI NA DAYA:*
   Idan mace jini yana mata wasa wato yazo yau ya dauke bayan kwanaki uku sai kuma ya dawo to abunda zata yi anan shine, ta tsaya ta natsu, sai ta lissafa kwanakin da jinin ya zo sune kwanakin al'ada sai kuma ta ware kwanakin da jinin bai zoba sune kwanakin tsarki
domin da hakane zata cika kwanakin ta na al'ada, *MISALI,* kwanaki tara; sai ya zo a rana ta farko da ta biyu sai bai zoba a rana ta uku da ta hudu sai ya zo rana ta biyar amma bai zo ba a ta shida da ta bakwai sai ya zo a ta takwas da ta tara. To anan sai muce ta yi al'adar kwana biyar a cikin kwanaki tara, wannan matar ita
ake kira *(Al-Mulaffiqa)* a larabcin mata masu
al'ada. Idan ya zama an sami tazarar kwanaki takwas ko sha-biyar tsakanin daukewarsa da
dawowarsa to na biyun zai zama sabon jini ne kenan, ba na da ne ya dawo ba.


ZAMU DAKATA A NAN SAI LOKACI NA GABA INDA ZAMUYI BAYANIN ALAMOMIN  DAUKEWAR JININ AL'ADA INSHA ALLAHU.

ALLAH YAYI MANA JAGORA.

WANDA YAYI BITAR RUBUTUN SHINE:

✍ *Hashim Siraj Uba ats-tsamawy( _ABU~SINAN_ )*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

009 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN; *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na Tara 009_

