Friday, 8 December 2017

HUDUBAH MAI TAKEN KALMAR SHAHADA KASHI NA BIYU

HUDUBAR JUMU'A
A MASALLACI NA UKKU DAKE TSAFE ZAMFARA
DAGA IBRAHIM RABILU TSAFE
A Wannan Makon Limamin Massallaci Jumu'a Na
Ukku Dake Unguwar Area2, Tsafe Sheik Sani Na
Liman'
Yayi Hudubar Sane Akan #KALMAR_SHAHADA
KASHI NA BIYU
Godiya ta tabbata ga ALLAH Madaukakin sarki,
Muna gode masa muna neman yakare mu daga
sharrin kawunan mu, Tsira da aminci su kara
tabbata ga Manzon rahama Muhammad S.A.W
da alayen sa da sahabban sa, Da dukkan
Wadanda suka biyo bayansu da kyautatawa, Har
zuwa ranar sakamako.
A makon daya gabata malan yafara khudba akan
kalmar shahada, Inda yakawo mana sharudda
hudu da cikin takwas na kalmar shahada,
To a wannan makon ma Insha Allahu zamuji
cikon hudun tare da jin karin bayani, Dan amfana
da kuma kara fahimta ga yan uwa musulmi,
YAKU YAN UWA MUSULMI
Ita fa wannan kalmar ta LA'ILA HA ILALLAH A
Halicci duniya ne dan baki daya ne dan ita,
Hakama An halicci mutane da aljannu kaf dan
wannan kalmar haka Sama da kasa baki daya
duk an haliccesu ne dan wannan kalmar!
Wannan kalmar da ita ake banbanta kafuri da
muminin musulmi,
Wannan kalmar tana da rukuni guda biyu.
1-Korewa
2-Tabbatarwa
Ma'anar Korewa shine LA'ILAHA Babu wanda ya
chanchanta da bauta kowanene
IL'LALLAH (Tabbatarwa) Sai Allah madaukakin
sarki.
Yakamata Ko kuma wajibi kowane musulmi ya
dinga hakaito wannan ma'anar a lokacin da yake
furta wannan kalmar,
Ma'anar kalmar gaba daya shine BABU ABUN
BAUTAWA NA GASKIYA SAI ALLAH
ALLAH S.W.T Yafada cikin Suratul hajj cewa
''LALLAI SHI ALLAH SHINE WANDA YA
CHANCHANCI A BAUTAW AL-ALIYU AL-KABIRU''
Dukkan wani abun bautawa a duniya gaba daya
bai cika Al-aliyu ba, kuma bai cika Al-kabiru ba,
Shi kuwa duk wanda bai cika da wadannan
matakan ba to bai chanchanci bauta ba,
Tauhidi baya taba cika har sai an san wannan
kalmar, Kuma an dabbaka ta.
Dukkan Annabawan da Allah ya aiko har da
Manzo S.A.W Sunzo ne dan jaddadda wannan
kalmar.
Ba'a bautawa kowa sai Allah, koda Annabi ne, ko
mala'ika, Ko malamai ko waliyai ko kabarin su
Domin suma Allah sukabi har suka zama waliyai!
YAKU YAN UWA MUSULMI
Ga chi gaban sharudda
5-Idan ka fadeta yakasance kanason ALLAH Har
a zuciya ba'a baka kawai ba,
Ana fadan tane kawai dan zikiri bawai dan sanyi
jin haushi ga wani ba, Idan ka fadeta da wata
niya to tabba baka da lada.
A cikin sahihul bukhari ya ruwaito daga Manzo
S.A.W Cewa duk wanda ya kammala wasu
abubuwa guda ukku zai samu dandano na imani,
Akwai son ALLAH Dakuma son Manzo S.A.W
Muddin kanason cikawa da imani kaso ALLAH
Fiye da komai Ka kuma son Manzo ALLAH S.A.W
Fiye da kowa.
ALLAH Madaukakin sarki na cewa ''IDAN KUN
KASANCE KUNA SON ALLAH TO KUBINI ALLAH
ZAI SOKU''
YAKU YAN UWA MUSULMI
Dole ne a matsayin mu na musulmi mu kasance
muna son Alqur'ani da Hadisai na Manzo ALLAH
A koda yaushe ka kasance kana karatun Qur'ani
Kana karatun Hadisi.
6-Dole ka mika wuya ga Kalmar
Dole a mika wuya ga Kalmar Ma'ana Bin duk
abunda ke halal, Da kuma kauracewa haram,
Biyayya ga duk abunda kalmar ta kunsa.
A cikin suratul Lukman ALLAH Na cewa ''DUK
WANDA YA MIKA WUYA HAKIKA YAYI RIKO DA
IGIYA MAI KARFI''
7-Ka karbi duk Abunda kalmar tazo dashi
Ma'ana yarda da ita, Da dukkan abunda ta kunsa
baki daya,
ALLAH Na cewa ''KAFURAI SUNA GIRMAN KAI
DA ITA(KALMAR SHAHADA) SUNA CEWA YANZU
ZAMUBAR ABUNDA MUKA GADA MU BAUTAWA
ABU DAYA TAK''
Wannan kuwa shine yasanya kafurai wuta ma'ana
kin yadda da ita.
8-Dolene kafurcema dagutu
Ma'ana duk wani abu da wasu ke bautawa ka
kaurace masa,
Allah na cewa ''DUK WANDA YA KAFURCEWA
DAGUTU YAYI IMANI DA ALLAH YAYI RIKO DA
WATA IGIYA MAI KARFI''
YAKU YAN UWA MUSULMI
Akwai hadisai da yawa daga Manzo rahama
S.A.W Wadanda ke koyar damu falalar wannan
kalmar
Manzo S.A.W Yana cewa ''DUK WANDA YAFADI
KALMAR LA'ILAHA ILLALLAH WAHADAHU LA
SHARI KALA LAHUL MULKU WA HUWA ALA
KULLI SHAI'IN QADEER'' Hakika za'a kankare
masa zunubansa koda sunyi girman dutsen uhud.
A wani hadisin kuma yana cewa ''FIYAYYEN
ABUNDA NAKE FADA SHINE ''DUK WANDA
YAFADI KALMAR LA'ILAHA ILLALLAH
WAHADAHU LA SHARI KALA LAHUL MULKU WA
HUWA ALA KULLI SHAI'IN QADEER''
Duk wanda yafadi wannan a rana sau dari za'a
yafemai zunuban sa duka koda sunyi yawan
kunfar teku.
Duk wanda yafadi ''''DUK WANDA YAFADI
KALMAR LA'ILAHA ILLALLAH WAHADAHU LA
SHARI KALA LAHUL MULKU WA HUWA ALA
KULLI SHAI'IN QADEER'''' za'a kankare masa
zunubai dubu, kuma za'a basa lada dubu.
Hadisan nada yawa sosai wadannan misalai ne.
Daga karshe muna rokon Allah yasa kalmar mu
ta karshe ta kasance wannan kalmar, Ya gafarta
mana, Yajikanmu yayiwa jagororin ja gaba.
Ameen
ALHAMDULILLAH
©®IBRAHIM RABILU TSAFE ZAMFARA
04/Jimada Akhair/1438
03/03/2017.

No comments: