HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA
DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE
A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #KALMAR_SHAHADA
Godiya ta tabbata ga ALLAH Muna gode masa
muna neman taimakom wanda ALLAH Yashiryar
Shine shiryayye, Wanda ALLAH Yabatar Babu mai
iya shiryar dashi,
Hudubar Yau tayi magana ne akan Wata
tsaddadiyar kalma wato KALMATUSH SHAHADA !
Ita wanman Kalmar mai girman ita ce mabudi na
shiga musulunci, Da kuma banbatawa tsakanin
kafurci da imani,
Wannan Aya ALLAH Madaukakin sarki ya shaida
kanta kamar yadda Yafada a cikin Suratul Ali
imran ALLAH YA SHAIDAR CEWA BABU WANDA
YA CHANCHANTA DA BAUTAWA SAI SHI
ANNABAWA SUN SHAIDA MALA'IKU SUN
SHAIDA MALAMAI MA SUN SHAIDA
Yaku yan uwa musulmi musulunci mutun baya
ingantuwa har sai ya yarda da kalmar,
Ita ce kalmar shahada ana ce mata KALMAR
YAKINI
Wannan kalmar ita ke banbamta kafurci da
musulunci
Hadisi yazo daga manzo tsira cewa DUK WANDA
YAFADI KALMAR SHAHADA YANA
SAKANKANCEWA DA ITA HAR YA MUTU ZAI
SHIGA ALJANNAH.
Annabawan da ALLAH Madaukakin sarki ya tura
zuwa ga jama'a dukansu dan jaddadda KALMAR
SHAHADA
Kamar yadda Aya tazo cewa HAKIKA MUN AIKA
DA KOWANE ANNABI ZUWA GA AL'UMMAR SA
DAN SU BAUTAWA ALLAH SU KAFURCEWA
DAGUTU''
Misalin ALLAH Madaukakin sarki ya aikawa
kafuran Al'umma da manzanni
Samudawa ALLAH Ya aika masu da Annabin
Salihu dan yayi kira akan tsaida kalmar Shahada
Hakama Annabin Shu'aib an aikasa ga mutanen
madiya Dan yayi kira akan kalmar shahada.
Annabawa da manzanni dukkansu an aiko su dan
isar da wannan Kalmar ta LA'ILAHA ILLALLAH.
Hatta mafificin halitta Manzo sallallahu alaihi
wassalam Yazo ne dan isar da KALMAR
SHAHADA
Yaku yan uwa musulmi Kusani wajibi ne ga
musulmi yasan fassarar ta, bawai fadin ta ba
kadai,
Kuskurene Fassar da hausawa kewa KALMAR
SHAHADA Cewa
-Babu sarki sai ALLAH
Ko kuma masu cewa
-Babu iko sai na ALLAH, Wanda duk wannan
Fassarar kuskure ne.
Yaku yan uwa musulmi KALMAR SHAHADA Tana
da sharudda guda Takwai 8
1-Dole ne kasan Ma'anar ta
Sanin Ma'anar ta na nufin Haddaceta da sanin
hakikan nin fassarar ta da abunda ta kunsa.
2-SAKANKANCEWA
Ma'ana yarda da duk abunda ta kunsa banda
shakku ko ko kwanto, Sau daya a wannan
zamanin wasu na walwale KALMAR SHAHADAR
Su ta hanyar kalaman su da ayyukansu, kamar
fadar wata kalmar shirka, ko kuma aikata shirka
kamar sihiri da tsafe-tsafe Da zuwa wajen yan
duba ko malaman tsibbo ko bokaye.
3-Dole ne kayi Zikiri da ita
Ma'ana fadar ta a matsayin zikiri wato ambaton
Dan yin zikiri Bawai fadar ta dan nishadi ba, ko
dan baiwa wani haushi ko kuma ana fadar ta ana
rawa, dukkan wannan kuskure ne, Hakama
hadata da wata daudar duniya Misali kaga wata
mota mai kyau sai kaji an fadi LA'ILAHA
ILLALLAH
Kunga wannan kuskure a hada daudar duniya da
wannan babbar kalmar ita fa duniya ALLAH YA
TSINE MATA DUK ABUNDA KE CIKINTA IN
BANDA AMBATTON ALLAH DA ZIKIRIN SA
4-Fadar ta da gaske
Ma'ana fadar ta gaske bada niyar wasa ba ko
kuma ganganci ko kuma karya kamar yadda
munafukai sukeyi a lokachin Annabi Kamar yadda
ALLAH Yafada a cikin Suratul munafikun ''IDAN
MUNAFUKAI SUNZO WAJENKA SUNA CEWA SUN
SHAIDA KAI MANZO ALLAH NE TABBAS ALLAH
YA SHAIDA KAI MANZO NE AMMA SU
MUNAFUKAI MAKARYATA NE''
5-Dole kaso kalmar
Ma'ana kaso kalmar har a zuciya ta hanyar son
tane zaka ki tare da kauracewa wanda baya
sonta.
8-Ka yarda da ita
Ma'anar yarda da ita da duk abunda ta kunsa
dan hakika duk wanda yafadeta amma bai yarda
da ita to hakika shima munafuki ne kuma za'a
hada shi da munafukai na lokachin magabata
ALLAH Madaukakin sarki yana cewa ''WANDA YA
KAFURCEWA DAGUTU YAYI IMANI DA ALLAH
HAKIKA YAYI RIKON DA WATA IGIYA MAI KARFI
WADA BATA YANKEWA''
Igiyar da mai karfi ita ce KALMAR SHAHADA
Yaku yan uwa musulmi duk wanda ya furta ta to
dole ne yasan ma'anar ta
ALLAH Madaukakin sarki yana cewa ''BABU
MASU SHIGA ALJANNAH SAI WANDA YA
SHAIDA DA KALMAR SHAHADA.
Ba makawa saika san ma'anar ta
Akwai kura kurai da wasu keyi na furta ta
bagatatan wasu zaka gansu suna furta ba kan
gado wanda duk abunda ke duniyar nan ta fishi
daraja a wurin ALLAH Idan da duniya nada daraja
wajen ALLAH Da kafuri ko ruwan sha bai samu,
Wani hadisi yana cewa ''DUKAN WANDA YA
MUTU YASAN MA'ANAR KALMAR SHAHADA ZAI
SHIGA ALJANNAN
Wata rana wani yazo ya tambayi manzo tsira
cewa Wanene zai samu cetonka sai manzo tsira
yayi shiru (dan yaji ta sahabbai) sai abi huraira
ya tambayi ANNABI Yaya,
Sai manzo tsira yace dama nasan kai zaka fara
magana ''NA SHAIDA CEWA NI MANZO ALLAH
NE KUMA NA YARDA DA ALLAH HAKIKA DUK
WANDA YA MUTU YA SHAIDA WANNAN KALMAR
ZAI SAMU CETONA''
Imam bukhari yayi babi na musamman daya
sanyawa suna babi Dan ya nuna muhimmancin
sani abu,
Mai ahadari na cewa ''Baya halatta kai aikata
wani aiki har sai kasan hukuncin ALLAH Akansa''
Ya ALLAH Kasamu daga cikin muminai, masu
imani, masana KALMAR SHAHADA, Ka shiryamu
tare da iyalanmu,
Ya ALLAH Ka taimaki musulunci da musulmai, ka
kasqanta kafurci da kafurai, ka yiwa
shuwagabbani jagoranci kabar mu mutu muna
musulmi masu imani.
ALHAMDULILLAH
©®IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA
26 /05/1438
24/02/2017.
No comments:
Post a Comment