Gabatarwa: *UMMU SINAN*

*TABBATUWAR JININ AL'ADA;*
     Shifa abinda ya
shafi jinin al'ada al'amari ne da Allah madaukain sarki ya yi bayaninsa a cikin Alkur'ani mai girma, Allah yana cewa:

```''Kuma suna tambayarka dangane da al'ada,
Kace: Shidinnan cutane, ku nisanci (saduwa da) mata a lokacin al'ada, kada ku kusance su har sai sun yi tsarki (Jinin ya dauke), idan suka tsarkaka
(suka yi wanka) to ku je musu ta inda Allah ya umarceku, Lalle Allah yana son masu yawan tuba
kuma yana son masu tsarkaka''.```
*[Bakara, ayata:222.]*

Haka kuma ma'aikin Allah –Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi- yace; ```(Wannan)
Wani abune da Allah ya dorawa mata 'ya'yan
Adam''.```
> Ashe ba shaci-fadin da ake cewa bane ai sanadiyyar da yasa mata suke al'ada shine wannan ganyan bishiyar da Nana Hawwa'u ta ci
a gidan aljanna, amma Annabi Adam mala'ikane
ya rike masa makoshi(makogaro) sai ya amayar da ganyen shi yasa maza basa yi.
   Wannan labarin bashi da kanshin gaskiya domin ayoyin Alkur'ani sun tabbatar da Annabi Adam ya ci itaciyar.

Shifa jinin al'ada kada amanta jini ne da yake fitowa daga can cikin mahaifa a lokuta sanannu,
Allah madaukakin Sarki ya halicceshi domin ya zama abinci ga yaro a lokacin da yake cikin mahaifiyarsa domin inda zai yi tarayya da
mahaifiiyar ta shi a abincin da take ci to da karfinta ya ragu sosai, sai Allah ya sanya shi ya zama abinci ga reshi, shi yasa dakyar kaga
mace tanada juna biyu (ciki) kuma tana al'ada.

Idan kuma ta haihu sai Allah ya mayar dashi nono jaririn yana sha amatsayin abinci, shi yasa kadan ake samun matan da suke shayarwa kuma suna al'ada. Idan ya zamana mace bata
da juna biyu (ciki) kuma bata shayarwa sai ya
kasance ba inda zaije(jinin al'adar) to shine sai ya taru a
mahaifarta, shine mafi yawancin lokuta yake fita a kowanne wata cikin kwanuka shida ko
bakwai, ya kan karu ko ya ragu akan hakan (kamar yadda bayanai za su zo da izinin Allah).

ZAMU TUQE A NAN SAI LOKACI NA GABA INDA ZAMUYI BAYANI AKAN KARKASUWAR MATA AKAN JININ AL'ADA INSHA ALLAHU

ALLAH YAYI MANA JAGORA

WANDA YAYI BITAR RUBUTUN SHINE;

✍ *Hashim Siraj Uba ats-tsamawy ( _ABU~SINAN_ )*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

008 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN; *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na takwas 008_

Gabatarwa: *UMMU SINAN*

*MINENE MAFI QARANCIN JININ AL'ADA?*
   Malamai sun karawa juna sani
kan mafi karancin jinin al'ada, mafi karancinsa shine 'dugo guda' kenan idan ya duga sannan ya dauke, shikenan ta yi al'ada kuma ta dauke.

*MINENE MAFI YAWAN JININ AL'ADA?*
  Mafi yawan kwanakin jinin al'ada shine kwanaki goma sha-biyar, kenan idan ya
wuce haka to bai zama jinin al'ada ba muddin ba ciki take da shiba.

*MATA DANGANE DA JININ AL'ADA:*

  Anan ya kamata mu san cewa mata
suna da halaye biyar musamman idan muka yi
la'akari da shekarunsu domin auna jinin da ya
zo na al'ada ne ko bana al'ada bane, halayyar itace kamar haka:

1. *KASA DA SHEKARA TARA;*    Idan jini ya zowa
yarinyar da take kasa da shekara tara, to malamai sun tabbatar da wannan ba jinin al'ada bane, jinin ciwone sai a nemi magani.

2. *SHEKARA TARA ZUWA SAMA;*    Idan ya  zamana jinin ya zo ne
ga wacce ta cika she kara tara zuwa zamanta budurwa, to a irin wannan lokaci sai a tambayi
kwararrun mata da likita domin a fayyace jinin na al'adane ko na ciwo.
Kada mu sha'afa
yanayin abinci da kuma yanayin zafi da sanyi da
hutu da wahala suna tasiri a irin wannan wuri.
3. *BUDURCI ZUWA SHEKARA HAMSIN;* 
  Idan jini yazo
daga lokacin da ta zama budurwa zuwa shekaru hamsin (50) kai tsaye malamai sun
tabbatar da cewa wannan jinin na al'adane.

4. *DAGA SHEKARA HAMSIN ZUWA SITTIN DA TARA(50-69);*
  Idan jini ya zowa mace a tsakanin wadannan shekaru wato daga shekara
hamsin zuwa sittin da tara (50-69) to malamai sukace za'a tambayi kwararrun mata da likitoci domin sanin wannan jinin na ciwone ko na
al'ada.

5. *DAGA SHEKARA SABA'IN ZUWA SAMA;*
  Idan jini ya zo bayan mace ta cika
shekara saba'in (70) zuwa sama to malamai sukace wannan kai tsaye ba jinin al'ada bane.
Ashe tantance shekarun haihuwa ba karamin abu bane domin tuni musulunci ya gina hukunce-hukunce akansu, kuma ana gini ne akan tsarin
kalandar musulunci, wadannan bayanai na karkasuwar mata har zuwa gida biyar kamar yadda ya gabata haka *MALAM ADAWY*
  ya kawo a cikin littafinsa *'Hashiyatul Adawi'*, Allah ya ji kansa da gafara.

  Ina Kara jaddada cewa yanayin abin ci da abin sha da sanyi ko yanayin zafi suna tasiri
matuka, dukkan abinda ba'a mahimta ba
dangane da yana yin zuwan jini ko daukewarsa yarinyace ko babba to kamata ya yi ayi
tambaya cikin gaggawa lura da yadda muka yi
bayani da cewa yanada alaka da hukunce
hukunce, kina yin jinkiri sai salloli su kubuce miki, kuma wannan yana nuna cewa mace da
aka *SAKI* zata iya kammala idda a kasa da watanni uku.
Idan yarinya ta ga jinin kuma jinin ya zama shine zuwansa na farko sannan ya tabbata
cewa jinin al'adane to ta sani ta balaga,
dukkanin hukunce-hukuncen musulunci sun hau
kanta, idan ta yi salatin Annabi za'a rubuta mata lada idan kuma ta bari samari suna
jagwalgwalarta ita za'a rubutawa zunubi, ba wanda yace wai sai ta yi aure sannan za'a fara yi mata rubutu, kenan har azumi idan ta sha sai ta ranka.


ZAMU DAKATA A NAN SAI LOKACI NA GABA INDA ZAMUYI BAYANIN TABBATUWAR JININ AL'ADA INSHA ALLAHU.

ALLAH YAYI MANA JAGORA.

WANDA YAYI BITAR RUBUTUN SHINE;
✍ *Hashim Siraj Uba ats-tsamawy( _ABU~SINAN_ )*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

007 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN; *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na bakwai 007_

Gabatarwa: *UMMU SINAN*



*HUKUNCIN JININ AL'ADA ( JININ HAILA)*

Gabatarwa: Da sunan Allah Mai yawan rahama
mai yawan jinkai, tsira da amincin Allah su tabbata ga fiyayyen halittar Allah Annabin tsira
Annabi Muhammad s.a.w, da Iyalan shi da Sahabban shi baki daya.
   Bayan haka a yanzu kuma muna
daukene da abinda ya shafi jerin hukunce-hukuncen jinin al'ada wanda ake kira jinin haila,
da izinin Allah bayanshi za mu
kawo hukunce-hukuncen jinin biki (wato jinin
haihuwa).

*Muhimmanci:*   yana da matukar muhimmanci sanin hukunce hukunce jinin al'ada, muhimancin
bawai ya tsaya ga mata bane kadai, a'a har da maza, domin abubuwa da yawa na ibada da na zamantakewa suna da alaka da jinin al'ada, misali mai jinin al'ada bata sallah ko azumi ko
dawafi, wannan bangaran ibada kenan amma ta
bangaren zamantakewa mai jinin al'ada ba'a
sakinta ba kuma a saduwa da ita, sannan ga yadda Allah ya sanya idda da jinin al'ada, ta
yadda idan aka saki mace sai ta ga tsarki uku
(al'ada uku) kafin ace ta kammala idda, sannan sai ai maganar sabon aure, to idan tana
al'ada bayan kowadanne watanni shida kenan
sai bayan shekara daya da rabi za'a fara maganar aure, shi yasa muka ce sanin hukunce-hukuncen wannan jini ba wai ya rataya ga mata bane kadai har da maza.

*MINENE JININ AL'ADA:???*

    Jinin al'ada jinine da yake fita da karan kansa ta gaban macen da a
al'adance zata iya daukar ciki, ba tare da ya wuce
kwanaki goma sha-biyar ba.

Wannan shi ake nufi da jinin al'ada, da akace *'jinine da yake fita da kansa'* kenan idan ya
zamana ba da kansa ya fita ba kamar ace cinnaka ya cije ta a gaba ko kunama sai jini
ya balle mata to wannan bai zama jinin al'adaba.
   Da akace *Ta gaba*' kenan idan ya fita ta dubura ko ta hanci wannan bai zama jinin al'adaba.
  Da akace *'Wacce a al'adance zata iya daukar ciki'* kenan idan ya fita daga wacce a al'adance ba zata iya daukar ciki ba sabo da
yarinta ko girma to wannan shima bai zama jinin al'adaba.

Amma da aka ce *'Ba tare da ya wuce kwanaki goma sha-biyarba'* kenan idan ya wuce kwanaki
sha-biyar to bai zama kuma jinin al'adaba.

Wadannan nau'uka da akace basu zama jinin
al'adaba kenan hukuncin jinin al'ada bai hau kansu ba, za su yi sallah domin jinin ciwone sai a
nemi magani, Allah ya sawwaka.

ZAMU DAKATA A NAN SAI LOKACI NA GABA, INDA ZAMUYI BAYANIN MAFI QARANCIN JININ AL'ADA.

ALLAH YAYI MANA JAGORA.

WANDA YAYI BITAR RUBUTUN SHINE; *Hashim Siraj Uba ats-tsamawy ( _ABU~SINAN_ )*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

006 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN; *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na shida 006_

Gabatarwa: *UMMU SUNAN*

🔸 *DAGA CIKIN ABUBUWAN DAKE WAJABTA WANKA.*

1⃣  ```FITAR DA MINIYYI TA HANYAR SHA'AWA, A CIKIN BARCI KO A FARKE.```

2⃣ ```SADUWA DA IYALI(JIMA'I)```

3⃣ ```FITAR JININ HAILA(Al'ada) KO NA BIQI(Na haihuwa)```

4⃣ ```MUTUWA```

✍ *AL-ALLAMA SHEIKH MUHAMMAD BIN SALIH AL-UTHAIMIN*
(RAHIMAHULLAH) YAKE CEWA;

1⃣ *FITAR DA MANIYYI TA HANYAR SHA'AWA, A CIKIN BARCI KO A FARKE;* Duk Wanda ya fitar da maniyyi a cikin barci, wanka ya wajaba a gareshi, saboda Wanda yake barci yana mafarki, idan mafarkin yasa ya fitar da maniyyi, yana wajaba yayi wanka a kowane hali.

2⃣ *SADUWA(JIMA'I);*
    Idan miji ya sadu da matarshi, yana wajaba wanka a garesu, saboda boyuwar hashafa a cikin al'aurar matarshi, saboda fadar manzon Allah s.a.w cewa;

➡ << Ruwa daga ruwa suke>> Ma'ana: wanka yana wajaba a lokacin da namiji ko mace suka fitar da maniyyi.

➡<< Idan miji ya zauna tsakanin gabobinta guda hudu(matarsa) kuma yaji dadi da ita, wanka ya wajaba a garesu, koda basu fitar da komai ba, wannan matsalar(SADUWA BA TARE DA FITAR DA MANIYYI BA) da yawa daga cikin mutane suna jahiltar wannan hukuncin, ta inda wasu mazan suke amfani da yatsunsu a wajen saduwa da iyalansu ba tare da fitar da maniyyi ba sai suki yin wanka saboda jahilcin dake addabarsu, Malam yace wannan al'amari akwai hadari a cikinsa kwarai da gaske, abunda yake wajibi shine mutum yasan cewa idan ya sadu da iyalansa koda bai fitar da komai ba, wanka ya wajaba a garesu(mijin da matar).

3⃣ *FITAR JININ AL'ADA KO NA HAIHUWA;*
   Ita mace idan HAILA tazo mata sai ta dauke, yana wajaba tayi wanka, saboda fadar Allah S.W.T;
  "KU NISANCI MATA A LOKACIN DA SUKE HAILA, KADA KU KUSANCESU HAR SAI SUNYI TSARKI, IDAN SUNYI TSARKI TOH SAI KUZO MASU TA INDA ALLAH YA UMURCEKU, LALLAI ALLAH YANASON MASU TUBA, KUMA YANASON MASU TSARKAKEWA".
  Da fadar Manzon Allah s.a.w cewa; " MAI HAILA IDAN TA KARE KWANAKIN HAILARTA, DA MATA WADANDA SUKA HAIHU IDAN JINI YA DAUKE MUSU, NA GARESU SUYI WANKA."

  Siffar yadda ake wankan haila da na haihuwa kamar siffar yadda ake na janaba yake, sai dai wasu malaman sun so a wankan haila ko haihuwa ayi da ganyen magarya, saboda shi yafi a wurin tsafta da tsarki.

4⃣ *MUTUWA;* Dalili akan wankan gawa shine fadar Manzon Allah s.a.w cewa; "KU WANKE TA SAU UKU, KO SAU BIYAR KO SAU BAKWAI KO FIYE DA HAKA IDAN KUNGA YIYUWAR HAKAN.....HADITH

Da fadar Manzon Allah s.a.w cewa; " KU WANKE SHI DA RUWA, DA GANYEN MAGARYA, KU RUFESHI DA TUFAFINSA"...(mutumin da ya mutu a arfa a lokacin Manzon Allah s.a.w)

Sai Malamai sukace; Su wadanda suka mutu, wanka Na wajaba garesu, sai sai dai wajabcin yana hawa akan yan uwansu rayayyu, saboda shi Wanda ya mutu komi nashi ya yanke, bazai iya aikata komai ba, saboda haka yan uwansu dake raye su zasu yi musu wanka, kamar yadda Manzon Allah s.a.w ya umurta da yin haka.

▪_________________
◼ *Majmu'u fatawa warrasa'il Na Sheikh Muhammad bin Salih Al-uthaimin, Mujalladi Na sha daya, babin wanka.*

SAI WANI LOKACI NA GABA INSHA ALLAHU.

WANDA YAYI BITAR RUBUTUN SHINE; *Hashim Siraj Uba ats-tsamawy( _ABU~SINAN_ )*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

005 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA GROUP DIN *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na biyar 005_

Gabatarwa: *UMMU-SINAN*

*ABUBUWAN DA RASHIN TSARKI YAKE HANA AIKATAWA;*

    kamar yadda bayani ya gabata cewar tsarki
wajibine, to mu sani idan mutum bashi da tsarki baya halatta a gareshi ya aikata wadannan abubuwan da zasu zo;

1. *SALLAH:*
    Baya halatta ga wanda bashi da tsarki yayi sallar nafila ko farillah.

2. *SUJJADAR TILAWA:*

  Wato sujjadar da mutum zai yi idan yana karatun Alkur'ani mai girma sai ya kai wadansu gurare, domin ba shi da tsarki, duk da cewa malamai sun karawa juna sani akan wannan.

3. *DAUKAR ALQUR'ANI MAI TSARKI:*
     Idan mutum
bashi da tsarki to sai yayi tsarki kafin ya taba wannan littafi mai tsarki.

Wannan shine abunda ya sawwaka insha Allahu.

*A GABA ZAMUYI BAYANI AKAN HUKUNCIN JININ AL'ADA INSHA ALLAHU*


WANDA YAYI BITAR RUBUTUN SHINE: *Hashim Siraj Uba ats-tsamawy( _ABU-SINAN_ )*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

004 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA ZAUREN *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na hudu 004_

Gabatarwa: *UMMU-SINAN*

*CIGABA DA KAWO LADUBBAN ZAGAYAWA FITSARI KO BAYAN GIDA*

11. *KAUCEMA RAMI;*
    Ba'a yarda idan za ka yi fitsari ko bayan gida ka yi a rami ba sai dai idan
kai ka haka ramin, domin bakasan mike cikin ramin ba,
takan yiwu akwai mugun abu da zai iya cutar da kai.

12. *KAUCEMA WURAREN TSINUWA;*
    Wadannan wurare sune wuraren da mutane suke yawan
tsinema duk wanda ya yi musu bayan gida a wurin, wadannan wurare sune:
🔹 Inda mutane suke zama su huta, jikin bangone ko karkashin bishiya komadai inane.

🔹 Kan hanya: Akwai rashin mutunci mutum ya
zo kan hanya yayi bayan gida, wannan
dabi'a musulunci bai yarda da ita ba.

🔹 Mashayar ruwa: Hakanan baya cikin
karantarwar musulunci mutum ya zo inda al'umma suke diban ruwa rafi ne ko wani gulbi
ko gindin fanfo koma dai inane ya aikata wannan
ta'asa.
 
      Wadannan wurare uku musulunci ya
hana a aikata wannan danyan aiki a wurin, domin mutum yana jawa kansa tsinuwa, Allah ya tsaremu.

13 *NESA DA JAMA'AH;*
  Ana bukatar dukkan wanda zai yi bayan gida ya yi nesa da jama'a ta
yadda ba za su ganshi ba kuma ba za su ji nishin shi ba, bai dace ace kana bayan
gida mutane suna ganinka ko suna jin nishinka ba,
ko da a bayan bishiya ko ganyan kargo sai ka
boye, amma sau da yawa mutane suna tafiya a mota da motar ta tsaya sai ka ga kowa ya
tsaya dab da motar, sannan ba za'a tafi a barshiba.
14 *KADA KA FUSKANCI ALKIBLA;*
    Wato inda
mutum yake kallo lokacin sallah, kuma kada ya
juya mata baya, wannan idan a dajine, amma
idan a gidane to da sauki babu laifi.

ZAMU TSAYA A NAN SAI LOKACI NA GABA ZAMU KAWO ABUBUWAN DA RASHIN TSARKI YAKE HANA AYI SU INSHA ALLAHU.

WANDA YAYI BITAR RUBUTUN SHINE: *Hashim Siraj Uba ats-tsamawy( _ABU-SINAN_ )*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MAKUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

003 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE,  DAGA ZAUREN *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na uku 003_

Gabatarwa: *UMMU-SINAN*

*LADUBBAN ZAGAYAWA FITSARI KO BAYAN GIDA*

   Akwai tsari da ladubba da musulunci yake da su a lokacin da mutum ya ke niyyar kewayawa, wannan zai nuna maka cewa musulunci yayi bayani akan komai, daga cikin ladubban akwai;

1. *AMBATON SUNAN ALLAH*

  Ana bukatar kafin ka shiga ka ambaci sunan Allah domin ba'a ambaton Allah a makewayi, kuma ka nemi Allah ya tsareka da
sharrin aljanu, domin irin wadannan wurare
matattarace ta su, kafin ka shiga sai ka fadi:
ﺑِﺴْﻢِ ﺍَﻟﻠﻪِ، ﺍَﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﺇِﻧِّﻲ ﺃَﻋُﻮﺫُ ﺑِﻚَ ﻣِﻦَ ﺍَﻟْﺨُﺒُﺚِ
ﻭَﺍﻟْﺨَﺒَﺎﺋِﺚِ

Ma'ana: Da sunan Allah, Ya Allah lalle ni ina
neman tsarinka (Ka tsareni) daga sharrin aljanu maza da kuma aljanu mata. Idan kuma zaka fito sai kace:

ﻏُﻔْﺮَﺍﻧَﻚَ، ﺍَﻟْﺤَﻤْﺪُ ﻟﻠﻪِ ﺍَﻟَّﺬِﻱ ﺃَﺫْﻫَﺐَ ﻋَﻨِّﻲ ﺍَﻷَﺫَﻯ
ﻭَﻋَﺎﻓَﺎﻧِﻲ

Ma'ana: Ina neman gafarar Ka , Dukkan godiya
ta tabbata ga Allah wanda ya rabani da wannan
kazantar kuma ya bani lafiya.

Ka sani ba'a shiga bayi da dukkan wani abu da yake dauke da sunan Allah.!!!

2 Fara Gabatar Da Kafar Hagu Lokacin Shiga, kafar dama kuma lokacin fita.

3 *AYI A TSUGUNNE;*  
kada mutum ya yi fitsari ko bayan gida a tsaye, sai dai idan wurin kangone ko yana tsoron fitsarin ya fallatso masa,
sannan ba wanda zai ganshi, sai ya yi a tsaye.

4 *TABBATUWA A CIKIN SUTURA;*
   Ana bukatar kada mutum ya yaye al'aurar sa tun yana tsaye, sai ya tsugunna ya yi dab da kasa sai ya daga
suturarsa, domin ba'a yarda wani ya ga al'aurar
wani ba in ba miji da mataba, amma halin ko
unkula da wasu suke nunawa na bayyanar da
al'aurarsu ga kowa muddin jinsi gudane wannan
bai daceba, sai ka ji wani yace 'Ai duka
mazane, abinda kake da shi ina dashi', wannan
ba koyarwar musulunci bace, haka suma mata, wannan zai kaika ka ga maza sun tube
suna wanka lokaci guda a dakin wanka guda, haka suma mata, wai sun dauka abinda yake
haramun shine namiji ya ga al'aurar mace ko mace ta ga al'aurar namiji, kai wani lokaci kana
tafiya a cikin mota sai kai arba da wani
gabjejen kato yana wanka a rafi, wani kuma a gefen titi ya kafe mashin ko ya aje kayan tallansa, duk wadannan ba kyawawan halaye
bane, mutum musulmi ya nisance su.

5 *MUTUM YAFI BADA KARFI A KAFARSA TA HAGU;*
Kenan abinda akafi so shine mutum ya fi bayar da karfinsa a kan kafarsa ta hagu.

6 *YA BUDE TSAKANIN CINYOYINSA;*
  kenan kada ya matse, ballantana ya sa matsattsiyar tufa
wacce idan yana fitsari na gaban ne kawai zai
fita, sannan idan ya mayar cikin wando sauran
ya gangaro, Allah ya sawake.

7  *NISANTAR INDA RUWA YAKE;*
  musulunci bai
yadda mutum ya yi fitsari ko bayan gida a inda ruwa yakeba ko kusa dashi, dan wannan zai haifar da cututtuka.

8 *ANA SO MUTUM YA RUFE KANSA;*
  Ana son wanda yake bayan gida ya rufe kansa a daidai lokacin da yake yi, domin koda wani ya yi kuskuren ganinsa to shi bai ganshi ba, abin zai zo da
sauki, amma ba zaka ji dadi ba kana bayan gida ka hada ido da wani, wanda zai iya zama
dalibinka ne ko suruki ko da..,'

9 *KADA AYI MAGANA;*
  An hana mutum yana bayan gida yana Magana, sai dai idan akwai
dalili mai kwari, kamar ka ga makaho ya nufi
rijiya ko karamin yaro…'.

10 *KADA A TARI ISKA;*
An hana idan mutum zai yi bayan gida a dawa (daji) an hana ya tari iska,
domin zai busowa jama'a warin bayan gidansa, kenan sai ya yi nesa, ya kuma duba ina iska
take kadawa.
.............

ZAMU TSAYA A NAN SAI LOKACI NA GABA ZAMU KAWO MUKU SAURAN LADDUBBAN INSHA ALLAHU.

WANDA YAYI BITAR RUBUTUN SHINE: *Hashim Siraj Uba ats-tsamawy( _ABU-SINAN_ )*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN;

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

002 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE, DAGA ZAUREN *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na biyu 002_

Gabatarwa: *UMMU-SINAN*

*HUKUNCIN TSARKI A MUSULUNCI*

     Tsarki wajibine, saboda haka
dukkan wanda dayan wadancan abubuwan da muka lissafa a rubutun daya gabata
suka same shi to dole yayi tsarki.

*ABUNDA AKE TSARKI DASHI:*  
   
   Abinda ake tsarki dashi a shari'ah shine ruwa mai tsarki mai tsarkakewa, wannan shi ake kira Istinja'u .

Saidai idan mutum bai sami ruwan ba sai ya yi da duwatsu a kalla guda uku, idan ya ga na
ukun ya fito a bushe ba wata laima shikenen, idan kuma akwai laima to sai ya kara su kai
biyar wuturi ake bukata (3,5,7,9…) wannan kuma
ana yinshi a fitsari ko bayan gida, sannan idan
ka sami ruwa ba sai ka sake ba, wannan
hukunci shi ake kira Istijmari , ka samu ka hada duka a lokaci guda, misali idan ka yi bayan gida
sai kasa tsinke ko takarda mara rubutu sai ka share sannan sai ka biyo shi da ruwa. Kenan
ba'a tsarki da yawu (miyau).
Kada asha'afa, idan aka yi la'akari da abinda ya fita da kuma abinda ya fantsamo maka, za'a raba tsarki zuwa gida biyu:

(1) Tsarkin Hadasi: Shine tsarkin abinda ya fita daga dayan mafita guda biyu, kamar fitsari,
maziyyi…'.

(2) Tsarkin Kabasi: Shine tsarkake abinda ya taba jiki ko tufafi ko kuma wuri, kuma ko
wannensu baya yiwuwa saida ruwa mai tsarki mai tsarkakewa.
Amma idan aka yi la'akari da girma ko rashin
girma za'a kasa tsarki zuwa gida biyu shima:

(1) Babba wanda ake kira Hadasul Akbar:
Ankira shi babbane domin ba'a tsarkaka daga gareshi sai an yi wanka, kamar fitar maniyyi, ko
saduwa, ko daukewar jinin al'ada ko na biki.

(2) Karami wanda ake kira Hadasul Asghar:
wanda yake tsarki ko alwala ta wadatar, kamar
fitsari ko maziyyi.
Yadda ake yi: Da farko mutum ya wanke
hannunsa na hagu kafin ya sa a wurin da zai
wanke, domin hannun sa ya koshi da ruwa,
sannan sai ya wanke wurin fitsari. Daga nan
kuma sai ya fara wanke wurin bayan gida, ana bukatar mutum
ya wanke al'aurar sa baki dayanta musamman
idan maziyyi ne ya fita.

Insha Allahu zamu dakata anan sai wani lokaci Na gaba zamu tashi bayani akan LADUBBAN SHIGA BAYAN GIDA/MAKEWAYI(TOILET).



WANDA YAYI BITAR RUBUTUN SHINE: *Hashim Siraj Uba ats-tsamawy( _ABU-SINAN_ )*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN:

*MUKYAUTATA NIYYA*
http://wa.me/+2348064734911

*KARATUTTUKAN MALUMAN SUNNAH*
http://wa.me/+2349031666613

001 MU KOYI IBADA A SAUKAKE

📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖
MU KOYI IBADA A SAUKAKE,
DAGA ZAUREN *MUKYAUTATA NIYYA*
📖📖📖📖📖📖📖📖📖📖

_Fitowa Na daya 001_

Gabatarwa: *UMMU-SINAN*

*MUKADDIMA*

Godiya ta tabbata ga Allah madaukakin sarki Wanda ya wajabta mana tsarki, tsira da aminci su tabbata ga fiyayyen halitta Annabi Muhammad s.a.w Wanda ya karantar damu yadda zamuyi tsarki.

_Bayan Haka;_
Insha Allahu kamar yadda muka alkawarta muku cewa zamu fara kawo muku karantarwa akan ibada da sauransu, yanzu zamu fara daga yau har zuwa lokacin da muke iyawa insha Allahu.
Mun tsara Abubuwan daki-daki, zamu fara da magana akan tsarki kafin sauran, zamuyi kokarin ganin kullum munyi sau daya, filin tambaya a bude yake insha Allahu.

*TSARKI DA YADDA AKE YINSA A MUSULUNCI*

*Shimfida:*  Mu sani ya 'yan-uwa masu albarka,
wannan addini na musulunci addinine da yake
cikakken addini ta kowane bangare, bai takaitu
ga alwala da sallah ba kawai, ya shafi kowane bangare na rayuwa, kamar tsafta kiwon lafiya
zamantakewa, kasuwanci taimakon juna, tsare-
tsaren gudanarwa dadai sauransu.
A yanzu zamu kawo bayanai da suka shafi tsarki, dame-dame ake yiwa tsarki? Me rashin tsarkin yake jawowa? Ya ladubban yin tsarkin
suke? Ya ake shiga makewayi? Dadai sauran wadansu batutuwa da suke da alaka da wannan
maudu'i, da fatan Allah ya yi mana jagora ya
kuma fahimtar da mu.

*ABUBUWAN DA AKEWA TSARKI:*

Ana yin tsarki ne
daga dukkan abinda ya fito ta daya daga
mafita guda biyu ko ma ta duka inbanda hutu (tusa). Kenan ana yiwa fitsari, bayan gida maniyyi maziyyi jinin al'ada….tsarki, kawai dai idan mutum yana da alwala sai ya yi tusa to
alwalar kawai zai sake ba sai ya dauki buta ya yi tsarki ba.

Insha Allahu zamu dakata anan sai lokaci Na gaba.

WANDA YAYI BITAR RUBUTUN SHINE: *Hashim siraj uba ats-tsamawy(ABU-SINAN)*

DOMIN SHIGA GROUPS DIN:

*MUKYAUTATA NIYYA*
wa.me/+2348064734911

*KARATTUTUKAN MALUMAN SUNNAH*
wa.me/+2349031666613

Monday, 8 October 2018

SHAWARAR UMMU JURAIJ GA YAN UWA MATA

GAREMU MATA,SHAWARA CE KAWAI!!!.

Duba da yanda Allah ya halicce mu ,yasa nake ganin ya kamata mu Dan nutsu kadan mu gane muna da tawaya da kuma matsaloli a tare damu.
Duk inda aka duba koda Asibiti ko wurin magani za a tarar  mata munfi maza damuwa da kuma yawan lalurori.
Haka bangaren shedanci mata munfi yawa.
Sannan bangare tsafi da tsubbu mune a gaba.

Wani Malami Yace  "Idan Namiji ya zama Ustaz za a ga abin kamar wani abu gama gari,amma kafin mace ta zama ustaziya completely sai anci baqar wuya,zaka ganta dai kamar Ustaziya amma daga shedan ya Dan hura ta sai kaga ta zama wata qaramar shaidaniya ko 'Yar bori,amma Duk barnar 'ya mace indai akwai tsoron Allah a tare da ita da kuma ilimi kana fara Mata nasiha da wa'azi zata nutsu sa6anin wacce ta rasa wannan abubuwa guda 2,ita mace dole sai kayi haquri da wasu dabi ah NATA".Kuma na yarda da wannan maganar tasa,haka muke.

Hakan yasa naga ya kamata mudan riqe wannan domin samun nutsuwa a rayuwar mu ta yau da gobe,saboda yanda zamu ga mun zama abubuwan wasan  shaidanu,su shiga jikinmu sanda suka so su kuma fita sanda suka ga dama,Allah ya qare mu da lafiya baki daya.

Ki Tabbatar kina wadannan abubuwan koda kina da lalura ko baki da ita don Allah na roqeki.

*Karanta koda Rabin izu ne na Qur'ani kullum duk kasalarki ko simini 1 ki daure kiyi,a hankali zakiji kina qara yawan karatun idan kika saba,ko kinji kamar kin dauki dala da gwuron dutse idan za kiyi karatun ki fadawa zuciyar taki dole sai kinyi,don wata tace min " idan zata karanta Qur ani ji take kamar zata mutu".

*ki nemi (hisnul Muslim) Littafi ne,ki ajiye akusa dake ki duba a hankali akwai Azkar Wanda za kiyi da safe da kuma Wanda za kiyi da yamma,ko unguwa zaki je kidan  saka shi a jaka idan lokacin yi yayi ki dakko kiyi.

*Idan kika kama ruwa bayan fitsari ki Dan daure kiyi alwala ko ba ko da yaushe ba amma kidan dinga kokartawa kina yi.Zama da alwalan  yana da kyau koda kina Haidha kiyi.

*Yar uwa kina sallame sallar farilla ki karanta ayatul,kursiyyu,falaqi,Naasi,Qul huwal lahu(ikhlas)ko wacce 3,ki Dora da amanar rasul,barinma ki qara da subhanallahi 33,Alhamdulillah33,Allahu akbar33 ,ki yima Annabi (SAW)salati ,nan take zaki ji wani sanyi da nutsuwa aranki.

*Kin farka daga bacci kinyi Addu ah,zaki shiga ban daki kinyi addu'ah,zaki fito kinyi addu ah,zaki zauna kince Bismillah,zaki ci Abinci kinyi addu ah,kin gama ci kinyi Addu ah,zaki sanya tufafi koda bismillah kice,zaki cire Ki ambaci hakan,zaki fita daga gida kinyi addu ah,kin dawo zaki shiga gida kinyi addu ah,komai zaki yi na aiki ko baki iya addu arba,kawai ambaci "Bismillah".

*Ki Dan dinga zama kina Nazarin abubuwan da Ki kasan Haram ne ki kudirce fara ragewa,a hankali sai Allah ya dafa mana,kamar jin kada kada-kade,kallo mara amfani,sai fa muna ragewa Nasan muna son nishadi amma Reduction yayi a rayuwa,kamar zama ba dan kwali duk sai mun dinga kula ,Idan muna zaune bama komai muyi ta istigfari,hailala,salati da sauransu.

Guarantee na baki idan bakya yi ki fara daga yau zaki ji wani chanji na musamman acikin Duniyar ki.Allah yasa mu dace baki daya Ameen.

✍ummu juraij

Monday, 19 March 2018

AZUMIN WATAN RAJAB(SUNNAH KO BIDI'AH)?

🌺🍇🍏🌹🌷🌼🌸💐🌺
*AZUMIN WATAN RAJAB(AZUMIN TSOFAFFI) SUNNAH NE KO BIDI'AH???*
🌺💐🌸🌼🍇🌷🌹🍏🌺

Rubutawa: *_Hashim Surajo Uba Tsamiya(ABU SINÃN)_*

بسم الله الرحمن الر حيم

```Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya chanchanci a bauta masa shi kadai kuma ya hanemu da shirkah, Tsira da Aminci su tabbata ga farin jekada Annabi Muhammad s.a.w wanda ya tsoratar damu daga aikata bidi'ah.

Bayan haka; Nayi nufin yin wannan rubutu ne saboda ganin ya dace mu fadakar da yan uwa musamman iyaye da kakanni da ake zalunta da hadissan karya, dangane da falalar azumin watan Rajab.

Da farko dai shi watan Rajab yana daya daga watanni masu alfarma wanda aya ta 36 a suratu taubah tayi bayani.

✏✏✏✏✏✏✏✏
MAGANGANUN MAGABATA AKAN AZUMIN WATAN RAJAB(AZUMIN TSOFAFFI)
✏✏✏✏✏✏✏✏

kai tsaye yanzu ga Wata tambaya da akayi ma sheikh bin baaz(R.H) dangane da azumin Rajab(azumin tsofaffi).

An tambayi sheikh bin baaz(R.H) akan cewa shin ko yana halatta azumtar watan Rajab (AZUMIN TSOFAFFI) gaba dayansa? Domin wasu Malamai suna fadar cewa: duk wanda ya azumci Rajab, an gafarta mashi zunubbansa koda sun kai yawan kumfar teku, wasu kuma malaman sunyi hani da azumtar watan suna cewa; duk da zamanshi cikin watanni masu alfarma baya halatta a azumceshi gaba daya???

Ga amsar da bin baaz ya bada, yana cewa; " Abun sani kawai shine ba'a shar'anta azumtar watan Rajab ba! Bari ma an karhantashi, abunda ya tabbata shine an shar'anta azumin sha'aban, manzon Allah s.a.w ya kasance yana yin azumin sha'aban, yana azumtar sha'aban sai kadan yake  ragewa, amma Rajab an karhanta yin azumi a cikinsa, azumi a cikinsa yana daga cikin aikin jahiliyya, saboda masu azumtar basu da dalilin azumtar watan!!! Hadisan da ake yawo dasu akan falalar watan Rajab basu da asali, bari ma na karya ne wadanda basu inganta ba, abunda shari'ah ta shar'anta ga musulmai shine suci susha a watan Rajab, sai dai idan ya kasance kana yin azumin nafila tun kafin zuwan watan wanda su dama shari'ah ta tabbatar dasu, kamar; litinin da Alhamis, Ayyamul-beedh da sauransu, wannan yana da kyau kuma babu laifi, amma azumtar watan gaba dayansa, ko kuma baka saba yin azumin nafila ba sai da watan ya shigo sai ka fake da azumin nafila ka gabatar da na Rajab wannan shari'ah bata yadda dashi ba.
Wannan itace amsar da sheikh bin Baaz ya bada dangane da azumin tsofaffi na Rajab.

Hadisi ya tabbata daga Aisha matar Annabi Muhammad s.a.w tana cewa:كان رسول الله صلى الله عليه وسلم يصوم حتى نقول لايفطر، ويفطر حتى نقول لايصوم، وما رأيته أكثر صياما منه في شعبان.
[صحيح أخرجه البحاري(١٩٦٩)، و مسلم(١١٥٦)].

Ma'ana; Aisha R.A take cewa; "Manzon Allah s.a.w ya kasance yana yin azumi har sai nace bai cin abinci! Yana cin abinci har sai nace bai yin azumi(ma'ana yana yin azumi da yawa, haka kuma yana aje azumi ya huta sosai) ban taba ganin Manzon Allah s.a.w yana cika azumin wata daya ba sai dai idan ramadhan ne, ban taba ganin watan da yafi azumi a cikinsa ba face sha'aban.
[Bukhari da Muslim].

ﻗﺎﻝ ﺷﻴﺦ ﺍﻹﺳﻼﻡ ﺍﺑﻦ ﺗﻴﻤﻴﺔ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻲ
" ﻣﺠﻤﻮﻉ ﺍﻟﻔﺘﺎﻭﻯ " ‏( 25/290 ‏) :
" ﻭﺃﻣﺎ ﺻﻮﻡ ﺭﺟﺐ ﺑﺨﺼﻮﺻﻪ ﻓﺄﺣﺎﺩﻳﺜﻪ ﻛﻠﻬﺎ
ﺿﻌﻴﻔﺔ ، ﺑﻞ ﻣﻮﺿﻮﻋﺔ ، ﻻ ﻳﻌﺘﻤﺪ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﻌﻠﻢ ﻋﻠﻰ
ﺷﻲﺀ ﻣﻨﻬﺎ ، ﻭﻟﻴﺴﺖ ﻣﻦ ﺍﻟﻀﻌﻴﻒ ﺍﻟﺬﻱ ﻳﺮﻭﻯ ﻓﻲ
ﺍﻟﻔﻀﺎﺋﻞ ، ﺑﻞ ﻋﺎﻣﺘﻬﺎ ﻣﻦ ﺍﻟﻤﻮﺿﻮﻋﺎﺕ ﺍﻟﻤﻜﺬﻭﺑﺎﺕ...

Shaikhul Islam Ibn taimiyyah (RH) y
ace: “Kebance watan rajab da yin azumi,
dukkan hadisan
da su ka zo akan haka da’ifai ne (masu
rauni), bari
ma hadisan karya ne, masu ilimi
basu amfani dasu, domin basu
cikin hadisan
da ake amfani dasu don nuna falalar
aikata abu,  bari ma dukkan su ma
hadisai ne
na karya..”
Duba Majmu’u Fatawa (25/290).

ﻭﻗﺎﻝ ﺍﺑﻦ ﺍﻟﻘﻴﻢ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ :
" ﻛﻞ ﺣﺪﻳﺚ ﻓﻲ ﺫﻛﺮ ﺻﻴﺎﻡ ﺭﺟﺐ ﻭﺻﻼﺓ ﺑﻌﺾ
ﺍﻟﻠﻴﺎﻟﻲ ﻓﻴﻪ ﻓﻬﻮ ﻛﺬﺏ ﻣﻔﺘﺮﻯ " ﺍﻧﺘﻬﻰ ﻣﻦ " ﺍﻟﻤﻨﺎﺭ
ﺍﻟﻤﻨﻴﻒ " ‏(ﺹ 96 ‏)

Imam Ibnul Qayyim (RH) yace;
“Dukkan hadisan 
da suka ambaci azumin watan rajab da
sallatar wasu
darare a cikin sa, hadisai ne na karya kuma 
kirkirarru”.
Duba Almanarul Muniif (shafi 96).

ﻭﻗﺎﻝ ﺍﻟﺤﺎﻓﻆ ﺍﺑﻦ ﺣﺠﺮ ﻓﻲ " ﺗﺒﻴﻴﻦ
ﺍﻟﻌﺠﺐ " ‏(ﺹ 11 ‏) :
" ﻟﻢ ﻳﺮﺩ ﻓﻲ ﻓﻀﻞ ﺷﻬﺮ ﺭﺟﺐ , ﻭﻻ ﻓﻲ ﺻﻴﺎﻣﻪ
ﻭﻻ ﺻﻴﺎﻡ ﺷﻲﺀ ﻣﻨﻪ ﻣﻌﻴﻦ , ﻭﻻ ﻓﻲ ﻗﻴﺎﻡ ﻟﻴﻠﺔ
ﻣﺨﺼﻮﺻﺔ ﻓﻴﻪ ﺣﺪﻳﺚ ﺻﺤﻴﺢ ﻳﺼﻠﺢ ﻟﻠﺤﺠﺔ "
ﺍﻧﺘﻬﻰ.

Alhafiz Ibn Hajar Al-Asqalani yake
cewa; “Babu
wani abu da aka ruwaito na falalar
watan Rajab,
ko yin azumi a cikin sa, ko azumtar
wasu adadin
kwanaki ayyanannu, ko tsayuwar
wasu darare
kebantattu”.
Duba Tabyinul ujub (shafi 11).

ﻭﻗﺎﻝ ﺍﻟﺸﻴﺦ ﺳﻴﺪ ﺳﺎﺑﻖ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻲ " ﻓﻘﻪ
ﺍﻟﺴﻨﺔ " ‏( 1/383 ‏) :
" ﻭﺻﻴﺎﻡ ﺭﺟﺐ ﻟﻴﺲ ﻟﻪ ﻓﻀﻞ ﺯﺍﺋﺪ ﻋﻠﻰ ﻏﻴﺮﻩ ﻣﻦ
ﺍﻟﺸﻬﻮﺭ , ﺇﻻ ﺃﻧﻪ ﻣﻦ ﺍﻷﺷﻬﺮ ﺍﻟﺤﺮﻡ , ﻭﻟﻢ ﻳﺮﺩ ﻓﻲ
ﺍﻟﺴﻨﺔ ﺍﻟﺼﺤﻴﺤﺔ ﺃﻥ ﻟﻠﺼﻴﺎﻡ ﻓﻀﻴﻠﺔ ﺑﺨﺼﻮﺻﻪ ,
ﻭﺃﻥ ﻣﺎ ﺟﺎﺀ ﻓﻲ ﺫﻟﻚ ﻣﻤﺎ ﻻ ﻳﻨﺘﻬﺾ ﻟﻼﺣﺘﺠﺎﺝ ﺑﻪ
" ﺍﻧﺘﻬﻰ

Imam Sayyid Sabiq (RA) yake cewa;
“Azumin
watan rajab bashi da wani fifiko na
falala akan
waninsa cikin watanni, sai dai shi
yana daga cikin
watanni (guda hudu) ma su alfarma,
kuma ba a
samu a cikin sunnah ingatacciya ba cewa
yin azumi a
cikin sa yana da falala kebantacciya,
abunda ya zo
akan haka (ma’ana hadisan da suka
zo) ba a kafa
hujja dasu (domin da’ifai ne)”
Duba Fiqhus-Sunnah (1/383).

ﻭﺳﺌﻞ ﺍﻟﺸﻴﺦ ﺍﺑﻦ ﻋﺜﻴﻤﻴﻦ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻦ ﺻﻴﺎﻡ
ﺍﻟﺴﺎﺑﻊ ﻭﺍﻟﻌﺸﺮﻳﻦ ﻣﻦ ﺭﺟﺐ ﻭﻗﻴﺎﻡ ﻟﻴﻠﺘﻪ .
ﻓﺄﺟﺎﺏ :
" ﺻﻴﺎﻡ ﺍﻟﻴﻮﻡ ﺍﻟﺴﺎﺑﻊ ﺍﻟﻌﺸﺮﻳﻦ ﻣﻦ ﺭﺟﺐ ﻭﻗﻴﺎﻡ
ﻟﻴﻠﺘﻪ ﻭﺗﺨﺼﻴﺺ ﺫﻟﻚ ﺑﺪﻋﺔ , ﻭﻛﻞ ﺑﺪﻋﺔ ﺿﻼﻟﺔ "
ﺍﻧﺘﻬﻰ .
" ﻣﺠﻤﻮﻉ ﻓﺘﺎﻭﻯ ﺍﺑﻦ ﻋﺜﻴﻤﻴﻦ " ‏( 20/440 ‏)

An tambayi sheikh Muhammad Salihul Usaimeen
(RH)
dangane da azumi ranar 27 ga watan
rajab da
kuma tsayuwar dararen sa.
Sai ya amsa da cewa:
“Yin azumi ranar 27 ga watan Rajab
da tsayuwar
darensa kebance shi da haka bidi’a
ne, dukkan
bidi’a kuma batace”
Duba Majmu’u fatawa na Usaimeen
(20/440).

   Haka zalika Sayyidina umar R.A ya kasance yana bulala akan wadanda ke kamewa akan azumin Rajab, yana ce musu kuci abinci, wannan watane da ya kasance ake girmamawa a lokacin jahiliyya. [Ibn Abi shaibah ya fitar 3/102] da ibn kathir a cikin musnadil- faruk 1/285]

Haka zalika ibn umar R.A ya kasance idan yaga mutane suna wuce gona da iri akan Rajab, yana kyamar hakan!
[Sahih: ibn abi shaibah ya fitar 3/102]

Ibn Abbas ya kasance yana hani akan azumin Rajab gaba dayansa, saboda kada a maida shi ya zama abunda za'a rinka yi duk shekara, wato a maidashi ya zama idi.
[Sahih; Abdulrazak ya fitar 7854].

✏✏✏✏✏✏✏✏
HADISAN DA SUKA INGANTA AKAN WATAN RAJAB!
✏✏✏✏✏✏✏✏
=  "kuyi axumi a cikinshi kuma kuci abinci a cikinshi.
[Sahih irwa'ul galeel 958]

= Sha'aban yana tsakanin Rajab da Ramadhan, ana shagaltar da mutane akanshi(domin samun saukin Ramadan) a cikin sha'aban ake daukar ayukkan bayi, ina kwadayin/inason kada a daga ayyukana face ina azumi.
[Isnadinsa mai kyau ne, silsilatus-sahiha 1898]

✏✏✏✏✏✏✏✏
HADISSAI DA'IFAI WADANDA MASU AZUMIN RAJAB KE KAFA HUJJA DASU.!!!
✏✏✏✏✏✏✏✏

= A cikin Aljanna akwai wani gulbi, ana kiransa Rajab, ruwansa suna da fari wanda farin yafi na nono, duk wanda yayi azumin Rajab na rana daya, Allah zai shayar dashi daga wannan gulbin.[Silsilatu-dha'ifah 1898]

= Rajab watan Allah, Sha'aban wata na(manzon Allah), Ramadan watan Al'umma ta. 
Da'ifi ne, silsilatu-dha'ifah 4400]

= Darare guda biyar ba'a maida Addu'ah: 1. Farkon Daren Rajab

2. Daren Rabin watan sha'aban

3. Daren jumu'ah

 4. Daren karamar sallah

5. Daren babbar sallah

[Maudu'i ne, silsilatu-dha'ifah 1452]

= Rajab watane mai girma, Allah na lunka lada idan kayi aikin Alkhairi a cikinsa, duk wanda yayi azumin Rajab na kwana daya,kamar yayi azumin shekara. Duk wanda yayi na kwana bakwai, za'a rufe mashi kofofin wutar jahannama bakwai. wanda yayi na kwana takwas, za'a bude mashi kofofin Aljanna takwas. Wanda yayi na kwana sha biyar, mai kira zaiyi kira a sama yace; an gafarta maka abunda ya gabata na laifuka...[maudu'i ne, silsilatu-dha'ifah 5413]

✏✏✏✏✏✏✏✏
RUBABBUN HADISSAN DA YAN SHI'AH KE KAFA HUJJA DASU AKAN FALALAR WATAN RAJAB.
✏✏✏✏✏✏✏✏
Daga Baban hassan (A.S) yace; Annabi Nuhu (A.S) ya tuka jirgin ruwa a farkon watan Rajab, sai ya umurci wadanda ke tare dashi da su azumci wannan ranar, yace; "duk wanda ya azumci wannan ranar Allah zai nisanta shi da wuta na tsawon tafiyar shekara daya.

=Daga Abi Ja'afar, Muhammad ibn Aliyu(A.S) yace; duk wanda yayi azumi a Rajab na rana daya, a farkon Rajab ko tsakiyarsa ko karshensa, Allah ya wajabta mashi shiga Aljanna, kuma Allah zai sanya shi a tare damu a cikin darajojinmu na Ahlul baiti a ranar kiyama, wanda yayi na kwana biyu, Allah zai gafarta mashi duk zunubbanshi da suka gabata, wanda yayi na kwana uku, Allah zai gafarta mashi abunda ya gabatar na zunubi da wanda zaiyi a gaba sannan za'a bashi damar ceton yan uwanshi ma'abota zunubi...

= As-sadik Ja'afar  ibn Muhammad yace; "kada ka bari ranar ashirin da bakwai ga Rajab ta wuce ba tare da ka azumceta ba! Domin a ranar ne aka saukar wa Annabi Muhammad s.a.w Annabta...

Duka wadannan zaka samesu a cikin littafi mai suna FALALAR WATANNI UKU, wanda gingimemen malamin Shi'ah mai suna MUHAMMAD IBN ALIYU IBN HUSSAIN IBN MUSA AL-QUMMY ya rubuta.
Allah ka la'anci qummy.

  A takaice wadannan sune hujjoji na dangane da rashin ingancin azumin Rajab(azumin tsofaffi), duk wanda yake ganin akwai Gyara matukar gyaran nashi ya inganta hadisi ne ko aya ina maraba dashi kwarai da gaske.

Allah ya hadamu dani daku da sauran musulmai a cikin Aljannah.

ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH...```

Copyright©
Dalibinku
*_Hashim Suraj Uba Tsamiya {ABU SINÃN}_*

☎08064734911
📞09030201868 
    08116194214

http://hashimtsamiya.blogspot.com

atstsamawy@gmail.com

17-07-1438AH
15-04-2017AC